‘Raini ne ya sa ake ƙalubalantar yunƙurin kafa ƙungiyar Hausawa zalla’
Published: 7th, May 2025 GMT
Wata ƙungiya mai rajin kare muradun al’ummar Hausawa a Nijeriya mai suna Kungiyar Hausawan Nijeriya ta tsaya kai da fata cewa dole a ƙyale Hausawa su kafa ƙungiyarsu kamar kowacce ƙabila tun da dai doka ba ta hana su ba.
Martanin nasu na zuwa ne a daidai lokacin da masu kiran ke shan sukar cewa suna ƙoƙarin rura wutar ƙabilanci ne a Arewacin Nijeriya Najeriya, musamman a daidai lokacin da yankin ke buƙatar haɗin kai domin magance matsalolinsa.
To sai dai ƙungiyar ta ce ba ta ga dalilin da zai sa a ƙalubalanci yunƙurin nasu ba, tun da dai ’yan ƙabilar Yarabawa suna da ƙungiyar Afenifere, ’yan kabilar Ibo suna da Ohaneze, Fulani kuma suna da Miyetti-Allah.
Sun ce hakan na nufin Hausawa ne kawai a cikin manyan ƙabilun ƙasar ba su da ƙungiyarsu ta ƙashin kansu.
A yayin wata zantawarsu da manema labarai a Kano, shugaban kungiyar, Abdullahi Abdullahi, ya ce yunƙurin ya zama wajibi domin kare muradun Hausawa a ƙasar ta kowacce fuska, musamman ta ɓangaren tsaro da ya ce ’yan bindiga na neman hana Hausawa rayuwa a yankunansu.
A cewarsa, “Akwai yunkurin da ake yin a kore samuwar asalin Hausawa ta hanyar cewa a yanzu babu cikakkun Hausawa na asali, a daidai lokacin da ake kiran wasu da cikakkun ’yan kabilar Ibo, Yarabawa da Fulani.
“Ayyukan ta’addancin da ake yi wa Hausawa a kasarsu abin takaici ne.
“Ina wadanda suka kashe Sarkin Gobir? Ina mutanen da Bello Turji ya ƙone ƙurmus a motar bas a Sakkwato ranar da Buhari ya tafi Legas ƙaddamar da littafi?
“Ina matan da ’yan ta’adda suka yi wa fyade a masallaci? Ina labarin jariran da ’yan ta’adda suka ba wa karnuka suka cinye da ransu? Ina labarin mafarautan da aka kashe a jihar Edo a kwanan nan? Waye zai nema musu hakki kuma waye zai bi musu kadi?
“Dole wadannan abubuwan suka sa dole mu Hausawa mu tashi tsaye mu tunkare su tare da masu goya musu baya daga cikin malaman addini, ’yan siyasa, masu rike da sarautun gargajiya da dukkan kungiyoyinsu,” in ji shugaban kungiyar.
Kungiyar ta kuma ce sam ba ta goyon bayan kiran da wasu ke yi na a yi wa rikakken dan ta’addan nan, Bello Turji afuwa, inda suka ce hakan babban kuskure ne da za a yi da-na-sani a kai.
Daga nan sai ƙungiyar ta yi Allah-wadai da abin da ta kira rashin sanin ciwon kai, kan yadda ta ce an kafa wani babban allon talla mai dauke da rubutun “Katsina babu korafi” ɗauke da hoton Shugaban Kasa Bola Tinubu yayin ziyarar da ya kai Jihar Katsina a ’yan kwanakin nan, a maimakon a fada masa matsalar da ake ciki ta rashin tsaro.
Sai dai kuma ƙungiyar ta ce idan zaɓe na gaba ya zo, babu wanda Hausawa za su sake zaɓa sai ɗan uwansu Bahaushe.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hausawa Ƙungiyar Hausawa Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Dadiyata: Buhari ya gaza nemo shi, Tinubu yana da lokaci — Amnesty
Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan Adam ta Amnesty International, ta ce Gwamnatin Tarayya ta yi sakaci game da ɓacewar ɗan gwagwarmaya Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata.
A wata sanarwa da ta fitar, Amnesty, ta ce abin takaici ne ganin cewa shekara shida kenan da Dadiyata ya ɓace ba tare da wani sahihin bayani ba.
Mutum ɗaya ya rasu, an jikkata wasu yayin arangama da ’yan sanda a Abuja Rufe gidan rediyo ya haifar da cece-ku-ce a NejaDadiyata ya ɓace ne a ranar 2 ga watan Agustan 2019, bayan wasu mutane ɗauke da makamai sun shiga gidansa da ke unguwar Barnawa a Jihar Kaduna, suka tafi da shi.
Tun daga wannan lokacin, iyalansa da abokansa ke jiran jin wani abu game da ɓacewarsa, amma har yanzu babu bayani.
Shugaban Amnesty a Najeriya, Isa Sanusi, ya ce Dadiyata mutum ne mai kishin ƙasa kuma yana da kishi wajen faɗin gaskiya a kafafen sada zumunta.
Ya ce akwai yiwuwar ɓacewar Dadiyata na da alaƙa da irin sukar da yake yi wa gwamnati da wasu ‘yan siyasa.
Ko da yake gwamnati ta musanta cewa tana da hannu, Amnesty ta ce dole gwamnati ta ɗauki alhakin binciken abin da ya faru da bayyana gaskiya domin rage wa iyalan Dadiyata raɗaɗi.
Ƙungiyar ta kuma buƙaci hukumomin tsaro su yi bincike mai zurfi, su kuma bayyana sakamakon da suka samu.
Ta ce abin takaici ne a ce shekara shida kenan ba tare da wani bayani dangane da ɓacewarsa ba.
Hakazalika, Amnesty ta buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu, da ya sa baki cikin lamarin domin a san halin da ake ciki.
Ta ce lokaci na ƙurewa, iyalan Dadiyata suna buƙatar amsa guda ɗaya kan inda ya shiga.
Wanda suka halarci taron manema labaran sun haɗa da matarsa Khadija Lame da ƙaninsa Usman Idris.