Aragchi Ya Ce Hanyar Diblomasiyya Ce Kadai Hanar Warware Matsalar Shirin Nukliyar Iran
Published: 6th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa hanyar deblomasiyya ce kadai zata warware matsakar shirin nukliyar kasar iran da kasashen yamma.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a zantawa ta wayar tarho da jami’a mai kula da al-amuran harkokin waje na kungiyar tarayyar Turai Kaja Kallas.
Labarin ya kara da cewa ministan yana ganin matsalolin shirin Nucliya da kuma tsaron kasar ba za’a iya warwaresu ba sai ta wannan hanyar.
JMI ta dauki wannan hanya ce don ita ce kadai wacce zata kai da gamsuwar ko wani bangare a cikin al-amuran da suke sabani a cikinsu. Aragchi ya fadawa Kallas kan cewa da wannan dalilin ne JMI ta dauki hanyar tattaunawa ba kai tsaye ba don warware matsalra ta da Amurka.
Ya ce a shekarun da suka gabata JMI ta sha tattaunawa da kasashen turai Ingila, faransa da Jamus amma sai a zo inda suke tashi baram-baram, don kowa ya tsaya a kan matsayinsa. Sannan ya kammala da cewa don kaucewa sabani dayan bangaren bai kamata ya gabatar da wani al-amari wand aba zai yu ba.
A nata bangaren Kallas ya bayyana cewa kungiyar kasashen Turai a shirye take ta shiga tattaunawa ta siyasa da JMI sannan a halin yanzu kungiyar tana neman lokacinda ya dace don yin hakan.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro
Ya ce duk da cewa akwai damuwa kan yadda za a aiwatar da hakan, Gwamnatin Tarayya na da damar tsara ƙa’idoji da dokoki na musamman ga kowace jiha don hana amfani da ‘yansandan wajen cin zarafi.
A halin yanzu, gwamnonin jihohi daga faɗin Nijeriya na gudanar da wani taron gaggawa a Babban Birnin Tarayya, wanda ke gudana a sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF).
Taron ya samu halartar gwamnonin jihohi da mataimakansu daga dukkanin jihohi 36 na ƙasar.
Koda yake ba a bayyana cikakken ajandar taron ba, kasancewar mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, da Ministan Tsaro, Mohammed Badaru, na cikin mahalarta taron, ya nuna cewa batutuwan tsaro ne ke kan gaba a tattaunawar.
Taron na gaggawa na zuwa ne a daidai lokacin da tsaro ke taɓarɓarewa a sassa da dama na ƙasar, lamarin da ke ƙara haifar da kira daga al’umma da shugabanni domin ɗaukar matakin gaggawa da haɗin gwiwa tsakanin jihohi da Gwamnatin Tarayya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp