Leadership News Hausa:
2025-07-26@07:49:04 GMT

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

Published: 6th, June 2025 GMT

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

Ya ke ‘yar uwa mai albarka,idan kina da ‘ya a gidan aure ko kanwa,don Allah mu tuntube su ranar Sallah mu ji halin da suke ciki su da jikokinki, wannan lokaci ne da za ki taimaka musu don ganin farin cikin su, abin akwai wahala a Sallah ka ji gida shiru ba labari, don Allah iyaye a taimaka ma yaran da suke gidan aure.

Sannan makota masu karfi ku duba girman Allah ku yi sadaka idan kun yi yanka, ana raba naman Sallah uku, na amfanin gida, sadaka ma mabukata da kuma na kyauta ma, ‘yan uwa da abokan arziki, hakan zai taimaka wajen kowa ya yi walwala ya san Sallah ake yi.

Shekarar da ta wuce wata ke ba da labari ta ce, “Shekarun da suka wuce makotanta shanu biyu suka yanka da raguna wanda suke kallon juna, dayan makwabtan kuma shanu da raguna, amma ba wanda ya aiko musu sadaka ga yara ta kulle su a gida ta hana kowa fita, Jama’a wannan wane irin makotaka ne Sallah guda. Allah ya sa mu gane.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Ba Da Agajin Jin Kai Ta ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinawa Ta “UNRWA” Ta Sanar Da Kashe Ma’aikatan 330 A Gaza

Hukumar ba da agaji da kula da ‘yan gudun hijirar Falasdinawa ta “UNRWA” tana karkashin wuta sakamakon ma’aikatan 330 da suka yi shahada kuma aka lalata cibiyoyinta 300 a Gaza!

Inas Hamdan, mai magana da yawun hukumar ta UNRWA a birnin Alkahira, ta tabbatar da cewa; Yunwar da ke faruwa a zirin Gaza, wani bala’i ne da ba a taba ganin irinsa ba, wanda ya shafi mutane sama da miliyan biyu, ciki har da akalla yara miliyan daya. Wannan ya saba wa duk dokokin jin kai da ka’idoji, kuma abin takaici, lamarin yana da kara muni.

Hamdan ta yi nuni da cewa, a lokacin da suke magana kan matsalar agajin jin kai ko shigar da kayan abinci zuwa zirin Gaza, suna fuskantar shamaki da aka sanya a zirin Gaza, baya ga tsarin rabon da wata gidauniya mai suna Gazan Humanitarian Foundation ke gudanarwa, wanda ke zama tarkon mutuwa. Ya zuwa yanzu, fiye da mutane dubu sun mutu yayin da suke jiran abinci, haƙƙin duk mazauna cikin wannan mawuyacin yanayi.

Ta yi gargadin cewa matakan karancin abinci na ci gaba da tabarbarewa, inda ya kai matakin da ba a taba ganin irinsa ba da kuma matukar damuwa. Adadin matsalolin rashin abinci mai gina jiki, musamman a tsakanin yara, yana nuna mummunar tabarbarewa a wannan fanni. Akalla yara 5,500 ‘yan kasa da shekaru biyar ne ke fama da matsananciyar rashin abinci mai gina jiki, ciki har da yara akalla 800 da ke cikin matsanancin hali na rashin abinci mai gina jiki, ma’ana suna fuskantar barazanar yunwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An yanke wa mutum 3 hukuncin kisa kan kisan kai a Gombe
  • ‎Sarkin Katsinan Gusau ya rasu
  • Hukumar Ba Da Agajin Jin Kai Ta ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinawa Ta “UNRWA” Ta Sanar Da Kashe Ma’aikatan 330 A Gaza
  • Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau
  • Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (4)
  • Fiye Da  Falasdinawa 111 Ne Su Ka Yi Shahada Saboda Yunwa A Gaza
  • Matar aure ta kashe mijinta a kan abinci a Yobe
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace
  •  Fiye Da  Kungiyoyin 100 A Duniya Sun Yi Gargadi Akan Halin Yunwa Da HKi Ta Jefa Mutanen Gaza A Ciki
  • Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa