Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-09-18@09:08:53 GMT

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Gumi

Published: 18th, September 2025 GMT

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Gumi

Mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Mani Malam Mumini ya jajanta wa al’ummar karamar hukumar Gumi kan mumunan al’amuran da suka salwantar da rayukan mazauna kauyen Fas su 19 a makonnin da suka gabata.

 

Malam Mumini ya bayyana haka ne a lokacin da ya jagoranci wasu jami’an gwamnati da suka kai ziyarar jaje ga al’umma, inda ya jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa, da Majalisar Masarautar, da daukacin al’ummar Gumi.

 

Ya bayyana bala’in a matsayin mai raɗaɗi, yana mai jaddada cewa, gwamnatin jihar ta himmatu wajen magance matsalolin.

 

Mataimakin Gwamnan ya tuna cewa lamarin na farko ya faru ne a lokacin da mazauna kauyen cikin firgici kan harin da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne suka kai, suka shiga cikin wani jirgin ruwa wanda a karshe ya kife sakamakon kifewar da ya yi, wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dama.

 

Ya kuma bayyana cewa, a yayin da bala’i na biyu ya faru kwanaki bayan wata motar bus ta Homa dauke da ‘yan  daurin aure ta kutsa cikin kogin Gwalli a kan hanyar da ta wuce kan gada mai dauke da yashi, inda mutane 19 suka mutu.

 

Ya yi nuni da cewa, duk da cewa dan majalisar da ke wakiltar yankin ya gabatar da kudiri a kan munin yanayin gadar, amma har yanzu ana duba lamarin a lokacin da bala’in ya afku.

 

Mani Malam Mumini ya ce tuni gwamnatin jihar ta aike da tawagar injiniyoyi domin tantance gadar da kuma hanyoyin da suka hada da juna.

 

Wani shugaban al’umma a Gwalli ya yi kira da a kawo dauki cikin gaggawa tare da jaddada muhimman dabarun hana gadar ta ruguje nan gaba.

 

Shima da yake nasa jawabin mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Zamfara, Adamu Aliyu Gumi, ya bayyana wannan lamari a matsayin babban rashi ga al’umma, ya kuma yi kira da a gaggauta daukar mataki na gaggawa domin kaucewa afkuwar bala’o’i.

 

A yayin ziyarar, Mataimakin Gwamnan ya kuma kai gaisuwar ban girma ga Mai Martaba Sarkin Gumi, Mai Shari’a Lawal Hassan mai murabus, tare da jajanta masa bisa wannan al’amarin da aka samu.

 

A nasa jawabi, mai martaba Sarkin Gumi, Mai Shari’a Lawal Hassan ya bukaci gwamnatin jihar da ta hada kai da hukumar kula da hanyoyin ruwa ta kasa NIWA domin samar wa majalisar jiragen ruwa na zamani domin rage yawaitar hadurran jiragen ruwa.

 

Mai shari’a Hassan ya koka da cewa, kwalekwalen katako na gargajiya da ake amfani da su a halin yanzu ba su da tsaro kuma suna tabarbarewa cikin sauri, suna jefa rayuka cikin hadari.

 

Sarkin ya kuma yabawa gwamnatin jihar bisa kudurin da ta dauka na magance matsalar rashin tsaro da kuma kalubalen da ke addabar jihar.

 

Tun da farko, shugaban karamar hukumar Gumi, Aminu Nuhu Falale, ya kuma bukaci a kara kaimi wajen samar da tsaro musamman a yankin Birnin Magaji, saboda karuwar hare-haren ‘yan bindiga.

 

Ya bayyana cewa, hatsarin kwale-kwale na karshe ya samo asali ne sakamakon firgici yayin da mutanen kauyen suka yi yunkurin tserewa daga hannun ‘yan bindiga, lamarin da ya kai ga kifewar kwale-kwalen.

 

COV/AMINU DALHATU

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ta aziya Zamfara gwamnatin jihar

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.

 

Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.

 

Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.

 

Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.

 

Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.

 

Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Zamfara Ta Nemi Karin Tallafi Ga ‘Yan Gudun Hijira
  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja