Sarki Sanusi 16 Ya Yi Sabbin Nadade A Kano
Published: 4th, May 2025 GMT
Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya nada sabon Galadima na Kano, Alhaji Munir Sanusi Bayero, tare da wasu manyan ‘yan Majalisar Sarki Masarautar su hudu.
Sabbin masu rike da mukaman gargajiya da aka yi wa rawani sun hada da Wamban Kano, Alhaji Kabir Tijjani Hashim, Turakin Kano, Alhaji Mahmud Ado Bayero, Tafidan Kano, Adam Lamido Sanusi, da Yariman Kano, Alhaji Ahmad Abbas Sanusi.
Da yake jawabi bayan bikin nadin, Sarki Sanusi ya shawarci sabbin sarakunan da aka nada da su kasance masu koyi da shugabanni, inda ya ce sun riga sun nuna biyayya, tawali’u da tausayin talaka.
Ya bayyana irin gudunmawar da suke bayarwa ga al’umma, ya kuma bukace su da su ci gaba da yin koyi da magabata.
Bikin kaddamarwar ya samu halartar gwamnan jihar Abba Yusuf da sauran ‘yan majalisar zartarwa na jihar da shugabannin gargajiya da na addini da ‘yan uwa da abokan arziki da dai sauransu.
A wani biki na daban da aka gudanar a fadar Karamar Hukumar Nassarawa, Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya nada Alhaji Sunusi Lamido Ado Bayero a matsayin sabon Galadiman Kano, inda ya bayyana irin tsarin shugabancin da ke gudana a masarautar.
Cover /Abdullahi Jalaluddeen/Kano
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sarkin Kano
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
Gwamnatin Kano ta raba kayayyakin aiki na zamani na kimanin Naira Miliyan 250 ga cibiyoyin horas da sana’o’in hannu biyu da ke Kofar Mata da Gwale, domin yaƙi da shan miyagun kwayoyi da aikata laifuffuka a tsakanin matasa, ta hanyar samar da aikin yi.
Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Dakta Yusuf Kofarmata, ya ce an amince da tallafin ne bisa umarnin Gwamna Abba Kabir Yusuf don bunƙasa tsare-tsaren ƙarfafa matasa a jihar.
Ya bayyana cewa an samar da injinan sarrafa fata guda 26 domin cibiyoyin wadanda al’ummar yankunan suka kafa, amma ba su da isassun kayayyakin aiki.
Ya ce Gwamna Yusuf ne ya gina Cibiyar Horaswar ta Gwale kasancewar nan ce mazabarsa, yayin da Dakta Yakubu Adam ya taka rawa wajen gina ta Kofar-Mata.
Ya ce cibiyoyin za su samar da daruruwan ayyukan yi tare da rage matsalolin zaman kashe-wando da ta’addanci a tsakanin matasa.
A nasa jawabin, Ali Musa Kofar-Mata na ƙungiyar IKMA ya gode wa gwamnati bisa wannan gudummawar da ya kira mai sauya rayuwa.
Ya ce cibiyar ta fara ɗaukar matasa maza da mata, kuma horon zai ɗauki watanni uku kafin a shiga sabon zagaye.
Abdullahi Jalaluddeen