A cewar ma’aikatar, dakatarwar ta na nufin samar da damar ci gaba da tattaunawa da duk masu ruwa da
tsaki da kuma yin cikakkiyar bitar tsarin harajin da tasirinsa na dogon lokaci ga tattalin arziki.
A watan Afrilu 2025, Kwaturola Janar na Kwastom, Adeniyi, ya bayyana shirin sake gabatar da harajin
kashi 4 bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki, cewa wannan cajin, wanda ake lissafawa bisa Free on
Board (FOB) na kayan da ake shigowa da su, an riga an sokƙ shi a baya daga al’umma masu kasuwanci
saboda nauyinsa ga masu shigo da kaya.

Nan da nan sanarwar ta jawo cece-kuce daga ƴ an kasuwa, kamfanonin jigilar kaya, da ƙungiyoyin
masana’antu, waɗanda suka bayyana cewa matakin zai rage amincewar masu zuba jari kuma ya rage jan
hankalin da Nijeriya ke yi a matsayin cibiyar kasuwanci.

Ma’aikatar kuɗi ta fayyace cewa dakatarwar ba ta nufin soke harajin, sai dai mataki ne na dakatarwa
domin sake duba yiwuwar tasirin harajin. Ma’aikatar ta jaddada ƙudurin gwamnati na daidaita samun
kuɗaɗen shiga tare da bunƙasa tattalin arziki.

“Ma’aikatar Kuɗi na sa ran yin aiki kafaɗa da kafaɗa da Hukumar Haraji ta Nijeriya (NCS) da duk masu
ruwa da tsaki domin shirya tsarin samun kuɗaɗe cikin adalci da inganci wanda zai tallafa wa kuɗaɗen
gwamnati ba tare da lalata harkokin kasuwanci ko daidaiton tattalin arziki ba,” in ji sanarwar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai November 3, 2025 Daga Birnin Sin Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka November 3, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan November 3, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Kaduna Ta Amince da Dokar Kafa Hukumar Fasahar Sadarwa da Tattalin Arzikin na Zamani
  • Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
  • Abba ya umarci a riƙa gudanar da taron tsaro a ƙananan hukumomin Kano
  • An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau
  • Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
  • NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka