Aminiya:
2025-09-17@20:31:03 GMT

Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku

Published: 16th, September 2025 GMT

Al’ummar garin Dukku a Ƙaramar Hukumar Dukku ta Jihar Gombe sun koka kan mummunan halin hanyar da ta haɗa su da babban birnin jihar, tare da kira ga gwamnati da ta gaggauta gyaran ta.

A cewar direbobi, tafiyar Dukku zuwa Gombe wadda a da take ɗaukar mintuna 50 kacal, yanzu ta koma fiye da awa biyu saboda lalacewar hanyar, abin da ke jawo gajiya da takaici ga fasinjoji da masu tuƙi.

An fara gina hanyar Gombe-Dukku-Darazo ne tun a shekarun 1980, aka gyara ta a farkon shekarun 2000. Sai dai daga baya aka yi sakaci da ita duk da kasancewarta hanyar da matafiya daga jihohin Adamawa, Taraba, Jigawa, Kano, Bauchi da wasu ke bi.

“Gyaran motoci na cinye mana kuɗi”

Usman Abubakar, direba mai shekaru 45 da gogewar tuki na sama da shekaru 19, ya ce lalacewar hanyar na sa direbobi kashe kuɗi masu yawa wajen gyaran motoci.

Bida Poly ta sa sojoji kula da jarrabawar ɗalibai ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu

“Gaskiya hanyar ta lalace matuƙa. A da tafiyar Dukku zuwa Gombe kan ɗauki mintuna 45, yanzu kuwa ko awa biyu ba ta isa ba. Rami ne a ko’ina, musamman daga Tongoyel zuwa Bojude da Bozonshulwa. Sau da dama idan ka fito da safe sai ka tarar da motoci sun tsaya cak a hanya. Shock absorber, gilashi da sauran sassan mota suna yawan lalacewa saboda ramukan hanyar,” in ji shi.

Ya ce a da ‘shock absorber’ na iya kaiwa shekara biyu kafin ya lalace, amma yanzu ko watanni uku bai yi ba sai ya karye. Hakazalika tsohon gilashi da ake siya ₦90,000 yanzu cikin sati biyu kawai sai ya fashe.

Usman ya kuma ce ya sha yin haɗura a hanyar cikin watanni biyu kacal, inda tayar motarsa ta fashe, ‘shock absorber’ ya karye, sannan kingpin ya lalace — duka sakamakon shiga ramuka.

Wani direba, Abubakar Hassan, ya ce lalacewar hanyar ta kai shi ga tunanin barin aikin tuƙi gaba ɗaya saboda asarar kuɗi.

“Idan ruwan sama ya sauka, tafiya sai ta koma tamkar azaba. Sau da dama motoci kan kwana a hanya saboda lalacewa,” in ji shi.

Fasinjoji sun bayyana ƙalubale

Kabiru Zubairu, ɗaya daga cikin fasinjojin da ke yawan amfani da hanyar, ya ce, “A da tafiyar kilomita 72 kan ɗauki mintuna 45 zuwa 60, yanzu ta koma awa biyu. Idan na taso Dukku da karfe 7:00 na safe, yanzu sai mu isa bayan 9:00. Wannan na jawo mana jinkiri sosai.”

Wani fasinja, Abubakar Aliyu, ya ce mutane da dama sun daina zuwa Gombe saboda halin hanyar. “Idan ka yi tafiya sai jikinka ya yi ciwo. Wasu matasa kan zuba yashi a cikin ramuka, amma ruwan sama yana wanke shi,” in ji shi.

Muhimmancin hanyar — Masana

Mai sharhi a harkokin jama’a, Sulaiman Sa’idu Liman, ya ce kusan kilomita 64 daga cikin 72 na hanyar Dukku zuwa Gombe sun lalace, kuma motoci yanzu ba sa iya wuce gudu na kilomita 20 a awa ɗaya.

“Hanyar na da muhimmanci ga tattalin arziki da walwalar al’umma. Ana jigilar kayan gona, kayayyakin lafiya da marasa lafiya ta wannan hanya zuwa Asibitin Koyarwa na Tarayya (FTH) Gombe,” in ji shi.

Likita Aliyu Bashir kuwa ya ce lalacewar hanyar na haifar da matsaloli ga lafiyar jama’a, musamman ƙura da ke haddasa cutar asma, da kuma haɗarin haihuwa kafin lokaci ga mata masu juna biyu saboda girgizar mota.

Kungiyoyi da direbobi sun yi kira

Shugaban Ƙungiyar Tuntuɓa ta Dukku (DCF), Muhammad Bala Hashidu, ya yi kira da a gaggauta gyaran hanyar gaba ɗaya.

Shi ma shugaban Kungiyar Direbobi ta NURTW a Dukku, Abdulhamid Hassan, ya ce kusan kowace rana ana samun aƙalla motoci 10 da ke lalacewa a kan hanyar, abin da ya rage musu kuɗin shiga.

Gwamnati ta magantu

Mai magana da yawun gwamnan Gombe, Ismaila Uba Misilli, ya tabbatar da cewa gwamnati na aiki tare da takwarorinta na Arewa maso Gabas domin samun tallafin Gwamnatin Tarayya wajen gyaran hanyar.

“Kwanan nan gwamnonin yankin sun gana da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu inda suka roƙi a gyara muhimman hanyoyi ciki har da wannan. Domin hanya ta tarayya ce, gwamnatocin jihohi ba su da ikon gyaran ta kai tsaye. Amma gwamnoni sun dage wajen ganin an gyara ta,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hanyar Dukku lalacewar hanyar lalacewar hanyar

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila

Babban daraktan kamfanin dillancin labaran kasar Qatar ya bayyana cewa taron gaggawa na kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC da ke tafe yana nuni da wani muhimmin sauyi na hadin kan kasashen larabawa da musulmi dangane da laifukan da ake aikatawa kan al’ummar Palastinu.

A cewar Pars Today, dukkanin idanuwa a ranakun Lahadi da Litinin (15-16 ga Satumba, 2025) za su kasance a Doha, babban birnin kasar Qatar, wanda zai karbi bakuncin taron gaggawa na shugabannin kasashen Larabawa da na Islama, don ba da amsa ga baki daya kan harin da Isra’ila ta kai kan Qatar.

Ana gudanar da wannan taron gaggawa ne a cikin yanayi na musamman na yanki da na duniya kuma ya biyo bayan harin da Isra’ila ta kai kan Qatar. Ana dai kallonsa a matsayin wani gagarumin sauyi ba wai kawai dangane da batun Falasdinu ba, har ma da sauran ci gaban siyasa a yankin.

A cikin wannan mahallin, masana da kwararru kan harkokin yada labarai na Qatar sun jaddada cewa zaluncin da Isra’ila ke yi wa Qatar ya farfado da ra’ayin kishin kasa na Larabawa tare da sake fasalin wasu muhimman batutuwan yankin.

Hadin kan Matsayin Larabawa da Musulunci

Ahmed Al-Rumaihi, Darakta-Janar na Kamfanin Dillancin Labarai na Qatar, ya ce hanyar shari’a ta kasa da kasa ita ce mafi kyawu kuma zabin da ya dace don tunkarar ci gaba da keta haddin ‘yan mamaya na (Sionist) – na farko daga cikin laifuffukan da aka rubuta da Benjamin Netanyahu, Firayim Ministan Isra’ila ya yi. Kotunan duniya, musamman kotun shari’a ta duniya, sun kafa sharuɗɗa da yawa waɗanda ke tabbatar da girman waɗannan laifuka.

Al-Rumaihi ya kara da cewa, ana ci gaba da yin Allah-wadai da wannan mugunyar ta’addancin da Isra’ila ke yi wa kasar Qatar, a duniya, kuma wannan ba wani abu ba ne, illa dai sakamakon yadda duniya ke kara wayar da kan jama’a game da keta haddin majalisar ministocin Isra’ila.

Farfado da Ra’ayin kishin Kasa

Babban editan jaridar Al-Sharq na kasar Qatar Jaber Al-Harami ya bayyana cewa, ha’incin da Isra’ila ta yi wa Qatar ya farfado da ra’ayin kishin kasa na Larabawa zuwa wani mataki da ba a taba ganin irinsa ba, wanda ke karfafa imanin cewa ba kasa daya ba ce kawai, yankin gaba daya. Al-Harami ya jaddada cewa, Isra’ila ba ta amince da wani jan layi ba, ba ta bi yarjejeniyoyin da aka kulla ko yarjejeniya ba, a maimakon haka tana aiwatar da munanan manufofin ba tare da la’akari da ka’ida ba.

A cewar Al-Harami, ta hanyar wannan wuce gona da iri Isra’ila na neman kafa sabbin sharudda da bukatu a karkashin shirin da ake kira “Isra’ila Babba”, inda ta sanya kasashen Larabawa a gaban wani zabi na wanzuwa. Don haka wajibi ne taron na Doha ya tashi daga kace-nace zuwa aiki na hakika.

Hakazalika, Nasser Al-Azba, wani lauya na kasa da kasa, ya jaddada cewa, lokaci ya yi da ya wuce yin Allah wadai da take-take, maimakon daukar matakai masu amfani da kuma daukar matakai masu inganci a kasa.

Al-Azba ya bayyana cewa, harin da Isra’ila ta kai kan Qatar a baya-bayan nan, ya nuna karara karya ce ga yarjejeniyar Vienna ta 1968, wadda ta kafa tsarin doka na kare jami’an diflomasiyya da masu shiga tsakani na kasa da kasa. A tarihi, manzanni sun kasance suna samun cikakkiyar kariya, kuma wannan ka’ida tana cikin dokokin duniya a yau.

Lauyan dokar kasa da kasa ya kara da cewa mayar da martani bai kamata ya takaita ga matakan shari’a ba, amma kuma dole ne ya hada da kulla kawance da kasashe da ba na yammacin Turai ba kamar su China, Rasha, da kasashen BRICS, yayin da a lokaci guda za a tattara ra’ayoyin jama’a na duniya don fallasa irin ta’addancin Isra’ila.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025  Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan:  Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •   Iran Ta Yi Nasarar Gwajin Tauraron Dan’adam ” Nahid 2″ Da Zai Samar Wa Yankunan Karkara Hanyar Sadarwa Ta “Internet”
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff
  • Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba