Cutar Kwalara ta kashe mutum 58 a Bauchi
Published: 19th, September 2025 GMT
Aƙalla mutane 58 ne aka tabbatar da mutuwarsu sakamakon barkewar cutar Kwalara a ƙananan hukumomi 14 daga cikin 20 da ke jihar Bauchi.
Haka kuma, an samu sabbin mutane 258 da suka kamu da cutar a faɗin jihar.
Amurka ta hau kujerar-na-ƙi kan buƙatar MDD ta tsagaita wuta a Gaza An yanke wa Soja hukuncin kisa ta hanyar ratayaMataimakin Gwamnan jihar, Auwal Mohammed Jatau, ne ya bayyana hakan yayin ƙaddamar da wasu kwamitoci biyu kan yaki da cutar a jihar.
Mataimakin Gwamnan ya nuna damuwarsa kan yadda barkewar cutar ke ci gaba da kashe mutane, lalata rayuwar jama’a, da kuma jefa tsarin kiwon lafiya na jihar cikin matsala.
Jatau ya bayyana cewa: “Ana iya kaucewa wannan barkewar cutar idan aka ɗauki matakan gaggawa, aka haɗa kai wajen tunkarar cutar, tare da ci gaba da inganta ruwa, tsafta da kula da muhalli. Jihar Bauchi ta samu sabbin mutane 258 da suka kamu da cutar, tare da mutuwar wasu 58.”
Ya ƙara da cewa duk da ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi, Kwalara na ci gaba da zama barazana ga lafiyar jama’a.
Ya ce kafa kwamitin yaki da cutar ba wai kawai ya zo a kan lokaci ba, har ma yana da matuƙar muhimmanci wajen cimma burin da aka sa gaba na dakile ci gaba da yaduwarta.
A cewarsa: “Wannan kwamitin zai zama ja-gaba wajen jagorancin hukumomin gwamnati a jihar Bauchi kan barkewar Kwalara, tare da tsara dabarun kariya na dogon lokaci da suka yi daidai da Tsarin Ƙasa na Yaki da Cholera da kuma manufofin Cibiyar Dakile Cututtuka ta Najeriya (NCDC).”
Mataimakin gwamnan ya tunatar da mambobin kwamitocin cewa zaɓensu ya nuna ƙwarewarsu, sadaukarwarsu da muhimmancin rawar da za su taka wajen nasarar aikin, tare da fatan za su tabbatar da sa ido, gano cuta da wuri, da kuma ɗaukar matakin gaggawa idan ta barke.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kwalara
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
Ya ce ya sayi layin wayar ne daga hannun wani Audu, ɗan kungiyar Vikings wanda ya tsere yanzu.
A wani lamari kuma, ‘yansanda sun kama wasu mutum huɗu da suka shiga gonar wani mutum a Lapai Gwari, inda suka saci kifi da darajar kuɗinsu ta kai Naira 750,000.
Babban wanda ake zargi, Hussaini Garba, ya amsa laifi tare da bayyana Ahmed Yusuf, Ibrahim Musa da Abdulazeez Bawa a matsayin mutanen da suke sayen kifin idan ya sato.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp