Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce
Published: 19th, September 2025 GMT
A cewar ma’aikatar, dakatarwar ta na nufin samar da damar ci gaba da tattaunawa da duk masu ruwa da
tsaki da kuma yin cikakkiyar bitar tsarin harajin da tasirinsa na dogon lokaci ga tattalin arziki.
A watan Afrilu 2025, Kwaturola Janar na Kwastom, Adeniyi, ya bayyana shirin sake gabatar da harajin
kashi 4 bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki, cewa wannan cajin, wanda ake lissafawa bisa Free on
Board (FOB) na kayan da ake shigowa da su, an riga an sokƙ shi a baya daga al’umma masu kasuwanci
saboda nauyinsa ga masu shigo da kaya.
Nan da nan sanarwar ta jawo cece-kuce daga ƴ an kasuwa, kamfanonin jigilar kaya, da ƙungiyoyin
masana’antu, waɗanda suka bayyana cewa matakin zai rage amincewar masu zuba jari kuma ya rage jan
hankalin da Nijeriya ke yi a matsayin cibiyar kasuwanci.
Ma’aikatar kuɗi ta fayyace cewa dakatarwar ba ta nufin soke harajin, sai dai mataki ne na dakatarwa
domin sake duba yiwuwar tasirin harajin. Ma’aikatar ta jaddada ƙudurin gwamnati na daidaita samun
kuɗaɗen shiga tare da bunƙasa tattalin arziki.
“Ma’aikatar Kuɗi na sa ran yin aiki kafaɗa da kafaɗa da Hukumar Haraji ta Nijeriya (NCS) da duk masu
ruwa da tsaki domin shirya tsarin samun kuɗaɗe cikin adalci da inganci wanda zai tallafa wa kuɗaɗen
gwamnati ba tare da lalata harkokin kasuwanci ko daidaiton tattalin arziki ba,” in ji sanarwar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai November 3, 2025
Daga Birnin Sin Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka November 3, 2025
Daga Birnin Sin Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan November 3, 2025