Jiragen Yaken HKI Sun Kai Hare-Hare A Kan Tashar Jiragen Sama Na Birnin San’aa Na Kasar Yemen
Published: 6th, May 2025 GMT
A safiyar yau ne jiragen yakin HKI suka kai hare-hare kan tashar Jiragen sama na birnin San’a na kasar Yemen inda ake ganin hakan kara ruruta wutan yaki a yankin ne.
Klamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa a dai-dai lokacinda jiragen yakin Amurka suka dauki kimani watannin biyu suka kai hare hare kan kasar Yemen a yau jiragen yakin HKI sun kai wasu sabbin harehare a kan birnin san’a baban birnin kasar.
A cikin makon nan ne kungiyar Ansarulla.. ta kai hare hare da makamai masu linzami a kan tashar jiragen sama na bengerio tashar jiragen sama mafi girma, a kasar wanda ta dakatar da tashin jiragen sama na kwanaki sannan wasu dan kadan suka fara tashi tsakanin jiya da yau.
Kubgiyar Huthi ta ce zata maida martani mafi tsanani a kan HKI don tallafawa mutane gaza wadanda hki take gashewa da ta sama da makamaita kasa kuma da yunwa.
Kafafen yada labarai na HKI sun bayyana cewa jiragen yakin kasar sun kai hare hare har 15 a kan tashae jirasgen sama na san’aa kuma sun lalata ta gaba daya. Kungiyar an sarullah dai tace zata maida martani mai karfi a na gaba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: jiragen sama na kai hare hare jiragen yakin
এছাড়াও পড়ুন:
Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Yin Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Sahayoniyya Kan Kasar Yemen
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta yi Allah wadai da zaluncin ‘yan sahayoniyya a kan kasar Yemen
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi kakkausar suka kan harin wuce gona da iri da sojojin yahudawan sahayoniyya suka kai tashar jiragen ruwa na Hodeidah da sauran ababen more rayuwa na kasar Yemen, yana mai bayyana hakan a matsayin babban laifi da kuma keta ka’idoji da dokokin kasa da kasa.
A cikin bayaninsa da sanyin safiyar yau Talata, Baqa’i ya yi nuni da cewa: Hare-haren da ‘yan sahayoniyya suka kai kan tashar jiragen ruwa, da masana’antu, da kuma wuraren zama a kasar Yemen, ana aiwatar da su ne tare da goyon baya da kuma taimakon Amurka. Ya bayyana wadannan hare-haren a matsayin cin zarafi ga doka da kuma keta ka’idoji Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya dangane da mutunta ‘yancin kai na kasa da kuma iyakokin kasa. Ya kuma yi kira da a hada kai da daukar kwararan matakai na kasa da kasa da kasashen yankin don dakile kashe-kashe da barna da Amurka da yahudawan sahayoniyya suke yi a kasashen musulmi.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya jaddada cewa: Hanya daya tilo ta hana yaduwar rashin tsaro a yankin ita ce dakatar da kisan kiyashi da laifuffukan da yahudawan sahayoniyya suke yi a Gaza da kuma kawo karshen rashin hukunta masu aikata muggan laifukan a yankin.