Wanda ya ba su masauki a otal, gida, ko wani wurin zama shi ma zai fuskanci irin wannan hukunci.

Duk wanda ya je aikin Hajji ba tare da izini ba ko dan ƙasa ne ko wanda ya daɗe fiye da lokacin zama za a kori mutum zuwa ƙasarsa tare da dakatar da shi daga shiga Saudiyya na tsawon shekaru 10.

Hukumomin shari’a za su kuma karɓi motocin da aka yi amfani da su wajen safarar waɗanda ba su da izinin yin aikin Hajji, musamman idan motocin na masu laifin ne.

A wani labari da ya shafi aikin Hajji, Hukumar Hajji ta Ka6sa (NAHCON) ta sanar da cewa jigilar mahajjatan Nijeriya na shekarar 2025 zai fara ne daga ranar 9 ga watan Mayu.

A cewar wata sanarwa da Daraktar Watsa Labarai ta NAHCON, Fatima Sanda Usara, ta fitar ta ce mahajjata 43,000 ne suka riga suka biya kuɗin Hajji a bana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Saudiyya Tara

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗaliba ’yar shekara 15 daga Yobe ta lashe Gasar Muhawara ta Duniya

Wata ɗaliba ’yar shekara 15 daga Jihar Yobe, Rukayya Muhammad Fema, ta zama Gwarzuwar Shekarar 2025 a Gasar Muhawara ta Duniya ta Teen Eagle.

Rukayya ta yi zarra ne a wannan babbar gasa da ta gudana a birnin Landan na ƙasar Birtaniya, inda zaƙaƙuran ɗalibai daga ƙasashe 69 a faɗin duniya suka fafata a tsakaninsu.

Jami’in Sadarwar Zamani na Gwamnatin Jihar Yobe, Yusuf Ali, ya bayyana cewa Rukayya ta samu kafa wannan tarihi ne a dalilin zurfin tunani da kuma kaifin basirarta da kuma fahimtar al’amuran duniya, duk kuwa da ƙarancin shekarunta.

Ɗalibar daga Kwalejin Nigerian Tulip International (NTIC), Rukayya, ta ɗauki hankalin alƙalan gasar da sauran jama’a saboda ƙarfin hujjojinta da ta gabatar da kuma iya bayani mai ganawarsa cikin natsuwa, lamarin da ya ba ta damar doke duk abokan karawarta.

Nafisa ta cancaci kyautar Dala 100,000 da gida da OON —Pantami NAJERIYA A YAU: Yadda Ayyuka Suka Ragu A Jihohi Bayan Kudin Shiga Ya Karu

Ita ce mutum ya biyu daga Jihar Yobe kuma daga makaranta tare da Nafisa Abdullah Aminu wadda ta zama gwarzuwa a ɓangaren Harshen Turanci a yayin gasar, inda suka wakilci Najeriya, ƙasa mai yawan al’umma sama da miliyan 200.

Nasararta nuna irin basirar da Allah Ya yi wa matasan Najeriya inda suke yin zarra a sassan duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗaliba ’yar shekara 15 daga Yobe ta lashe Gasar Muhawara ta Duniya
  • ’Yar shekara 17 daga Yobe ta lashe Gasar Turanci ta Duniya
  • Sanata Buba ya ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobi kyauta
  • Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15
  • Gwamnatin Kano Ta Karɓi Rahoton Binciken Kwamishinan Sufuri Kan Belin Wanda Ake Zargi Da Safarar Kwayoyi
  • Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Duba Titi Mai Tsawo Kilomita 49
  • Ma’aikatan jinya sun dakatar da yajin aiki a faɗin Najeriya
  • Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu