Lamarin ya tayar da hankali a unguwar, inda wasu matasa suka yi yunƙurin kai farmakar Saudat.

Amma jami’an tsaro sun isa wajen a kan lokaci, suka ceci amaryar tare da kai ta wajen hukuma.

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare.

Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Amarya Zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli

Gwamnatin Jihar Kano ta sake tabbatar da kudurinta na yaki da zaizayar ƙasa, ambaliyar ruwa, da sauran matsalolin da suka shafi muhalli.

Wannan bayani ya fito ne daga Gwamna Abba Kabir Yusuf yayin kaddamar da babban shirin dashen itatuwa da za a shuka tsirrai miliyan biyar da rabi a faɗin jihar, wanda aka gudanar a ƙaramar hukumar Makoda.

Ya bayyana cewa babban burin wannan shiri shi ne magance dimbin matsalolin muhalli da ke addabar al’ummar Kano.

Gwamna Yusuf ya jaddada cewa waɗannan matsaloli sun jawo manyan kalubale ga al’umma.

Ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta samar da dukkan kayayyakin da suka wajaba don kula da tsirran da za a dasa, domin su girma yadda ya kamata tare da cika manufarsu. Wannan goyon baya na da matuƙar muhimmanci wajen nasarar shirin.

Ya bukaci dukkan shugabannin ƙananan hukumomi 44, sarakuna da jami’an raya al’umma da su shiga cikin wannan shiri, yana mai cewa halartar su na da matuƙar amfani wajen cimma burin da aka sa gaba.

“Idan aka kula da itatuwan da kyau, za su taka muhimmiyar rawa wajen rage sauyin yanayi da sauran matsalolin da suka shafi muhalli. Wannan na cikin manyan manufofin muhalli na Jihar Kano.” In ji shi.

Kwamishinan Muhalli, Dr. Dahiru Mohammad Hashim, ya yabawa Gwamna Yusuf bisa goyon bayan da yake bai wa ma’aikatar don yaki da matsalolin muhalli.

Wakilin Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Muhammad Sanusi II, wato Sarkin Dawakin Mai Tuta Alhaji Mohammad Bello Abubakar, ya sake jaddada goyon bayan masarautar ga wannan shirin na dashen itatuwa.

A yayin taron, an gabatar da kyaututtuka ga wasu mutane da suka taka rawar gani wajen tallafawa al’ummominsu.

Wannan karramawa na matsayin kwarin gwiwa ne ga wasu domin su shiga irin waɗannan ayyuka na kula da muhalli.

 

Abdullahi Jalaluddeen

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
  • Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
  • Kwamitin Binciken Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
  • Kwamitin Binciken Ya Kammala Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli
  • Son Zai Bar Tottenham Zuwa Amurka Bayan Shafe Shekaru 10 A Ingila
  • Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
  • Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
  • An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo