Mummunan Hatsari Ya Kashe Mutane 23, Da Yawa Sun Jikkata A Kano
Published: 15th, February 2025 GMT
Hukumar kiyaye haɗɗura ta ƙasa (FRSC) reshen jihar Kano ta tabbatar da cewa mutane 23 ne suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin da ya afku a gadar sama ta Muhammadu Buhari da ke kan hanyar Kano zuwa Maiduguri a ranar Juma’a nan da ta gabata.
A cewar hukumar FRSC, hatsarin ya rutsa da wata tirela ce wacce take ɗauke da kayayyaki da fasinjoji.
Binciken farko ya nuna cewa hatsarin ya faru ne sakamakon tukin ganganci wanda aka fi alakƙanta shi da faruwar lamarin. Hatsarin ya rutsa da a ƙalla mutane 71, inda 48 suka samu raunuka, yayin da 23 suka mutu.
Jami’an bayar da agajin gaggawa na FRSC tare da haɗin gwuiwa da rundunar ‘yansandan Nijeriya sun isa wurin da lamarin ya faru cikin gaggawa domin ceto waɗanda lamarin ya rutsa da su.
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Sanda Sun Kama Wani Kasurgumin Barowon Shanu Da Garkuwa Da Mutane A Kasuwar Shinge
Jami’an Sashen Binciken Laifuka na Rundunar ‘Yan Sanda a Jihar Nasarawa (SCID) sun kama wani mai garkuwa da mutane a Kasuwar Shinge da ke Lafia, bisa rahotonnin sirri da suka samu.
An samu nasarar cafke wanda ake zargin bayan shafe dogon lokaci rundunar na nemasa ruwa a jallo saboda laifuka da dama da suka hada da garkuwa da mutane da kuma satar shanu.
A yayin bincike, wanda ake zargin ya amsa laifinsa, sannan ya jagoranci jami’an tsaro zuwa maboyarsa da ke kauyen Ruwan Baka a karamar hukumar Doma, inda aka samu bindiga kirar AK-49 mai lamba 453144 tare da alburusai.
Wannan nasarar ta biyo bayan kama wata Fatima Salisu a ‘yan kwanakin baya, wadda aka tare tana jigilar makamai daga Doma zuwa Jihar Katsina domin kaiwa miyagu.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Nasarawa, CP Shattima Jauro Mohammed, ya jaddada kudirin rundunar na ci gaba da yaki da aikata laifuka tare da tabbatar da tsaro ga dukkan mazauna jihar Nasarawa.
Ya bukaci jama’a da su kasance masu lura, tare da bayar da rahoton duk wani motsi ko aikin da ba su yarda da shi ba, domin ‘yan sanda za su ci gaba da aiki tukuru don tabbatar da zaman lafiyar al’umma.
Aliyu Muraki