Jiragen Yaken HKI Sun Kai Hare-Hare A Kan Tashar Jiragen Sama Na Birnin San’aa Na Kasar Yemen
Published: 6th, May 2025 GMT
A safiyar yau ne jiragen yakin HKI suka kai hare-hare kan tashar Jiragen sama na birnin San’a na kasar Yemen inda ake ganin hakan kara ruruta wutan yaki a yankin ne.
Klamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa a dai-dai lokacinda jiragen yakin Amurka suka dauki kimani watannin biyu suka kai hare hare kan kasar Yemen a yau jiragen yakin HKI sun kai wasu sabbin harehare a kan birnin san’a baban birnin kasar.
A cikin makon nan ne kungiyar Ansarulla.. ta kai hare hare da makamai masu linzami a kan tashar jiragen sama na bengerio tashar jiragen sama mafi girma, a kasar wanda ta dakatar da tashin jiragen sama na kwanaki sannan wasu dan kadan suka fara tashi tsakanin jiya da yau.
Kubgiyar Huthi ta ce zata maida martani mafi tsanani a kan HKI don tallafawa mutane gaza wadanda hki take gashewa da ta sama da makamaita kasa kuma da yunwa.
Kafafen yada labarai na HKI sun bayyana cewa jiragen yakin kasar sun kai hare hare har 15 a kan tashae jirasgen sama na san’aa kuma sun lalata ta gaba daya. Kungiyar an sarullah dai tace zata maida martani mai karfi a na gaba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: jiragen sama na kai hare hare jiragen yakin
এছাড়াও পড়ুন:
DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Hare haren ‘yan ta’adda na kara ta’azzara a yankuna daban daban na fadin kasar nan wanda hakan ke nuni da Karin rashin tsaro da ya dade yana ciwa alumma da ma gwamnati tuwo a kwarya.
Ko a kwana kwanan nan an ga yadda jihar filato tayi ta fama da irin wadannan hare hare da kuma hare haren ramuwar gayya.
Wani kididdiga kungiyar dake tattara bayanan hare haren ta’addanci ta fitar ya nuna cewa Najeriya ta taso daga mataki na 8 zuwa na 6 a batun ta’addanci a duniya.
Kazalika a kwanakin nan wani hari da aka kai a wasu yankunan jihar Binuwe yayi sanadiyyar halakar mutane da dama, wadda hakan ya jawo cece ku ce da ya kai har wasu na kiran mutane su tashi don kare kan su.
Irin wannan kira dai an dade ana yi, sai dai gwamnati na ganin ba daidai ne mutane su kare kan su daga hare haren ‘yan ta’adda ba.
NAJERIYA A YAU: Yadda Cin Ganyayyaki Ke Yi Wa ‘Yan Najeriya Wahala DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon LafiyaShirin Daga Laraba na wannan mako zai yi nazari ne kan shin ko kare kai daga hare haren ‘yan ta’adda zai kawo karshen matsalar tsaro da ake fuskanta a Najeriya?
Domin sauke shirin, latsa nan