Faransa, Masar da Jordan sun yi kira da a tsagaita wuta cikin gaggawa a Gaza
Published: 8th, April 2025 GMT
Shugabannin kasashen Faransa da Masar da kuma Jordan sun fitar da wata sanarwa ta hadin gwiwa inda suka bukaci a tsagaita bude wuta cikin gaggawa a Gaza, tare da sukar Isra’ila kan gazawarta wajen tabbatar da ayyukan jin kai a zirin.
Kiran tsagaita wuta ya nuna bukatar samar da agajin jin kai cikin gaggawa a Gaza kuma ya nuna damuwar da kasashen duniya ke ci gaba da yi kan tashe-tashen hankula da rikicin jin kai a Gaza.
Haka kuma sanarwar wadannan kasashe uku ta nuna muhimmancin hanyar diflomasiyya na samun zaman lafiya da kwanciyar hankali.
A baya dai shugaba Macron ya nuna adawarsa da mamaye yankunan Falasdinawa da Isra’ila ta yi.
Macron ya kuma kira sabbin hare-haren da Isra’ila ta kai a yankin bayan rugujewar yarjejeniyar tsagaita bude wuta a tsakiyar watan Maris da cewa wani babban koma baya ne.
Sarki Abdallah na biyu na Jordan, shugaban Faransa Emmanuel Macron, da shugaban Masar Abdel Fattah el-Sisi na Masar sun bayyana cewa, “Dole ne a dakatar da yakin Gaza duba da bala’in da ya haifar a yanzu.
Tashin hankali, ta’addanci, da yaki ba za su iya samar da zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya ba.
Sanarwar ta yi nuni da bukatar gaggawa na kara kai kayan agaji a Gaza, inda tuni aka fara samun matsalar yunwa, da kare hukumomin Majalisar Dinkin Duniya da ma’aikatan jin kai da ke aiki a yankin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna
Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta taya sabon mai martaba Sarkin Katsinar Gusau, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello, murnar hawansa karagar mulki a matsayin Sarkin Katsinan Gusau na 16.
Jam’iyyar a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren yada labaranta, Yusuf Idris Gusau, ta bayyana sabon sarkin a matsayin mai tarihi da kuma nadin sarautar Allah, wanda ya zo ne jim kadan bayan rasuwar mahaifinsa, marigayi sarki, Alhaji Ibrahim Bello.
Sanarwar ta nuna cewa Alhaji Abdulkadir kyawawan halaye na gaskiya, kwazonsa, sadaukarwa, biyayya ga mahaifinsa da ya rasu, da kuma mutunta al’umma ta kowane hali, sun nuna shi ne wanda ya cancanta.
A cewar sanarwar, wannan shi ne karo na farko a tarihin masarautar da wani dan da ya haifa kai tsaye ya gaji mahaifinsa, wanda jam’iyyar ta ce hakan yana nuna yardar Allah da kuma ci gaba da gadon adalci na marigayi sarki.
Jam’iyyar APC ta bukaci sabon sarkin da ya kiyaye dabi’u da abubuwan gado na mahaifinsa da kakanni, musamman na fitaccen malamin addinin musulunci kuma shugaba, Sambo Dan-Ashafa.
Jam’iyyar ta yi addu’ar Allah ya yi masa jagora, ya kare shi, da kuma hikimar Sarki don ya jagoranci al’umma zuwa ga zaman lafiya da wadata.
Har ila yau, ta ba da tabbacin ci gaba da goyon bayanta da shirye-shiryenta na neman shawara, jagoranci, da albarka daga sabon sarki.
Daga karshe sanarwar da sakon fatan alheri ga mai martaba sarki da daukacin masarautar Gusau.
REL/AMINU DALHATU