HausaTv:
2025-05-06@14:19:21 GMT

Hamas : Tattaunawar sulhu ba ta da wani tasiri a halin da ake ciki

Published: 6th, May 2025 GMT

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta bayyana cewa tattaunawar sulhu a Gaza ba ta da wani tasiri a wannan mataki.

Ofishin kungiyar, ya yi kira ga kasashen duniya da su matsa lamba kan gwamnatin Netanyahu don kawo karshen laifukan yunwa, kishirwa da kisan kai a Gaza, in ji wani babban jami’in kungiyar.

Halin da ake ciki a Gaza ya kai intaha inji kungiyoyin kasa da kasa.  

A wani rahoto data fitar a baya baya nan kungiyar agaji ta Red Crescent ta Falasdinu ta yi gargadi kan halin da ake ciki a zirin fiye da na watanni 19 da suka gabata.”

kungiyar ta jaddada cewa “mafi yawan jama’a na yankin na fuskantar matsananciyar hadarin yunwa.”

Sama da mutane miliyan daya da suka rasa matsugunansu a zirin Gaza ba su da damar samun ababen bukatuwa na yau da kullun.

Tun daga ranar 7 ga Oktoban 2023, lokacin da gwamnatin Isra’ila ta kaddamar da yakin kisan kare dangi a kan zirin Gaza, an kashe Falasdinawa sama da 52,535 tare da jikkata wasu fiye da 118,491 galibi mata da kananan yara.

A cikin watan Janairu, kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas da gwamnatin mamaya ta Isra’ila sun amince da shirin tsagaita wuta na matakai uku, wanda ya fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu, saidia daga bisani Isra’ila ta fi fatali da shi ta koma kai hare-haren ta a Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sharhin Bayan Labarai: Ranar Malami A Kasar Iran

Assalamu alaikum masu sauraro, sharhin bayan labarammu zai yi magana ne a kan Aya. Shahid Mttahari, shahidi na farko daga cikin malamai jagororin juyin juya halin musulunci a nan kasar Iran a shekara 1979.

A jiya Jumma ce 2 ga watan Mayu na wannan shekara ta 2025 aka yi juyayin shahadar malami na fadrko wanda ya kai ga shahada bayan nasaral juyin juya halin musulunci a nan iran.

Aya. Murtadha Muttahari, malami marubuci sannan jagora mai farkar da mutane a Iran da sauran kasashen duniya ta hanyar alkalaminsa da kuma jawabansa na shekaru masu yawa.

Kafin juyin juya halin musulunci a nan Iran shekaru 46 da suka gabata, Aya, Muttahari ya zama fitilla ga mutane da dama a nan kasar Iran, musamman daliban Jami’I’oo a nan Iran kuma musamman daliban Jami’ar Tehran wadanda ya dauki shekari kimani 23 yana karantar da ilmin addinai da kuma falsafa.

Shaida Muttahari ya rubuta littafai a fannoniun ilmi da dama , kama daga Fikihu, akidu, falsafatarihi da sauransu kuma ya karantar da su. Banda haka shi jagora ne na fada da azzaluman shugabannni a karni na 20 da ya gabata.

Sanaiyyar wadannan al-amura da Shahid Muttahari aka sanya ranar 2 ga watan Mayu na ko wace shekara tun bayan shahadarsa a matsayin ranar Malami.

Aya. Mutahhari ya barman littafan da ya rubuta fiye da 100 kuma an tarjama wasunsu zuwa harsuna da dama a duniya. Wadannan littafan sun zama fitila wadanda suka farkar da mutanen da dama a ko ina a duniya.

Wani mai tarjamar Littafai a kasar Malasiya Seyyed Sheikh ibn Seyyed Mostafa, ya ce shi kadai ya tarjama littafan Shahid Mutahhari har guda 70, amma har yanzin ana bukatar littafan sa, a kasuwan. A bangaren ikida wasu malaman addini sun bayyana cewa ba wanda masana a kasahen yamma suka fahinci falsafan addinin musulunci kamar yadda suka fahinta a littgafan shaida muttahari.

Wata kungiyar batacciya a lokacin a nan Iran wacce ake kira Furkan ne ta sa daya daga cikin mabiyanta ya zo ya bindige shahid Muttahiri a kusa da gidansa a nan Tehran kwanaki 80 kacal da samun nasarar juyin juya halin musulunci a nan kasar Iran a shekara 1979. Da wani dalili wannan kungiyar ta kasheshi, Al..ya sani. Da fatan All..ya hasakak kabarinsa ya sa mu kara fahintar ilmin da ya bara mana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Janyo Shahadan Falasdinawa 50 A Yankin Zirin Gaza
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Ce Masifar Yunwa Ta Kara Yin Kamari A Yankin Zirin Gaza Na Falasdinu
  • Sharhin Bayan Labarai: Ranar Malami A Kasar Iran
  • HKI Ta Tabbatar Da Halakar Sojojinta 2 A Yankin Rafa Na Zirin Gaza
  • Kissoshin Rayuwa : Imam Al-Hassan (a) 113
  • Iran ta yi Allah-wadai da harin da Isra’ila ta kai kan jirgin ruwan da ke jigilar abinci zuwa Gaza
  • Wani harin makami mai linzami daga Yemen ya fada filin jirgin saman Ben Gurion na Isra’ila
  • Ghana Za Ta Hada Gwiwa Da Gwamnatin Jihar Kebbi Kan Noma
  • Kungiyar Hizbullahi Ta Lebanon Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Suka Kai Kan Kasar Siriya