Aminiya:
2025-05-06@12:40:55 GMT

Hajj 2025: Maniyyatan Kaduna za su fara tashi ranar 14 ga watan Mayu

Published: 6th, May 2025 GMT

Hukumar Kula da Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna za ta fara jigilar maniyyata zuwa kasar Saudiyya a ranar 14 ga watan Mayu, 2025.

Shugaban hukumar, Malam Salihu S. Abubakar, ne ya bayyana hakan a wani shirin rediyo kai tsaye da aka watsa daga Kaduna, inda ya bayyana shirye-shiryen da jihar ta kammala domin aikin Hajjin bana.

Ya bayyana cewa maniyyata 4,060 daga jihar Kaduna za su sauke farali a bana, kuma kamfanin jirgin sama na UMZA ne zai yi jigilarsu.

Shugaban hukumar ya bayyana cewa domin kammala matakan da ake bi kafin tafiya, za a yi duk maniyya cikakken gwajin lafiya a sansanin alhazai da ke Mando.

Wata mata ta auri maza biyu a lokaci guda a Kano NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ‘Yan Gwagwarmaya Ke Shiga Tasku A Najeriya?

Ka’idodin lafiya na ƙasa da ƙasa da kuma na Saudiyya sun shardan cewa dukkan mata maniyyata za su yi gwajin daukar ciki kafin tafiya.

Malam Salihu ya bukaci maniyyata su kiyaye dokoki da ƙa’idojin da hukumomin Saudiyya suka gindaya, yana mai jaddada muhimmancin ladabi, haɗin kai da kuma kiyaye tsaron kai a lokacin aikin Hajji.

Ya tabbatar da cewa hukumar za ta ci gaba da sadaukar da kai don ganin maniyyata sun sami sauƙin tafiya tare da samun damar ibada cikin kwanciyar hankali da nutsuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: maniyyata Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

HKI Ta Tabbatar Da Halakar Sojojinta 2 A Yankin Rafa Na Zirin Gaza

Gwamnatin HKI ta bada sanarwan halakar sojojinta biyu da kuma jikatan wasu alokacinda suke bincike da kuma kokarin shiga wani rami na karkashin kasa a inda wani bom ya tashi ya kashe su ya kuma raunata wasu.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakafen yana labaran yahudawan na fadar haka a safiyar yau kuma wadanda aka rutsa da su sun hada da  Captain Noam Ravid, dan shekara 23 a duniya da kuma Staff Sergeant Yaly Seror, dan shekara 20 a duniya.

Labarin ya kara da cewa hatsarin ya faru ne a jiya asabar, sannan wasu sojoji biyu daga rundunar Yahalom sun ji rauni.

Tun ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 ne aka fara yakin tufanul Aksa, inda sojojin yahudawan tare da taimakon kasashen yamma suka fara kisan kiyashi ga Falasdinawa a yankin, wanda ya kaiga shahadar mutane 52,495 ya zuwa yanzu. Sannan wasu 118,366 suka ji rauni.

An dan tsaida yaki daga ranar 19 ga watan Jenerun wannan shekara har aka kai wata marhala sai HKI ta tsaida aiwatarda yarjeniyar. Sannan ta sake komawa yaki.

An kashe sojojin yahudawa fiye da 850 daga ciki har da sojojin kasa 414 a yankin na Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Daukar nauyin dalibai: Rikici ya barke a Hukumar Raya Arewa Maso Yamma
  • Aikin Hajjin 2025 Ya Fara A Hukumance Yayin Da Tawagar NAHCON Ta Musamman Ta Tashi Zuwa Makkah
  • Majalisar Kano Ta Amince Da Dokar Wutar Lantarki Da Za Ta Raba Wa Jihohi 3 Wuta
  • Ghana ta ci tarar ministoci saboda rashin bayyana kadarorin da suka mallaka
  • An Kama Wani Ɗan Ghana Bisa Zargin Kai Mata Hajji Ba Tare Da Lasisi Ba
  • HKI Ta Tabbatar Da Halakar Sojojinta 2 A Yankin Rafa Na Zirin Gaza
  • OPEC+ Zata Kara Yawan Man Fetur Da Take Haka Da Ganga 411,000 A Cikin Watan Yuli Mai Zuwa
  • Maniyyata Daga Turai Akan Dawakai Sun Isa Kasar Saudiyya Domin Yin Aikin Hajjin 2025
  • Hajjin Bana: Gwamnatin Jigawa ta aika wa NAHCON Naira biliyan 6