Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa hanyar deblomasiyya ce kadai zata warware matsakar shirin nukliyar kasar iran da kasashen yamma.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a zantawa ta wayar tarho da jami’a mai kula da al-amuran harkokin waje na kungiyar tarayyar Turai Kaja Kallas.

Labarin ya kara da cewa ministan yana ganin matsalolin shirin Nucliya da kuma tsaron kasar ba za’a iya warwaresu ba sai ta wannan hanyar.

JMI ta dauki wannan hanya ce don ita ce kadai wacce zata kai da gamsuwar ko wani bangare a cikin al-amuran da suke sabani a cikinsu. Aragchi ya fadawa Kallas kan cewa da wannan dalilin ne JMI ta dauki hanyar tattaunawa ba kai tsaye ba don warware matsalra ta da Amurka.

Ya ce a shekarun da suka gabata JMI ta sha tattaunawa da kasashen turai Ingila, faransa da Jamus amma sai a zo inda suke tashi baram-baram, don kowa ya tsaya a kan matsayinsa.  Sannan ya kammala da cewa don kaucewa sabani dayan bangaren bai kamata ya gabatar da wani al-amari wand aba zai yu ba.

A nata bangaren Kallas ya bayyana cewa kungiyar kasashen Turai a shirye take ta shiga tattaunawa ta siyasa da JMI sannan a halin yanzu kungiyar tana neman lokacinda ya dace don yin hakan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

MDD ta yi gargadi  game da mummunar matsalar da yunwa ka iya haifarwa ga al’ummar Gaza

Majalisar Dinkin Duniya ta fitar da wani kakkausar gargadi kan matsalar ruwan sha da ke kara kamari a zirin Gaza, inda ta bayyana cewa yunwa na ci gaba da rataya a kan al’ummar da ke kara hana samun tsaftataccen ruwan sha da tsaftar muhalli.

A cikin wani sabon rahoto, MDD ta ce kashi 96% na iyalai a Gaza na fuskantar matsalar rashin ruwa, yayin da kashi 90% na al’ummar kasar ba su da tsaftataccen ruwan sha. Ya kara da cewa kashi 75 cikin 100 na mazauna garin suna kokawa wajen shiga bandaki, lamarin da ke kara tabarbarewar bala’in jin kai a cikin ci gaba da kawanya da kuma ta’addancin Isra’ila na tsawon watanni

Tun da farko, ofishin kare hakkin bil adama na Majalisar Dinkin Duniya ya sanar da cewa Falasdinawa 1,373 ne suka yi shahada yayin da suke neman abinci tun lokacin da aka kaddamar da aikin agaji na Gaza a ranar 27 ga watan Mayu.

Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya António Guterres ya tabbatar da cewa Falasdinawa a Gaza na fuskantar wani mummunan bala’i na jin kai, sakamakon yakin yunwa da Isra’ila ta kakaba mata a yakin da take yi na kisan kare dangi a yankin.

Babban Kwamishinan UNRWA Philippe Lazzarini ya yi tsokaci kan karar da babban jami’in na Majalisar Dinkin Duniya ya yi, yana mai bayyana cewa, yanayin yunwa mafi muni ya riga ya faru a Gaza, kuma bala’in “da mutum ya yi.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Rasha da China sun fara wani gagarumin atisayen soji na hadin gwiwa a tekun Japan August 4, 2025 Araqchi Ya Bayyana Makomar Sinadarin Uranium Da Iran Ta Inganta A Lokacin Yaki August 3, 2025 Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci  Sun Bayyana Cewa: Masu Shirin Halaka Gaza Suna Son Mamaye Duniyar Musulmi Ne August 3, 2025 Iran Ta Jaddada Cewa: Karfin Makamai Masu Linzami Da Jiragen Sama Marasa Matuka Ciki Suna Nan Cikin  Shiri August 3, 2025 Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Tana Kokarin Boye Barnarta A Zirin Gaza August 3, 2025 Tsohon Shugaban Amurka Joe Biden Ya Caccaki Trump Kan Rusa Kundin Tsarin Mulkin Kasar August 3, 2025 IRGC Tace Bata Amince Da Kasashen Biyu A Kan Kasar Falasdinu Ba August 3, 2025 Iran Da Japan Suna Iya Jagorantar Duniya Don Rabata Da Makamai Kare Dangi August 3, 2025 Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa Ba za ta Ajiye Makamanta ba Sai Bayan samar Da Kasar falasdinu August 3, 2025 Kungiyar Hamas Ta Wallafa Hotunan bidiyo Na Fursinan HKI tsare A Gaza August 3, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Iran Ko Da Zata Sake Tattaunawa Da Amurka Zata Kasance Dauke Da Makamai Cikin Shirin
  • Iran Ta Ce Ba Wani Ma’aikacin Hukumar IAEA A Kasar A Halin Yanzu
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli
  • Gwamnan Kano Ya Kaddamar da Shirin Dashen Bishiyoyi
  • MDD ta yi gargadi  game da mummunar matsalar da yunwa ka iya haifarwa ga al’ummar Gaza
  • Sauyin Yanayi: Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da shirin dashen bishiya miliyan 5
  • IRGC Tace Bata Amince Da Kasashen Biyu A Kan Kasar Falasdinu Ba
  • Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa Ba za ta Ajiye Makamanta ba Sai Bayan samar Da Kasar falasdinu
  • Sojojin HKI, Daga Jiya Zuwa Yau lahadi Kadai Sun Kashe Falasdinawa 62
  • Kungiyar Wasan Taekwondo Ta Guragu Ta Iran Ta Zama Zakara A Asiya Karo Na 10 A Jere