Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
Published: 17th, September 2025 GMT
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya yabawa Hukumar Makarantun Kimiyya da Fasaha ta Jiha bisa ƙirƙirar Kyautar Malami Mafi Nagarta, yana mai bayyana hakan da ɗaya daga cikin manyan manufofin da za su ƙarfafa koyo da koyarwa a fadin jihar.
A cikin wata sanarwa da Babban Jami’in Yaɗa Labaran sa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa bikin na farko na bada lambar yabo da aka gudanar a Dutse ya dace domin girmama malamai da suka yi fice ta hanyar jajircewa da sadaukar da kai.
Ya ƙara da cewa wannan mataki zai ƙara kwarin gwiwa, ya samar da gasa mai kyau, tare da inganta darussa a makarantu.
Namadi ya jaddada cewa ingancin ilimi bai tsaya kan gina makarantu kawai ba, yana ta’allaka ne ga ingancin malamai, kayan koyarwa da kuma yanayin makarantu.
Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta fara ɗaukar malamai tare da horas da su akai-akai domin rage cunkoson ɗalibai da malamai da kuma horar da su sabbin dabarun koyarwa.
“Wannan shiri ɗaya ne daga cikin mafi kyawu da muka gani. Idan wani ya yi kuskure, sai a hukunta shi, yayin da duk wanda ya yi fice, wajibi ne a yaba masa. Wannan shi ne yadda ake samun cigaba,” in ji gwamnan.
Ya bukaci sauran hukumomin ilimi kamar Hukumar Gudanar da Makarantun Sakandare, Hukumar Ilimin Addinin Musulunci, da Ma’aikatar Ilimin Firamare su yi koyi da wannan tsari domin ƙara ƙarfafa gwanintar malamai a dukkan matakai.
Gwamnan ya kuma sake jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da maida hankali wajen gina makarantu, horar da malamai, da walwalar su.
Ya tabbatar da cewa za a ci gaba da baiwa bangaren ilimi goyon baya don inganta sakamakon koyo a makarantu a fadin Jihar Jigawa.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Koyarwa a makarantu
এছাড়াও পড়ুন:
NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Oguntala ta bayyana cewa, ana sa ran babban ministan ma’aiktar bunkasa tattalin arziki na teku Mista Adegboyega Oyetola, zai halarci taron, wanda aka tsara za a gudanar a watan Disambar wannan shekarar a garin Ibadan.
Ta bukaci hukumar ta Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, da ta yi hadaka da kungiyar domin gudanar da taron wanda ta sanar da cewa, Shugaban Hukumar ta NPA Dakta Abubakar Dantsoho ne, zai kasance babban mai gabatar da jawabi, a wajen taron kungiyar.
Kazalika, ta yi kira ga Hukumar ta NPA, da ta dauki nauyin manyan kasidun da za a gabatar da wajen taron tare da samar da ilimi kan batun da ya shafi fannin na bunkasa tattalin arziki na teku.
Shugabar ta kuma bai wa hukumar ta NPA damar da ta yi bajin koli a yayin gudnar da taron, inda kuma ta sanar wa da hukumar ta NPA cewa, ta zabo wasu daga cikin injiniyoyin NPA da ta sanya a cikin kwamtin shiye-shiyen gudanar da taron.
Ta kuma shedawa Dantsoho cewa, wasu masu masana’antu da wasu daga bangaren gwamnati da kuma wasu daga bangaren manyan makarantun kasar nan, na da burin yin hadaka da hukumar ta NPA.
“Mun sa irin kokarin da shugaban hukumar ta NPA key i, musaman wajen kara bunkasa tattalin azrikin da ke a fannin ayyukan Tashoshin Jitagen Ruwan kasar” .
“Muna sane da cewa, ba za mu iya gudanar da gagarumin atron namu, matukar ba mu samu guduanmwar da za ku iya bamu ba, domin shirya taron a acikin nasara, musamman duba da irin gudunmawar da za ku iya bayarwa,” Inji ta.
“Ba wai muna neman hukumar ta dauki nauyin mu bane, muna kawai bukatar yin hadaka da hukumar ta NPA ne , musamman duba da irin gawaurtaccen taron da muke yin yi,” A cewar shugabar.
“Fannin na bunkasa tattalin arzikin teku, abu ne da yake ci gaba da kara tumbatsa kuma abu ne, da ke da makoma mai kyau, haka fannin ne, da har yanzu, mutane ba su gama fahimtarsa ba,” Inji ta.
Ta kara da cewa, idan aka ba za daukacin bangarorin injiniyoyin zuwa rassa guda 93 da ake da su a kasar nan da kuma sauran wadanda suke a kasar waje, hakan zai kara taimaka wa, wajen kara bunkasa kasar nan.
Shugabar ta kuma bijro da batun shigar wadanda suka samu shedar kammala karatun injiniya wadanda suka samu horo daga gun kwararrun injiniyoyi suke kuma yin aiki a hukumar ta NPA.
Ta kara da cewa, bisa matakan bin ka’ida da bangaren gudanar da mulki da kungiyar ta dauka su ne, na tabbatar da duk wanda ya karaci ilimin injiniya dole ne ya kasance ya kai mataki na goma
A na sa jawabin shugaban hukumar ta NPA Dakta Abubakar Dantsoho ya sanar da cewa, kashi 70 zuwa 80 na ma’ikatan da ke aiki a hukumar ta NPA injiniyoyi ne.
Dantsoho ya kuma bai wa shugabar kungiyar tabbacin cewa, za ta yi hadaka da kungiyar ta NSE, musamman domin a kara ciyar da kasar nan gaba, inda ya buga misali da sauran kasashen duniya da suka yi hadaka da kungiyoyin injiniyoyi wanda hakan ya ba su damar samun nasara, musamam ta hanyar yin hadaka.
Shugaban ya sanar da cewa, idan aka yi hadakar da hukum
ShareTweetSendShare MASU ALAKA