Wata mata ta auri maza biyu a lokaci guda a Kano
Published: 6th, May 2025 GMT
An gurfanar da wata matar aure a gaban kotun Musulunci kan zargin ta da auren maza biyu a lokaci guda a Jihar Kano.
Wannan lamari ya faru ne wata shida bayan auren matar mai suna Harira Muhammad Tudun Murtala da mijinta na farko mai suna Sagiru Shu’aibu Tudun Murtala.
A yayin zaman Kotun Musulunci da ke zamanta a Post Office Malam Sagiru ya shaida wa alkali cewa kasncewar ba tare suke zaune da matar tasa ba, wata rana ya je gidanta sai kawai ya iske ta tare da wani mutum a gan gadon aurensu, lamarin da ya sa ya sanar da makwabta abin da ke faruwa.
Bayan gurfana da ita a gaban kotu, Harira ta musanta cewa akwai aure tsakaninta da mijin nata na farko, lamarin da ya sa alkali ya umarce ta da yin rantsuwa da Alkur’ani, amma sai ta janye kalamanta.
NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ‘Yan Gwagwarmaya Ke Shiga Tasku A Najeriya? ’Yan bindiga sun kashe matar aure bayan karɓar N10m kuɗin fansaA nasa bangaren, mijinta na biyu, mai suna Bello Abdullahi ’Yankaba ya shaida wa kotun cewa aurenta ya yi a kan sadaki naira dubu dari kuma wani kawunta mai suna Abdullahi Umar ne waliyyin aurensu.
Bayan sauraron bayanansu, alkalin kotun, Khadi Munzali Tanko Soron-Dinki, ya ba da umarnin a zurfafa bincike kan lamarin sa’annan a tsare matar da mijin nata na biyu a gidan yari, zuwar ranar 16 ga watan Mayu da za a ci gaba da sauraron shari’ar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: mijinta na farko
এছাড়াও পড়ুন:
NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano
A cewarsa, shaye-shayen miyagun kwayoyi, shi ne musabbabin da ke haifar da aikata laifuka da dama, wanda galibi ke zama sanadin tashin hankali da rikice-rikice a cikin al’umma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp