Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-04@13:49:39 GMT

Sarki Sanusi 16 Ya Yi Sabbin Nadade A Kano

Published: 4th, May 2025 GMT

Sarki Sanusi 16 Ya Yi Sabbin Nadade A Kano

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya nada sabon Galadima na Kano, Alhaji Munir Sanusi Bayero, tare da wasu manyan ‘yan Majalisar Sarki Masarautar su hudu.

 

 

 

Sabbin masu rike da mukaman gargajiya da aka yi wa rawani sun hada da Wamban Kano, Alhaji Kabir Tijjani Hashim, Turakin Kano, Alhaji Mahmud Ado Bayero, Tafidan Kano, Adam Lamido Sanusi, da Yariman Kano, Alhaji Ahmad Abbas Sanusi.

 

 

Da yake jawabi bayan bikin nadin, Sarki Sanusi ya shawarci sabbin sarakunan da aka nada da su kasance masu koyi da shugabanni, inda ya ce sun riga sun nuna biyayya, tawali’u da tausayin talaka.

 

 

 

Ya bayyana irin gudunmawar da suke bayarwa ga al’umma, ya kuma bukace su da su ci gaba da yin koyi da magabata.

 

 

Bikin kaddamarwar ya samu halartar gwamnan jihar Abba Yusuf da sauran ‘yan majalisar zartarwa na jihar da shugabannin gargajiya da na addini da ‘yan uwa da abokan arziki da dai sauransu.

 

A wani biki na daban da aka gudanar a fadar Karamar Hukumar Nassarawa, Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya nada Alhaji Sunusi Lamido Ado Bayero a matsayin sabon Galadiman Kano, inda ya bayyana irin tsarin shugabancin da ke gudana a masarautar.

 

 

Cover /Abdullahi Jalaluddeen/Kano

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sarkin Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Aikin Gina Tashar Jirgin Ƙasa A Kano Yana Ci Gaba Gadan-gadan

Faɗin ginin, wanda ya haura sukwaya mita 13,000, ya ƙunshi babban ginin tashar da ababen da ke tattare da shi, kuma zai kasance tashar da ta fi kowace girma a layin dogon da ake kira Kaka Reluwe.

 

Kaka Reluwe na nufin hanyar dogo daga KAduna zuwa KAno.

 

Kamfanin CCECC ya ce idan an gama aikin, zai taimaka gaya wajen haɓaka harkokin sufuri kuma ya kawo matuƙar sauƙi ga miliyoyin matafiya a ɓangaren Kano na hanyar jirgin.

 

Shi dai wannan layin dogo na Kaka Reluwe, hanya ce mai tsawon kilomita 204. Ta tashi daga Kaduna, ta bi ta Zariya, zuwa Kano.

 

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ne ya ƙaddamar da ita a ranar 15 ga Yuli, 2021, sannan gwamnatin Bola Ahmed Tinubu tana ci gaba da aikin babu ƙaƙƙautawa don tabbatar da ta kammala ta a kan lokaci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Isra’ila sun kaddamar da sabbin hare-hare kan Siriya
  • Yadda aka yi bikin yaye sabbin matuƙa jiragen Rundunar Sojin Saman Najeriya
  • Sarki Sanusi ya naɗa sabon Galadiman Kano da wasu 4
  • NLC Kano Ta Yabawa Gwamnati Na Kokarin Kyautata Jin Dadin Ma’aikata
  • Aikin Gina Tashar Jirgin Ƙasa A Kano Yana Ci Gaba Gadan-gadan
  • Ranar Ma’aikata: Gwamnan Kano Ya Biya Basussukan Fansho, Ya ƙirƙiro Sabbin Ma’aikatu