Aminiya:
2025-05-06@13:12:26 GMT

Wata mata ta auri maza biyu a lokaci guda a Kano

Published: 6th, May 2025 GMT

An gurfanar da wata matar aure a gaban kotun Musulunci kan zargin ta da auren maza biyu a lokaci guda a Jihar Kano.

Wannan lamari ya faru ne wata shida bayan auren matar mai suna Harira Muhammad Tudun Murtala da mijinta na farko mai suna Sagiru Shu’aibu Tudun Murtala.

A yayin zaman Kotun Musulunci da ke zamanta a Post Office Malam Sagiru ya shaida wa alkali cewa kasncewar ba tare suke zaune da matar tasa ba, wata rana ya je gidanta sai kawai ya iske ta tare da wani mutum a gan gadon aurensu, lamarin da ya sa ya sanar da makwabta abin da ke faruwa.

Bayan gurfana da ita a gaban kotu, Harira ta musanta cewa akwai aure tsakaninta da mijin nata na farko, lamarin da ya sa alkali ya umarce ta da yin rantsuwa da Alkur’ani, amma sai ta janye kalamanta.

NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ‘Yan Gwagwarmaya Ke Shiga Tasku A Najeriya? ’Yan bindiga sun kashe matar aure bayan karɓar N10m kuɗin fansa

A nasa bangaren, mijinta na biyu, mai suna Bello Abdullahi ’Yankaba ya shaida wa kotun cewa aurenta ya yi a kan sadaki naira dubu dari kuma wani kawunta mai suna Abdullahi Umar ne waliyyin aurensu.

Bayan sauraron bayanansu, alkalin kotun, Khadi Munzali Tanko Soron-Dinki, ya ba da umarnin a zurfafa bincike kan lamarin sa’annan a tsare matar da mijin nata na biyu a gidan yari, zuwar ranar 16 ga watan Mayu da za a ci gaba da sauraron shari’ar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: mijinta na farko

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan fashi sun kashe magidanci a Kano

Ana fargabar cewa wasu da ake zargin ’yan fashi ne sun kashe wani magidanci a  unguwar Ɗanbare da ke Ƙaramar Hukumar Kumbotso a Jihar Kano.

Bayanai sun ce waɗanda ake zargin sun kashe magidancin ne da adda, bayan sun shiga gidansa da yake zaune domin sata da asuba.

To sai dai mazauna unguwar sun bayyana wa Aminiya cewa sun samu nasarar kama wanda suke zargin shugaban ’yan fashin ne, sun kuma miƙa shi ofishin ’yan sanda na Ɗorayi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe matar aure bayan karɓar N10m kuɗin fansa
  •  Sojojin HKI Sun Kai Hare-hare A Sassa Mabanbanta Na Kasar Yemen
  • ’Yan fashi sun kashe magidanci a Kano
  • Kotu za ta rataye matashi kan kisan karuwa
  • Yau Kotun ICJ ke yanke hukunci kan zargin da Khartoum ke wa UEA
  • An Kama Wani Ɗan Ghana Bisa Zargin Kai Mata Hajji Ba Tare Da Lasisi Ba
  • Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga 3, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace
  • Lakurawa sun kashe ’yan bijilanti 11 a Sakkwato
  • An kama masu garkuwa da mutane 3 da kuɓutar da wasu