Hamas : Tattaunawar sulhu ba ta da wani tasiri a halin da ake ciki
Published: 6th, May 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta bayyana cewa tattaunawar sulhu a Gaza ba ta da wani tasiri a wannan mataki.
Ofishin kungiyar, ya yi kira ga kasashen duniya da su matsa lamba kan gwamnatin Netanyahu don kawo karshen laifukan yunwa, kishirwa da kisan kai a Gaza, in ji wani babban jami’in kungiyar.
Halin da ake ciki a Gaza ya kai intaha inji kungiyoyin kasa da kasa.
A wani rahoto data fitar a baya baya nan kungiyar agaji ta Red Crescent ta Falasdinu ta yi gargadi kan halin da ake ciki a zirin fiye da na watanni 19 da suka gabata.”
kungiyar ta jaddada cewa “mafi yawan jama’a na yankin na fuskantar matsananciyar hadarin yunwa.”
Sama da mutane miliyan daya da suka rasa matsugunansu a zirin Gaza ba su da damar samun ababen bukatuwa na yau da kullun.
Tun daga ranar 7 ga Oktoban 2023, lokacin da gwamnatin Isra’ila ta kaddamar da yakin kisan kare dangi a kan zirin Gaza, an kashe Falasdinawa sama da 52,535 tare da jikkata wasu fiye da 118,491 galibi mata da kananan yara.
A cikin watan Janairu, kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas da gwamnatin mamaya ta Isra’ila sun amince da shirin tsagaita wuta na matakai uku, wanda ya fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu, saidia daga bisani Isra’ila ta fi fatali da shi ta koma kai hare-haren ta a Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila Na ci Gaba Da Kutsa Kai A Tsakiyar Gaza A Yau Juma’a
Rahotanni sun bayyana cewa tankunan yakin HKI na ci gaba da kutsa kai a tsakiyar gaza a yau juma’a, lamarin da ya jawo tsananta kai hare-hare ta kasa da tilastawa dubban mutane barin muhallinsu sakamakon yankewar hanyoyin sadarwa,
A gefe daya kuma Amurka a karo na 6 ta hau kujerar naki kan kudurin kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya na bukatar dakatar da bude wuta da kuma sakin fursunoni da aka kama.
Yankin gaza yana dauke da mutane miliyan daya kafin yaki, sai dai rahutanni sun bayyana cewa ya zuwa yanzu sama da 350,000 ne suka bace.
Hare hare Isra’ila tun daga 7 ga watan oktoban shekara ta 2023 ta kashe falasdinawa 65141 kuma ta jikkkata 165925 kamar yadda majiyar lafiya ta gaza ta sanar.
Kimanin mutane 1000 ne suka tsere zuwa kasashen makwabta ta kasa wasu akn jakuna wasu akan ababen hawa domin tsira da rayukansu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Dangantaka Na Kara Tsami Tsakani Faransa Da Isra’ila Kan Amincewa Da Falasdinu . September 19, 2025 Sojojin HKI 12 Ne Suka Halaka Ko Suka Ji Rauni A Gaza September 19, 2025 Amurka Ta Yi Amfani Da Kujeran Veto Don Hana Zaman Lafiya A Gaza September 19, 2025 HKI Ta Kai Hare-Hare Kan Wurare Har 5 A Kudancin Kasar Lebanon September 19, 2025 Majiyoyin Diblomasiyya Sun Ce Washington Zata Jagoranci Turawa A Tattaunawa Da Iran September 19, 2025 Iran Ta Bukaci Kwamitin Tsaro Na MDD Ta Zabi Diblomasiyya Kan Fito Na Fito September 19, 2025 Yahudawa Suna Ci Gaba Da Yin Hijira Zuwa Wajen HKI September 18, 2025 ‘Yan Gwgawarmaya Sun Kashe Sojojin HKi 4 A Gaza September 18, 2025 An Halaka Sojojin HKI Biyu Ta Hanyar Sukarsu Da Wuka A Kusa Da Iyakar Jordan September 18, 2025 Husi: Kai Wa Kasar Katar Hari Gargadi Ne Ga Al’ummar Musulmi September 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci