Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
Published: 17th, September 2025 GMT
Gwamnatin Kano ta raba kayayyakin aiki na zamani na kimanin Naira Miliyan 250 ga cibiyoyin horas da sana’o’in hannu biyu da ke Kofar Mata da Gwale, domin yaƙi da shan miyagun kwayoyi da aikata laifuffuka a tsakanin matasa, ta hanyar samar da aikin yi.
Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Dakta Yusuf Kofarmata, ya ce an amince da tallafin ne bisa umarnin Gwamna Abba Kabir Yusuf don bunƙasa tsare-tsaren ƙarfafa matasa a jihar.
Ya bayyana cewa an samar da injinan sarrafa fata guda 26 domin cibiyoyin wadanda al’ummar yankunan suka kafa, amma ba su da isassun kayayyakin aiki.
Ya ce Gwamna Yusuf ne ya gina Cibiyar Horaswar ta Gwale kasancewar nan ce mazabarsa, yayin da Dakta Yakubu Adam ya taka rawa wajen gina ta Kofar-Mata.
Ya ce cibiyoyin za su samar da daruruwan ayyukan yi tare da rage matsalolin zaman kashe-wando da ta’addanci a tsakanin matasa.
A nasa jawabin, Ali Musa Kofar-Mata na ƙungiyar IKMA ya gode wa gwamnati bisa wannan gudummawar da ya kira mai sauya rayuwa.
Ya ce cibiyar ta fara ɗaukar matasa maza da mata, kuma horon zai ɗauki watanni uku kafin a shiga sabon zagaye.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Shiyyar Kano (KEDCO) ya ƙaryata zargin da Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) ya yi masa, dangane da mutuwar wasu marasa lafiya sakamakon katse wutar lantarki da aka ce kamfanin ya yi.
Asibitin na AKTH ya bayyana damuwarsa a ranar Lahadi kan abin da ya kira abin takaici yana mai cewa mutanen da suka mutu za su iya tsira da ransu da ba a ɗauke wutar ba.
Amma a martanin da ya bayar, Shugaban Sashen Hulɗa da Jama’a na KEDCO, Sani Bala Sani, ya ce asibitin na ƙoƙarin ɓata sunan kamfanin ne kawai, domin an dawo da wutar tun kafin asibitin ya fitar da wannan sanarwar.
Sani ya bayyana cewa matsalar ta samo asali ne daga wani yunƙurin da ake yi na raba ginin asibitin da cibiyoyin lafiya daga gidajen ma’aikatan asibitin.
“Cibiyar asibitin da cibiyoyin lafiya suna da alaƙa da layin 33kV na Zariya Road wanda aka fi ba fifiko wajen raba wuta, kuma suna samun kimanin sa’o’i 22 na wutar lantarki a kullum ƙarƙashin tsarin Band A.
“Amma, shugabannin AKTH sun dage cewa sai gidajen ma’aikata sun ci gaba da kasancewa a layin wutar lantarki ɗaya da cibiyoyin lafiya. Wannan ya janyo barazana ga inganci da kwanciyar hankali na wutar da aka ware wa asibitin.
“An yi ƙoƙari sau da dama don raba gidajen ma’aikata daga cibiyoyin lafiya, amma haƙarmu ba ta kai ga cimma ruwa ba saboda ƙin amincewar shugabannin asibitin. Abin takaici, wannan ya haifar da matsala mai tsanani da ta janyo katsewar wutar da muke ƙoƙarin kaucewa,” in ji KEDCO.
Don tabbatar da wutar lantarki ba tare da katsewa ba ga asibitin, kamfanin KEDCO ya ce yana ci gaba da aikin raba layukan wutar lantarkin biyu. Ya ce annan mataki ya zama dole don tabbatar da inganci, tsaro da kyautata lantarki ga asibitin.
Kamfanin ya kuma zargi asibitin da rashin biyan kuɗin wutar lantarki da gidajen ma’aikata ke amfani da ita, wanda ke shafar ingancin ayyukan samar da wuta na kamfanin.
KEDCO ya ce a cikin wata wasiƙa da ya aike ranar 12 ga Agusta, 2025, Babban Jami’in Kasuwanci na kamfanin, Muhammad Aminu Ɗantata, ya sanar da Shugaban Asibitin AKTH game da shirin dakatar da samar da wutar lantarki ga gidajen ma’aikata da wuraren da ba su da muhimmanci, sakamakon rashin cikakken biyan kuɗin wutar wata-wata.
Wasiƙar ta bayyana cewa:
“Duk da roƙon da aka yi sau da dama, asibitin ya ƙi biyan cikakken kuɗin wutar da yake sha a duk wata.
Wannan ya haifar da bashin wutar lantarki da ya kai ₦949,880,922.45 a watan Agustan 2025.
“An bukaci asibitin ya biya kuɗin watan Agusta 2025 na ₦108,957,582.29 gaba ɗaya cikin kwanakin aiki 10, don kaucewa yanke wuta a wuraren da abin ya shafa,” in ji wasiƙar.
Kamfanin ya ƙuduri aniyar ci gaba da samar da wutar lantarki ba tare da katsewa ba ga AKTH a matsayin babbar cibiyar lafiya.
A ƙarshe, KEDCO ya roƙi shugabannin asibitin da su ba da haɗin kai a aikin raba layukan wutar, wanda ya ce yana da amfani ga marasa lafiya, ma’aikata, da al’umma baki ɗaya.