Aminiya:
2025-08-05@23:57:56 GMT

Majalisar Dattawa ta kafa kwamitin lura da gwamnan riƙo na Jihar Ribas

Published: 6th, May 2025 GMT

Majalisar Dattawa ta kafa kwamiti mai mambobi 18 domin sanya idanu kan yadda gwamnan riƙo na Jihar Ribas Vice Admiral Ibok Ete Ibas mai ritaya ke tafi da aikinsa.

Majalisar ta ce ta ɗauki matakin ne a wani yuƙuri na ƙarfafa shugabanci na gari ba tare da rufa-rufa ba a jihar da ke kudu maso kudancin Najeriya.

Alƙaluman sakamakon jarabawar bana — JAMB Friedrich Merz ya zama sabon shugaban gwamnatin Jamus

Shugaban Majalisar Dattawan, Godswill Akpabio ya sanar yayin zaman majalisar na yau Talata cewa kafa kwamitin na da matuƙar mahimmancin wajen sa ido kan abubuwan da ke faruwa a jihar.

Shugaban masu rinjaye Opeyemi Bamidele ne shugaban kwamatin, yayin da mambobin kuma sun haɗa da Adamu Aliero, da Osita Izunaso, da Osita Ngwu, da Kaka Shehu, da Aminu Abass, da Tokunbo Abiru, Adeniyi Adebire.

A wannan Talatar ce shi ma Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas Tajudeen ya sanar da cewa za su kafa kwamitin da zai jiɓanci tabbatar da sulhu kan rikicin siyasa da ya yi wa Jihar Ribas dabaibayi.

Abbas wanda ya ce kwamitin wanda za su yi tarayya da Majalisar Dattawa wajen kafa shi zai ƙunshi wasu manyan ƙasar nan da ake mutuntawa domin tabbatar da wanzuwar dimokuraɗiyya a jihar.

Ana iya tuna cewa a watan Maris ne Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas sakamakon abin da ya kira “karyewar doka da oda” wanda ya auku sanadiyyar rikicin siyasa tsakanin Gwamna Similanayi Fubara na PDP mai adawa da tsohon Gwamna Wike mai ƙawance da APC mai mulki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Ribas Majalisar Dattawa

এছাড়াও পড়ুন:

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Kai Ziyara Ta Ta’aziyya Ga Sabon Sarkin Gusau

Tawagar Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta kai ziyarar ta’aziyya ga sabon Sarkin Gusau, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello a fadarsa.

 

Ziyarar ta biyo bayan rasuwar marigayi Sarkin Gusau, Dakta Ibrahim Bello, wanda aka yi ta murna da shi a bisa kyakkyawan jagoranci da kuma gudunmawar ci gaban masarautu da jihar Zamfara.

 

Hajiya Larai Musa Lawal, ta mika sakon ta’aziyyar uwargidan shugaban kasar ga iyalan gidan sarautar tare da addu’ar Allah ya jikansa da rahama.

 

Ta kuma mika sakon taya murna ga sabon sarkin, tare da yi masa fatan Allah ya kara masa lafiya mai cike da hikima da zaman lafiya da hadin kai.

 

A nasa jawabi, sabon Sarkin Katsinar Gusau, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello, ya nuna jin dadinsa ga uwargidan bisa wannan ziyarar da ta kai da kuma ci gaba da bada goyon baya.

 

Ya bayyana ta a matsayin ‘yar uwa kuma ya gode wa Gwamna Dauda Lawal bisa amincewar da aka yi masa.

 

Sarkin ya yi alkawarin rike gadon mahaifinsa da ya rasu tare da yin shugabanci cikin kankan da kai da sadaukarwa.

 

Tawagar ta kuma ziyarci Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Zamfara kuma Sarkin Anka, Alhaji Attahiru Muhammad Ahmad, domin yi masa ta’aziyyar rasuwar marigayi Sarkin Gusau.

 

Alhaji Attahiru ya yabawa uwargidan gwamnan wannan karimcin, inda ya bayyana hakan a matsayin alamar hadin kai da mutunta cibiyoyin gargajiya.

 

AMINU DALHATU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Katsina ta amince da sabuwar Dokar Masarautu
  • Iran Ta Kafa Kwamitin Tsaron Kasa Wanda Zai Kula Da Sabbin Matsalolin Tsaro
  • An Zargin Akantan jihar Nasarawa Da Shiga Harkokin Siyasa
  • Gwamnatin Kano Ta Karɓi Rahoton Binciken Kwamishinan Sufuri Kan Belin Wanda Ake Zargi Da Safarar Kwayoyi
  • Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Kai Ziyara Ta Ta’aziyya Ga Sabon Sarkin Gusau
  • Wani Dan Siyasa Ya Shirya Addu’o’i Na Musamman Domin Samun Zaman Lafiya A Zamfara
  • Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi
  • Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a