Aminiya:
2025-11-04@14:53:12 GMT

Matasan Nijeriya sun koma yin ci-rani a Nijar da Chadi

Published: 19th, September 2025 GMT

A yau a Nijeriya, kalmar “Japa” ta zama gamagari wajen bayyana yadda matasa da dama ke barin ƙasar domin neman ingantacciyar rayuwa a wasu ƙasashe.

Abin da ya bambanta shi yanzu shi ne inda suke nufa: ba kawai Turai da Amurka ba kawai, har ma da ƙasashen Afirka maƙwabta.

Yawaitar tsadar rayuwa da ƙarancin ayyukan yi da rashin tsaro, da kuma faɗuwar darajar Naira sun sanya matasa su fara duba wasu ƙasashen Afirka a matsayin mafaka.

Mutum 1,666 ne suka kashe kansu a Legas cikin shekaru biyar – ’Yan sanda Akasarin masu kai mana hare-hare daga jihohin da suka kewaye mu suke – Gwamnatin Filato

Maimakon tsallaka tekun Bahar Rum da haɗarin mutuwa, da dama daga cikinsu sun fara kallon ƙasashen Nijar da Chadi da Mali, Kwat D’Ibuwa da Kamaru da Jamhuriyar Binin a matsayin wuraren da za su iya fara sabuwar rayuwa.

Binciken Aminiya ya gano cewa, a yau dubban matasa daga Arewa da Kudancin Nijeriya sun tsere zuwa maƙwabtan ƙasashe, inda suke gudanar da sana’o’i ko haƙar ma’adinai ko shiga kasuwancin canjin kuɗi. Wasu ma sun koma neman ilimi a jami’o’in ƙasashen da suka fi samun kwanciyar hankali.

Masu lura da al’amura sun ce wannan sabon salo na hijira ko ci-rani yana nuna yadda matsalolin Nijeriya suka tsananta, har matasa ke ganin ƙasashen da a da suke kallo a matsayin marasa ci-gaba sun fi tasu sauƙin rayuwa.

Rayuwar baƙin haure

A biranen Nijar, musamman Maraɗi da Yamai, ana iya ganin ɗimbin ’yan Nijeriya suna gudanar da ayyukan yau da kullum. Wasu suna zama a ƙauyuka, wasu kuma a cikin manyan birane.

Rayuwarsu ba ta da sauƙi, amma duk da haka suna ganin ta fi ta gida sauƙi. Daga ƙakin haya mai cunkoso da suke raba shi tare da abokan tafiyarsu, zuwa cin abinci mai sauƙi kamar tuwon gero da miyar kuɓewa, matasan suna jurewa don cimma manufar da ta kawo su ta samun abin dogaro da kai.

Habibu Abdullahi, matashi daga Maiduguri, ya ce: “A da ’yan Nijar ne ke zuwa Nijeriya domin neman aiki. Amma yanzu mu ne muke zuwa wajensu saboda CFA ta fi Naira ƙarfi.”

Wasu kuma sun ce rayuwar baƙin haure tana da tsada, amma ribar da suke samu daga sana’o’in da suke yi na sa su ci gaba da zama.

Sana’o’in da suke yi

A Maraɗi da Zinder, sana’ar ɗinki ta zama abin dogaro ga ɗimbin matasan Nijeriya. Umar Mukhtar, tela ne daga Katsina, ya ce: “A nan kullum akwai kwastomomi. A Kano zan iya shafe mako ba tare da na yi ɗinki ba, amma a nan babu ranar da babu aiki.”

Umar Papa, wanda ya kammala karatun Biochemistry amma bai samu aiki a Nijeriya ba, yanzu yana aikin gini a Nijar. Ya bayyana cewa a rana ana biyan shi CFA3,000 zuwa CFA5,000, wato fiye da Naira 10,000. A wata guda, zai iya tara har N400,000 — abin da bai taɓa tsammani ba a gida.

Nasir Mustapha daga Malumfashi, kafinta ne da ya koma Nijar. A cewarsa, “A Nijeriya aikin kafinta yana da wahala saboda babu rarraba aiki. Amma a nan zan iya yin kujera guda na samu N65,000 a cikin kwana uku, alhali a gida sai na wahala in samu rabin hakan.”

A Djado, wani yanki mai tazara daga Maraɗi, matasa daga Nijeriya sun shiga sana’ar harkar haƙar zinari. Abdulkareem Dogo, wanda ya kammala karatu a Jami’ar Maiduguri, ya ce: “Haƙar zinari tana da haɗari, amma tana da riba. Gram ɗaya da aka tace zai iya kaiwa N170,000.”

Ya bayyana yadda suke shiga ramuka masu zurfi fiye da kafa 150, suna rataye da igiya, suna tono ƙasa cikin zafi da ƙura. A rana sukan yi zango guda na awa shida, sannan a fita wasu su shiga. Duk da haɗarin da ke tattare da wannan sana’a, yawanci matasan suna ci gaba da shiga saboda fatan samun arziki cikin sauri.

A biranen Diffa da Ƙonni, matasan Nijeriya sun kafa kasuwancin hada-hardar kuɗi ta POS da canjin kuɗi. Malam Musa Abdulƙadir, wanda ya buɗe ofishinsa shekaru biyu da suka gabata, ya ce, “A yau Naira ce ke yawo a kasuwannin kan iyaka, amma ana juya ta zuwa CFA domin samun ribar canji.”

A bara, CFA1,000 ana canza ta a kan N1,870, amma yanzu ta kai N2,800 — alamar yadda darajar Naira ke ci gaba da faɗuwa. Wannan ya sanya kasuwancin canjin kuɗi zama wata hanya ta samun kuɗin shiga mai yawa ga matasa.

Matsalolin da suke shiga

Duk da nasarar da wasu suka samu, akwai ƙalubale da dama. Mafi girma daga ciki akwai:

Wahalar zama: Mafi yawa daga cikin matasan na rayuwa ne a ƙakunan haya masu cunkoso. Mutum uku ko huɗu na kwana a ɗaki ɗaya, suna raba shimfiɗa.

Haɗarin lafiya: Rashin isasshen abinci mai gina jiki, gajiyar aiki da kuma rashin samun isasshen jinya suna jefa su cikin haɗari.

Takurar jami’an tsaro: A wasu lokuta ’yan sanda ko sojojin ƙasashen da suke ciki na tsangwamar su, suna karɓar cin hanci ko kuma suna korar su saboda rashin takardun zama.

Haɗarin sana’a: Musamman a haƙar zinari, inda rami zai iya ruftawa ya binne masu aiki gaba ɗaya. Wasu kuma suna shaƙar ƙura da hayaƙi har su kamu da cututtuka.

Alherin da suke samu

Duk waɗannan ƙalubale, matasan sun bayyana alherai da nasarorin da suke samu.

Ibrahim Lawal, mai san’ar ɗinki a Mali ya ce, “Na tafi Bamako ne bayan na gaji da zama Kano babu aiki. A nan ina samun CFA100,000 a wata, abin da ya fi abin da zan iya samu a gida gaba ɗaya.”

Shi ko Mubarak Musa ɗan kasuwa a Abidjan, ya ce, “Na fara sayar da kayayyakin gwanjo a Abidjan. Yanzu duk wata ina iya samun N500,000. Duk da cewa aikin na da wahala, amma aƙalla ina iya tallafa wa iyali na a gida.”

Deborah Ufedou, ɗaliba a Binin ta ce, “Na tsere ne saboda yajin aiki ASUU (Ƙungiyar Malaman Jami’a) domin na iya kammala karatu. A lokaci guda na fara sayar da kilishi da dambun nama. A kowane mako ina kashe N170,000 amma ribata na kaiwa N400,000 zuwa N430,000.”

Kira ga gwamnati

Matasan da muka yi hira da su sun roƙi gwamnati ta samar da ayyukan yi a gida, ta taimaka wa matasa su sami tallafin jari, sannan ta inganta tsaro domin a rage gudun hijira, sa’annan ta sauƙaƙa tsarin kasuwanci domin matasa su iya yin sana’a ba tare da wahala ba.

Habibu Abdullahi ya ce: “Idan gwamnati ta samar da aiki da tsaro, babu wanda zai bar iyalinsa ya shiga ƙasashen da ba ya jin harshensu. Amma muna barin gida ne saboda babu madadin.”

Tsohon jakadan Nijeriya, Mohammed Ibrahim, ya bayyana cewa wannan sabon salo na hijira alama ce ta tsanani da ƙasar ke ciki. A cewarsa, “Tun da daɗewa matasa kan yi hijira, amma abin da ya bambanta yanzu shi ne yawansu ya ƙaru kuma sun fi karkata zuwa ƙasashen Afirka.”

Ya kuma ba da labarin wata tawaga ta diflomasiyya a shekarar 2006 tare da jakadun Jamus da na Birtaniya a lokacin, wanda ya yi tattaki daga birnin Tripoli na Ƙasar Libya ta cikin hamadar Sahara zuwa Nijar da Nijeriya.

Ya ce, tafiyar ta taƙaita ne saboda tsananin yanayi da aka fuskanta a cikin sahara.

Da yake tsokaci a kan yanayin ƙaura, ya ce ƙauran da ’yan Nijeriya ke yi zuwa wasu ƙasashe ba na gefe ɗaya ba ne. ‘’Kamar yadda mutane ke ganin ’yan Nijeriya na yin hijira zuwa wasu ƙasashe, ‘akwai wassu mutane daga ƙasashe da dama daga ƙasashen Afirka da ke maƙwabtaka da su ma suna ƙarasowa suna shiga Nijeriya don neman ingantacciyar dama na rayuwa da samun sana’a mai nagarta.

Masu nazari sun ce idan aka ci gaba da barin lamarin haka, Nijeriya za ta ci gaba da rasa matasa masu ƙwarewa. Wannan kuma zai shafi tattalin arzikin ƙasar nan gaba.

Rahoton Aminiya ya nuna cewa “Japa” zuwa ƙasashen Afirka ba wai ba ce mafita ga matasa ba ce kawai, illa ce kuma ga Nijeriya baki ƙaya.

Idan gwamnati ta yi watsi da matsalolin da suka haddasa wannan hijira, za a iya wayan gari matasa da dama sun bar ƙasar, wanda hakan zau bar giɓin da zai wahalar da tattalin arziki da ci-gaban ƙasa.

Fassara: Ahmed Ali, Kafanchan da Ahmed Muhammad Bauchi

Rahotanni Daga Tijjani Ibrahim ( Maradi) da Sani Ibrahim Paki (Kano) da Hamisu Kabir Matazu (Maiduguri) da Gbenga Adebayo da Eugene Agha (Lagos) da kuma Willie Bassey (Yenagoa)

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ci rani Najeriya Nijar a wasu ƙasashe Nijeriya sun

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza

Gwamnatin mamayar Isra’ila ta yanke hukuncin kisa kan masu fama da cutar kansa da kuma waɗanda suke fama da matsalar koda na mutuwa a Gaza domin hana fitar da su wata kasa don neman magani

Cibiyar Kare Hakkin Dan Adam ta Gaza ta bayyana matukar damuwarta game da tabarbarewar lafiyar marasa lafiya da ke fama da cutar kansa da kuma cutar koda a Zirin Gaza. Wadannan cututtuka sun kara ta’azzara ne sakamakon hare-haren sojojin mamayar Isra’ila kan Gaza da kuma ci gaba da killace yankin bayan tsagaita bude wuta, gami da hana shigar dq magunguna da kayayyakin ayyukan likitanci masu muhimmanci cikin yankin. Cibiyar ta kuma yi nuni da tsauraran matakan fitar da marasa lafiya zuwa ƙasashen waje don neman magani.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Lahadi, Cibiyar ta tabbatar da cewa, wannan yanayin ba shi da wata shakka cewa Isra’ila na aiwatar da manufar kisan gilla a kan dubban marasa lafiya ta hanyar hana su ‘yancinsu na rayuwa da magani da gangan, da kuma canza wahalarsu zuwa wani nau’in hukunci na gama gari.

Cibiyar ta ambaci majiyoyin lafiya da ke tabbatar da cewa, akwai marasa lafiya 12,500 da ke fama da cutar kansa a Zirin Gaza, ciki har da ƙananan yara. Ta lura cewa mata sun kai kusan kashi 52% na dukkan masu cutar kansa a Gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karuwanci da zubar da cikin ’yan mata ’yan gudun hijira ya karu a Maiduguri
  • Kasar Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya saboda  Dalilan Tsaro
  • Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro
  • Kano Pillars ta koma ƙarshen teburin Gasar Firimiyar Nijeriya
  • Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT
  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada