Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa hanyar deblomasiyya ce kadai zata warware matsakar shirin nukliyar kasar iran da kasashen yamma.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a zantawa ta wayar tarho da jami’a mai kula da al-amuran harkokin waje na kungiyar tarayyar Turai Kaja Kallas.

Labarin ya kara da cewa ministan yana ganin matsalolin shirin Nucliya da kuma tsaron kasar ba za’a iya warwaresu ba sai ta wannan hanyar.

JMI ta dauki wannan hanya ce don ita ce kadai wacce zata kai da gamsuwar ko wani bangare a cikin al-amuran da suke sabani a cikinsu. Aragchi ya fadawa Kallas kan cewa da wannan dalilin ne JMI ta dauki hanyar tattaunawa ba kai tsaye ba don warware matsalra ta da Amurka.

Ya ce a shekarun da suka gabata JMI ta sha tattaunawa da kasashen turai Ingila, faransa da Jamus amma sai a zo inda suke tashi baram-baram, don kowa ya tsaya a kan matsayinsa.  Sannan ya kammala da cewa don kaucewa sabani dayan bangaren bai kamata ya gabatar da wani al-amari wand aba zai yu ba.

A nata bangaren Kallas ya bayyana cewa kungiyar kasashen Turai a shirye take ta shiga tattaunawa ta siyasa da JMI sannan a halin yanzu kungiyar tana neman lokacinda ya dace don yin hakan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hannayen jarin kamfanonin fina-finan Amurka sun fadi sakamakon barazanar Trump na kakaba harajin kwastam

Bayanai daga Amurka na cewa Hannayen jari na kafofin watsa labaru da kamfanonin shirya fina-finai da harkokin nishadi na Amurka sun fadi kasa, bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa, yana shirin kakaba harajin kwastam da kashi 100 bisa 100 a kan fina-finan da ake shiryawa a ketare.

Hannayen jarin kamfanonin fina-finai irin su Netflix Inc. da Warner Bros. Discovery Inc. sun fadi da kusan kashi 3 cikin dari, inda na Paramount Global da Walt Disney Co. kuma suka fadi da kusan kashi 2 cikin dari yayin da aka bude kasuwa.

A wani sakon da ya wallafa kan shafinsa na manhajar True Social, shugaban na Amurka ya ce yana umurtar ma’aikatar kasuwanci da wakilinsa na cinikayya da su “yi maza-maza su fara aikin kakaba” harajin a kan fina-finan kasashen waje, inda ya kara da cewa, “Muna son kara ganin fina-finan da ake yi a Amurka”.

Shugaban ya kuma sanya fina-finan kasashen waje a cikin jerin abubuwan dake kawo barazana ga tsaron kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Bukaci Kasashen Turai Su Shiga Tattaunawar Nukliya Da Take Yi Da Amurka
  • Hannayen jarin kamfanonin fina-finan Amurka sun fadi sakamakon barazanar Trump na kakaba harajin kwastam
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Batun Samun Hadin Kai Tsakanin Al’ummar Kasar
  • Sharhin bayan Labarai: Ci Gaban Harkokin Kasuwanci Tsakanin Iran Da Kasashen Waje Duk Tare Da Takunkuman Kasashen Yamma
  • Tarayyar Turai: Muna Goyon Bayan Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diplomasiyya
  • Iragchi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Babban Sakataren MDD Antonio Guterres
  • Shugaba Xi Zai Kai Ziyara Kasar Rasha
  • Iran : Araghchi zai ziyarci Pakistan da Indiya
  • Kungiyar Hizbullahi Ta Lebanon Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Suka Kai Kan Kasar Siriya