Mummunan Hatsari Ya Kashe Mutane 23, Da Yawa Sun Jikkata A Kano
Published: 15th, February 2025 GMT
Hukumar kiyaye haɗɗura ta ƙasa (FRSC) reshen jihar Kano ta tabbatar da cewa mutane 23 ne suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin da ya afku a gadar sama ta Muhammadu Buhari da ke kan hanyar Kano zuwa Maiduguri a ranar Juma’a nan da ta gabata.
A cewar hukumar FRSC, hatsarin ya rutsa da wata tirela ce wacce take ɗauke da kayayyaki da fasinjoji.                
      
				
Binciken farko ya nuna cewa hatsarin ya faru ne sakamakon tukin ganganci wanda aka fi alakƙanta shi da faruwar lamarin. Hatsarin ya rutsa da a ƙalla mutane 71, inda 48 suka samu raunuka, yayin da 23 suka mutu.
Jami’an bayar da agajin gaggawa na FRSC tare da haɗin gwuiwa da rundunar ‘yansandan Nijeriya sun isa wurin da lamarin ya faru cikin gaggawa domin ceto waɗanda lamarin ya rutsa da su.
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano
Sojojin haɗin gwuiwa ta Operation MESA ƙarƙashin Birgediya ta 3 sun kashe ƴan bindiga 19 a ƙaramar hukumar Shanono ta jihar Kano, bayan wata musayar wuta mai tsanani da ta faru a yankunan Unguwan Tudu, Unguwan Tsamiya, da Goron Dutse da misalin ƙarfe 5:00 na yamma ranar Asabar. Wannan sumame ya biyo bayan sahihan bayanan leƙen asiri kan motsin wasu ƴan ta’adda da suka shiga yankin daga maƙwabtan dazuka.
A cewar sanarwar Kyaftin Babatunde Zubairu, Mataimakin Daraktan hulɗa da Jama’a na Birgediya ta 3, Sojojin tare da jami’an tsaro sun fatattaki ƴan ta’addan bayan musayar wuta, inda aka kashe ƴan bindiga 19, yayin da wasu suka gudu da raunin harbi. Ya ce an ƙwato babura da dama da kuma wayoyi guda biyu da aka samu a wajensu.
Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da MakamashiSai dai, Sojoji biyu da jami’in sa-kai ɗaya sun rasa rayukansu yayin arta. Kyaftin Zubairu ya bayyana cewa sadaukarwar su hujja ce ta kishin ƙasa da jajircewar rundunar wajen kare ƴan Nijeriya da kawar da barazanar ta’addanci a yankin.
Kwamandan Brigade ta 3, Brigediya Janar Ahmed Tukur, ya yaba wa dakarun bisa jarumtarsu, yana mai tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da gudanar da aikace-aikacen tsabtace yankin domin hana ramuwar gayya da kare al’ummomin da ake yawan kai wa hare-hare. Ya kuma shawarci mazauna yankin da su ci gaba da lura da duk wani motsi na baƙuwar fuska da ba a saba gani ba tare da sanar da jami’an tsaro cikin lokaci.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA