Tashar talbijin din “News Fox” ta kasar Amurka  mai ra’ayin ‘yan mazan jiya ta watsa wani rahoto da yake cewa; Daga lokacin da Donald Trump ya zama shugaban kasa, sau 6 sojojin Yemen su ka kakkabo jiragen sama maras matuki samfurin Mq9.

Rahoton na tashar talabijin din Fox ya kuma yi ishara da yadda sojojin na Yemen su ka kakkabo jirgin sama marasa matuki da marecen juma’a, wanda shi ne karo na 6 tun daga ranar 3 ga watan Maris.

Rahoton ya kuma kara da cewa; Kowane daya daga cikin jiragen sama marasa matuki  samfurin mq9 ya kai dalar Amurka miliyan 30.

 Bugu da kari rahoton ya kuma bayyana cewa; Sau 35 sojojin Amurka suna kai wa kasar Yemen hare-hare, amma kuma duk da haka har yanzu  sojojin Yemen suna ci gaba da kai wa wadannan jiragen na Amurka masu tsada hari. Haka nan kuma sojojin na Yemen suna ci gaba da hana wucewar jiragen  ruwa da suke zuwa HKI.

Wannan rahoton kuma ya yi ishara da yadda sojojin na Yemen suke kai wa HKI hare-hare da makamai masu linzami masu cin dogon zango. 

Daga fara kai farmakin Aksa zuwa yanzu, adadin jiragen Amurka samfurin  MQ 9 da sojojin yemen su ka kakkabo sun kai 16, sai dai wata majiyar ta bayyana cewa, jiragen da sojojin na Yemen su ka kakkabo sun kai 20. Wani jami’in ma’aikatar tsaro ta kasar Amurka ya sanar da tashar talbijin din ta Fox cewa; A 2024 Amurka ta kera, jragen MQ 9 guda 230, amma a kasar Yemen kadai an harbo 16 daga cikinsu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026

Gwamnatin tarayya ta umarci hukumar shirya jarrabawar WAEC da NECO da su fara amfani da cikakken tsarin amfani da Komfuta (CBT) ga dukkan jarabawar su nan da shekarar 2026. Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ne ya bayar da wannan umarnin a ranar Litinin yayin ziyara da kuma duba yadda ake gudanar da gwaje-gwaje na CBT a cibiyoyin Bwari da kuma duba ɗakin gwajin jarrabawa JAMB a kwamfuta.

Alausa ya bayyana cewa, daga watan Mayu ko Yuni na 2026, duka ɓangarorin tambayoyin da aka saba na WAEC da NECO, na rubutu da na gwaje-gwaje, za su kasance a komfuta gaba ɗaya. Ya ƙara da cewa wannan matakin na daga cikin manufar gwamnatin na magance matsalar satar jarabawa.

Gwamnatin Kano Ta Biyawa Ɗalibai 119,903 Kudin Jarrabawar NECO Da NBAIS WAEC Ta Kwace Lasisin Makarantu 574 Sakamakon Satar Amsa

Ministan ya kuma sanar da cewa an kafa kwamitin bincike ƙarƙashin jagorancin Daraktan JAMB, Prof. Ishaq Oloyede, wanda zai duba tsarin jarabawar Nijeriya gaba ɗaya, inda aka ce sakamakon binciken zai fito nan da ƙarshen watan gobe. Alausa ya yaba da ingancin gudanar da jarabawar UTME ta 2025 da JAMB, wanda ya bayyana a matsayin “matsayi na duniya” kuma yana cika ƙa’idojin ƙasa da ƙasa.

A cikin jawabinsa, Oloyede ya bayyana cewa UTME ta 2025 tana ɗaya daga cikin mafi kyawun jarabawar da aka taɓa gudanarwa, inda ya kuma bayyana cewa duk wani zargin rashin dacewar cibiyoyin jarabawa yana buƙatar hujja mai ƙarfi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka
  • Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut