Akasarin masu kai mana hare-hare daga jihohin da suka kewaye mu suke – Gwamnatin Filato
Published: 19th, September 2025 GMT
Wani rahoto da kwamitin bincike da Gwamna Caleb Mutfwang ya kafa kan kashe-kashen da ke ci gaba da faruwa a Jihar Filato ya ce akasarin masu kai hare-hare suna fitowa ne daga jihohin da ke makwabtaka da Filato.
Shugaban kwamitin, Manjo Janar Rogers Ibe Nicholas, ya bayyana cewa sun gana da kabilu daban-daban da kungiyoyin masu ruwa da tsaki, tare da ziyartar dukkan al’ummomin da rikici ya shafa domin samun sahihan bayanai kan tashin hankalin da kuma hanyoyin samar da zaman lafiya mai ɗorewa.
Ya ce daga binciken da suka gudanar, an gano cewa masu kai hare-hare kan al’ummomin Filato suna fitowa ne daga jihohin Nasarawa, Kaduna, Bauchi da kuma Taraba.
“Kwamitin ya karɓi rahoton korafi daga wasu kauyuka biyu da ke jihar Nasarawa da ke iyaka da Quan’pan, inda aka ce ’yan bindiga sun kafa sansaninsu, lamarin da ya tilasta wa al’ummomin Filato da ke Quan’pan tserewa.”
“A Wase da Kanam, an samu rahoton cewa akwai sansanonin ’yan bindiga da ake zargin suna da alaƙa da kungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi.
“Dalilan da muka gano na haifar da hare-haren sun haɗa da kwace ƙasa da albarkatu faɗaɗa danniya, mamayar kabilanci da addini, rikicin siyasa, sai kuma karbar kudin fans ana masu garkuwa da mutane.
“Iyakokin da aka fi kia hari daga su sun haɗa da hanyoyin shigowa daga Nasarawa ta Wamba, Lafia da Awe; daga Kaduna ta Lere, Kaura da Sanga; daga Bauchi ta Toro, Tafawa Balewa, Bagoro da Alkaleri; da kuma daga Taraba ta Ibi da Karim Lamido.
“Wadannan hanyoyi ba sa samun kulawa sosai, kuma masu kai hari na amfani da su don kai farmaki da tserewa cikin sauri,” in ji shi.
Manjo Janar Rogers ya kuma jaddada cewa an kai hari a ƙauyuka 420, kuma kusan rayuka 12,000 sun salwanta, don haka ba za su bari a ci gaba da waɗannan kisan gillar ba.
Gwamna Caleb Mutfwang, yayin karɓar rahoton a gidan gwamnatin jihar da ke Jos, ya yi alkawarin aiwatar da shawarwarin da kwamitin ya bayar domin tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa a jihar.
Haka kuma, Gwamnan ya bayyana shirinsa na miƙa rahoton ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ƙwararrun jami’an tsaro, domin su fahimci yadda rikicin ya shafi jihar sama da shekaru 20, tare da samar da mafita mai ɗorewa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Matsalar Abinci
এছাড়াও পড়ুন:
Dakarun Sojin Kasar Yamen Su Kai Hare-hare A Muhimman Wurare A HKI.
Rahotanni sun bayyana cewa dakarun sojin kasar Yamen sun kaddamar da hare-hare guda 3 da gagarumar nasara a wasu mihimman wurare a HKI, da zimmar mayar da martani kan hare haren da Isra’ilan take kai mata, saboda ci gaba da nuna goyon bayan alummar falasdinu da take yi da ta kwashe shekaru biyu ta na yi musu kissan gilla,
Acikin wani bayani da kakakin sojin kasar Yamen Yahya Saree ya fitar ya sanar cewa kasarsa ta kaddamar da hare hare a muhimman wuraren guda 3 a Yaffa da HKI ta mamaye , kuma ta yi amfani da makami na haypersoni balisstic missile da ta basu suna da falasdinu na 2.
Haka zakila ta kai hari a yankin umm Rashrash wato Eilat inda ta yi amfani da jirage marasa matuki guda 3, da kuma Be’er sheva, sai dai yace za su ci gaba dakai har a Eilit ba kakkautawa. Kasar yamman ta sha alwashin ci gaba da kai hare-haren nuna goyon baya ga alummar falasdinu da ake zalunta har sai HKi ta dakatar da kisan kare dangi da take yi a gaza kuma a dauke killacewar da aka yi mata.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Isra’ila Na ci Gaba Da Kutsa Kai A Tsakiyar Gaza A Yau Juma’a September 19, 2025 Dangantaka Na Kara Tsami Tsakani Faransa Da Isra’ila Kan Amincewa Da Falasdinu . September 19, 2025 Sojojin HKI 12 Ne Suka Halaka Ko Suka Ji Rauni A Gaza September 19, 2025 Amurka Ta Yi Amfani Da Kujeran Veto Don Hana Zaman Lafiya A Gaza September 19, 2025 HKI Ta Kai Hare-Hare Kan Wurare Har 5 A Kudancin Kasar Lebanon September 19, 2025 Majiyoyin Diblomasiyya Sun Ce Washington Zata Jagoranci Turawa A Tattaunawa Da Iran September 19, 2025 Iran Ta Bukaci Kwamitin Tsaro Na MDD Ta Zabi Diblomasiyya Kan Fito Na Fito September 19, 2025 Yahudawa Suna Ci Gaba Da Yin Hijira Zuwa Wajen HKI September 18, 2025 ‘Yan Gwgawarmaya Sun Kashe Sojojin HKi 4 A Gaza September 18, 2025 An Halaka Sojojin HKI Biyu Ta Hanyar Sukarsu Da Wuka A Kusa Da Iyakar Jordan September 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci