Wata ƙungiya mai rajin kare muradun al’ummar Hausawa a Nijeriya mai suna Kungiyar Hausawan Nijeriya ta tsaya kai da fata cewa dole a ƙyale Hausawa su kafa ƙungiyarsu kamar kowacce ƙabila tun da dai doka ba ta hana su ba.

Martanin nasu na zuwa ne a daidai lokacin da masu kiran ke shan sukar cewa suna ƙoƙarin rura wutar ƙabilanci ne a Arewacin Nijeriya Najeriya, musamman a daidai lokacin da yankin ke buƙatar haɗin kai domin magance matsalolinsa.

Alƙaluman sakamakon jarabawar bana — JAMB Friedrich Merz ya zama sabon shugaban gwamnatin Jamus

To sai dai ƙungiyar ta ce ba ta ga dalilin da zai sa a ƙalubalanci yunƙurin nasu ba, tun da dai ’yan ƙabilar Yarabawa suna da ƙungiyar Afenifere, ’yan kabilar Ibo suna da Ohaneze, Fulani kuma suna da Miyetti-Allah.

Sun ce hakan na nufin Hausawa ne kawai a cikin manyan ƙabilun ƙasar ba su da ƙungiyarsu ta ƙashin kansu.

A yayin wata zantawarsu da manema labarai a Kano, shugaban kungiyar, Abdullahi Abdullahi, ya ce yunƙurin ya zama wajibi domin kare muradun Hausawa a ƙasar ta kowacce fuska, musamman ta ɓangaren tsaro da ya ce ’yan bindiga na neman hana Hausawa rayuwa a yankunansu.

A cewarsa, “Akwai yunkurin da ake yin a kore samuwar asalin Hausawa ta hanyar cewa a yanzu babu cikakkun Hausawa na asali, a daidai lokacin da ake kiran wasu da cikakkun ’yan kabilar Ibo, Yarabawa da Fulani.

“Ayyukan ta’addancin da ake yi wa Hausawa a kasarsu abin takaici ne.

“Ina wadanda suka kashe Sarkin Gobir? Ina mutanen da Bello Turji ya ƙone ƙurmus a motar bas a Sakkwato ranar da Buhari ya tafi Legas ƙaddamar da littafi?

“Ina matan da ’yan ta’adda suka yi wa fyade a masallaci? Ina labarin jariran da ’yan ta’adda suka ba wa karnuka suka cinye da ransu? Ina labarin mafarautan da aka kashe a jihar Edo a kwanan nan? Waye zai nema musu hakki kuma waye zai bi musu kadi?

“Dole wadannan abubuwan suka sa dole mu Hausawa mu tashi tsaye mu tunkare su tare da masu goya musu baya daga cikin malaman addini, ’yan siyasa, masu rike da sarautun gargajiya da dukkan kungiyoyinsu,” in ji shugaban kungiyar.

Kungiyar ta kuma ce sam ba ta goyon bayan kiran da wasu ke yi na a yi wa rikakken dan ta’addan nan, Bello Turji afuwa, inda suka ce hakan babban kuskure ne da za a yi da-na-sani a kai.

Daga nan sai ƙungiyar ta yi Allah-wadai da abin da ta kira rashin sanin ciwon kai, kan yadda ta ce an kafa wani babban allon talla mai dauke da rubutun “Katsina babu korafi” ɗauke da hoton Shugaban Kasa Bola Tinubu yayin ziyarar da ya kai Jihar Katsina a ’yan kwanakin nan, a maimakon a fada masa matsalar da ake ciki ta rashin tsaro.

Sai dai kuma ƙungiyar ta ce idan zaɓe na gaba ya zo, babu wanda Hausawa za su sake zaɓa sai ɗan uwansu Bahaushe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hausawa Ƙungiyar Hausawa Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Hare-haren Benuwe: Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a asibiti 

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, ya kai ziyara Jihar Benuwe domin jajanta wa mutanen jihar bisa hare-haren da suka faru a wasu ƙauyuka kwanan nan.

Ya je ne domin nuna alhininsa ga waɗanda abin ya shafa da kuma tattaunawa da shugabanni don nemo mafita mai ɗorewa.

Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi

A yayin ziyarar tasa ta yini guda, Shugaba Tinubu ya fara ne da ziyartar Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jihar Benuwe, inda ta duba waɗanda suka jikkata.

Shugaban ya shirya ganawa da iyalan waɗanda aka kashe, da waɗanda suka rasa muhallansu, da kuma shugabannin al’umma.

Hakazalika, Shugaba Tinubu zai gana da manyan masu ruwa da tsaki s jihar, ciki har da sarakunan gargajiya, ’yan siyasa, shugabannin addinai, da ƙungiyoyin matasa.

Burinsa shi ne samo hanyar kawo ƙarshen rikicin da ya addabi yankunan Yelwata, Apa, da kuma Agatu.

Yadda rikicin ya samo asali

Rikicin a Jihar Benuwe ya daɗe ana tafka shi, kuma mafi yawan lokuta rikici ne tsakanin manoma da makiyaya.

Manoma na zargin cewa shanun makiyaya na lalata gonakinsu, yayin da makiyaya ke kukan rashin wuraren kiwo.

A watan Afrilun shekarar 2023, sama da mutum 50 ne suka rasa rayukansu a ƙauyen Umogidi da ke Ƙaramar Hukumar Otukpo.

A watan Yunin 2023 kuma, an kai farmaki ƙauyuka da dama a Guma da Logo, inda mutane da dama suka mutu.

An daɗe ana zargin wasu daga cikin hare-haren ƙungiyar Miyetti Allah da wasu ’yan bindiga ne ke kai wa.

Yawancin mutane sun rasa gidajensu da gonakinsu, wasu kuma sun tsere zuwa sansanonin ’yan gudun hijira.

Duk da irin ƙoƙarin da gwamnonin da suka gabata suka yi, har yanzu matsalar na ci gaba da faruwa.

Ziyarar Shugaba Tinubu tana ƙarfafa wa mutane gwiwa cewa za a iya samo mafita domin kawo ƙarshen kashe-kashen da ke faruwa a Benuwe da sauran wuraren da rikicin ya shafa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista
  • Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
  • An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana
  • Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 
  • Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos
  • An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya
  • An ɗaure mutum 7 kan yi wa ɗan sanda rauni a Kano
  • Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara
  • An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina
  • Hare-haren Benuwe: Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a asibiti