Gwamnatin Tarayya ta raba wa talakawa N330bn — Ministan Kuɗi
Published: 18th, September 2025 GMT
Ministan Kuɗi da Tsare-tsaren Tattalin Arziƙi, Wale Edun, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta raba wa talakawa Naira biliyan 330 a matsayin tallafi.
Ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a Abuja, inda ya ce an raba kuɗin ne ta Ofishin Tsare-tsaren Jin-ƙai na Ƙasa (NASSCO), domin rage wa talakawa wahalar cire tallafin mai da sauyin musayar kuɗaɗen waje.
A cewarsa, aƙalla gidaje miliyan 19.7 (sama da mutum miliyan 70) aka sanya a Rajistar Tsarin Tallafa Wa Talakawa, kum tallafin ya kai ga gidaje miliyan 15.
“Zuwa yanzu, gidaje miliyan 8.5 sun samu aƙalla Naira 25,000 sau ɗaya, wasu kuma sun samu sau biyu ko uku.
“Sauran gidaje miliyan bakwai za su karɓi tallafin kafin ƙarshen shekara,” in ji Edun.
Ya ƙara da cewa ana biyan tallafin ne ta hanyar banki ko asusun wayoyi, ta hanyar amfani da lambar NIN na kowane wanda zai ci gajiyar.
Ministan, ya ce za a ci gaba da saka shirin a cikin kasafin kuɗin shekara-shekara domin ya ɗore.
Shugabar NASSCO, Hajiya Funmi Olotu, ta bayyana cewa dalilin biyan tallafin kashi-kashi, shi ne saboda umarnin Shugaba Bola Tinubu na haɗa tsarin da lambar NIN, domin tabbatar da gaskiya.
“Ba a raba kuɗi a hannu kai tsaye kamar da. Yanzu ana biyan kuɗi ne kai tsaye ta asusun banki. Wannan ne ya sa wasu gidajen suka riga suka karɓi sau ɗaya, biyu ko sau uku,” in ji ta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Talakawa gidaje miliyan
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
A cewar Salahudeen, Ranar Yaƙi da Cutar Polio ta Duniya muhimmiyar dama ce ta faɗakar da jama’a kan barazanar da cutar shan-inna ke haifarwa ga rayuwar al’umma da tattalin arziki, tare da sake duba nasarori da kalubalen da ake fuskanta.
Ya ce haɗin kai tsakanin gwamnatin jihar da kungiyoyin bunkasa lafiya — musamman Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) — ya taimaka matuƙa wajen cimma wannan gagarumar nasara.
“Gwamna Dauda Lawal ya ayyana dokar ta-baci a bangaren lafiya, kuma hakan ya zame ginshiqin da ya taimaka wajen samun tallafi, goyon baya da isassun ma’aikata don tabbatar da an kai rigakafi ko’ina,” inji shi.
Dekta Salahudeen ya kara da cewa WHO, UNICEF, Chigari, Sultan Foundation da Salina Foundation sun taka rawar gani wajen taimakawa jihar ta isa ga dukkan al’ummomi, ciki har da yankunan da ke da wahalar kaiwa.
Ya ce, waɗannan ƙungiyoyi sun samar da tallafin kudi, kayan aiki, horo ga ma’aikatan lafiya, da kuma goyon baya wajen aiwatar da rigakafi a kananan hukumomi 14 na jihar.
Daga cikin manyan nasarorin da aka samu, a cewar shi, akwai damar kai rigakafi har ma zuwa yankunan Fulani makiyaya da wuraren da ake gani a matsayin “hard-to-reach”, baya ga tallafin jami’an tsaro da ya taimaka wajen baje kolin ayyukan rigakafi cikin kwanciyar hankali.
“An samu damar ziyarar dukkan yankuna, har da na noma da kiwo, inda muka ga cewa ba zai yuwu mu bar kowane yaro a baya ba,” inji Salahudeen.
Ya ce gwamnatin jihar za ta ci gaba da hada karfi da kungiyoyin hadaka, domin tabbatar da kawar da shan-inna baki daya, tare da cigaba da karfafa wayar da kan jama’a kan muhimmancin rigakafi.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA