Uba ya harbe ɗansa bisa saboda zaton biri ne
Published: 2nd, June 2025 GMT
Wani yaro ɗan shekara 15 ya rasa ransa bayan mahaifinsa ya harbe shi bisa kuskure, yana zaton biri ne.
Wannan lamari mai ban tausayi ya faru ne a gonar magidancin inda shi da ɗan nasa suke aiki, a yankin Iye Ekiti da ke Ƙaramar Hukumar Ilejemeje ta Jihar Ekiti.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Ekiti, Joseph Eribo, ya tabbatar da faruwar lamarin a yau a Ado-Ekiti.
Ya bayyana cewa manomin ya daɗe yana fama da hare-haren birai a gonarsa kuma ya kai bindiga domin kare amfanin gonarsa.
Jirgin soji ya kashe ’yan sa-kai 20 da ke fatattakar ’yan bindiga a Zamfara An lakaɗa wa Mataimakin Firinsifal duka saboda hana satar a jarabawaBinciken farko ya nuna cewa mahaifin ya lura da motsi a wata bishiya da ke kusa da shi, sai ya harba bindiga yana zaton biri ne. Bayan ya yi harbin sai ya gano cewa ya harbi dansa da ke kan bishiyar har lahira.
Tuni dai ’yan sanda suka tsare mahaifin domin yi masa tambayoyi yayin da bincike ke ci gaba kan wannan lamari mai ban tausayi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Harbe ɗansa
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa gwamnatin Jihar Katsina na ƙoƙarin sasantawa da wasu ƙungiyoyin ‘yan bindiga a wasu yankunan jihar.
Wasu daga cikin ‘yan bindigar da ke Jibia, Batsari da DanMusa sun amince da zaman lafiya tare da miƙa makamansu.
Sai dai wannan hari na baya-bayan nan ya sa al’umma sun fara shakkar ko zaman lafiyar zai ɗore.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp