Sojojin Kasar Yamen Sun Maida Martani Ga Hare-Haren Amurka Kan Amurkan Da Kuma HKI
Published: 9th, April 2025 GMT
Sojojin kasar Yamen sun bada sanarwan maida martani ga hare-haren jiragen yakin kasar Amurka a kan kasar na baya-bayan nan, kuma zasu ci gaba da kai hare-haren kan wadannan wurare har zuwa lokacinda za’a kawo karshen yaki a Gaza.
Tashar talabijin ta presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin sojojin kasar Yemen Burgediya Janar Yahyah Saree yana fadar haka a yau Laraba .
Kafin haka dai jiragen Amurka wadanda suke tasowa daga jiragin yaki USS Harry Truman sun kai hare-hare kan wurare daban daban a kan kasar ta Yemen.
Tun cikin watan Octoban shekara ta 2023 ne sojojin kasar Yemen suka shiga yaki da kuma HKI da kasashen da suke tallafa mata, saboda tallafa wa falasdinawa a Gaza wadanda sojojin HKI take masu kissan gilla tun lokacin.
Gwamnatin kasar Amurka ta bada sanarwan kafa kawance ta tabbar da amincin jiragen kasuwanci na HKI a cikin tekun Red sea amma ta kasa samar da aminci ga jiragen HKI a ko masu zuwa wajenta a tekun har yanzu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Bayan an mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, kasashen duniya sun soma zura ido kan kasar Sin. Ana sa ran cewa, taron APEC da za a gudanar a Shenzhen, zai kara habaka hadin gwiwa, da samun ci gaba, da wadata tare a shiyyar, kana zai shaida yadda kasar Sin ke kara samar da sabbin damammaki ga yankin Asiya da Pasifik, bisa ga sabbin nasarorin da take samu ta hanyar zamanantarwa irin ta kasar Sin. (Mai fassara Bilkisu Xin)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA