An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Published: 6th, May 2025 GMT
Lamarin ya tayar da hankali a unguwar, inda wasu matasa suka yi yunƙurin kai farmakar Saudat.
Amma jami’an tsaro sun isa wajen a kan lokaci, suka ceci amaryar tare da kai ta wajen hukuma.
Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.
Daga kanmu, magana ta ƙare.
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli
Gwamnatin Jihar Kano ta sake tabbatar da kudurinta na yaki da zaizayar ƙasa, ambaliyar ruwa, da sauran matsalolin da suka shafi muhalli.
Wannan bayani ya fito ne daga Gwamna Abba Kabir Yusuf yayin kaddamar da babban shirin dashen itatuwa da za a shuka tsirrai miliyan biyar da rabi a faɗin jihar, wanda aka gudanar a ƙaramar hukumar Makoda.
Ya bayyana cewa babban burin wannan shiri shi ne magance dimbin matsalolin muhalli da ke addabar al’ummar Kano.
Gwamna Yusuf ya jaddada cewa waɗannan matsaloli sun jawo manyan kalubale ga al’umma.
Ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta samar da dukkan kayayyakin da suka wajaba don kula da tsirran da za a dasa, domin su girma yadda ya kamata tare da cika manufarsu. Wannan goyon baya na da matuƙar muhimmanci wajen nasarar shirin.
Ya bukaci dukkan shugabannin ƙananan hukumomi 44, sarakuna da jami’an raya al’umma da su shiga cikin wannan shiri, yana mai cewa halartar su na da matuƙar amfani wajen cimma burin da aka sa gaba.
“Idan aka kula da itatuwan da kyau, za su taka muhimmiyar rawa wajen rage sauyin yanayi da sauran matsalolin da suka shafi muhalli. Wannan na cikin manyan manufofin muhalli na Jihar Kano.” In ji shi.
Kwamishinan Muhalli, Dr. Dahiru Mohammad Hashim, ya yabawa Gwamna Yusuf bisa goyon bayan da yake bai wa ma’aikatar don yaki da matsalolin muhalli.
Wakilin Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Muhammad Sanusi II, wato Sarkin Dawakin Mai Tuta Alhaji Mohammad Bello Abubakar, ya sake jaddada goyon bayan masarautar ga wannan shirin na dashen itatuwa.
A yayin taron, an gabatar da kyaututtuka ga wasu mutane da suka taka rawar gani wajen tallafawa al’ummominsu.
Wannan karramawa na matsayin kwarin gwiwa ne ga wasu domin su shiga irin waɗannan ayyuka na kula da muhalli.
Abdullahi Jalaluddeen