Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-04@17:09:27 GMT

Sarki Sanusi 16 Ya Yi Sabbin Nadade A Kano

Published: 4th, May 2025 GMT

Sarki Sanusi 16 Ya Yi Sabbin Nadade A Kano

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya nada sabon Galadima na Kano, Alhaji Munir Sanusi Bayero, tare da wasu manyan ‘yan Majalisar Sarki Masarautar su hudu.

 

 

 

Sabbin masu rike da mukaman gargajiya da aka yi wa rawani sun hada da Wamban Kano, Alhaji Kabir Tijjani Hashim, Turakin Kano, Alhaji Mahmud Ado Bayero, Tafidan Kano, Adam Lamido Sanusi, da Yariman Kano, Alhaji Ahmad Abbas Sanusi.

 

 

Da yake jawabi bayan bikin nadin, Sarki Sanusi ya shawarci sabbin sarakunan da aka nada da su kasance masu koyi da shugabanni, inda ya ce sun riga sun nuna biyayya, tawali’u da tausayin talaka.

 

 

 

Ya bayyana irin gudunmawar da suke bayarwa ga al’umma, ya kuma bukace su da su ci gaba da yin koyi da magabata.

 

 

Bikin kaddamarwar ya samu halartar gwamnan jihar Abba Yusuf da sauran ‘yan majalisar zartarwa na jihar da shugabannin gargajiya da na addini da ‘yan uwa da abokan arziki da dai sauransu.

 

A wani biki na daban da aka gudanar a fadar Karamar Hukumar Nassarawa, Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya nada Alhaji Sunusi Lamido Ado Bayero a matsayin sabon Galadiman Kano, inda ya bayyana irin tsarin shugabancin da ke gudana a masarautar.

 

 

Cover /Abdullahi Jalaluddeen/Kano

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sarkin Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Mai Martaba Sarkin Dutse Ya Kaddamar Da Rabon Zakka Ta Shekarar 1446

Mai Martaba Sarkin Dutse, Dr Hameem Nuhu Muhammadu Sunusi ya kaddamar da rabon zakkar kudi ta shekarar musulunci ta 1446 a gundumar Yayari dake Karamar Hukumar Buji.

A jawabin sa, Mai Martaba Sarkin ya ja hankalin al’umma da su ci gaba da fitar da hakkin Allah domin samun makoma a nan duniya da kuma gobe kiyama.

Ya nuna gamsuwa da nasarorin da Gundumar ta samu wajen tattara zakka a masarautar sa.

Daga bisani ya karrama Hakimin Yayari, Alhaji Garba Muhammad da Dagaci da kuma Mai Unguwar cikin garin Yayari.

A jawabin sa, Sa’in Dutse, Mallam Mahmud Yunusa yace gundumar Yayari ce ta zo na 1 a tattara zakkar kudi yayin da Gundumomin Gantsa da Fagam suka zo na 2 da na 3.

 

Ya ce an raba zakkar fiye da naira miliyan goma ga mutane 300, inda wasu suka sami zakkar naira dubu 20 zuwa naira dubu 35.

A jawabin sa, shugaban Karamar Hukumar Buji Najibullah Falalu Tukur Gantsa yace Karamar Hukumar zata ci gaba da hadin kai da gundumar Yayari da sauran gundumomin hakimanta wajen ganin Karamar Hukumar ta rike matsayinta na ja gaba wajen tattara zakka.

Ya kuma yabawa mai Martaba Sarkin Dutse bisa jajircewar sa wajen ganin al’umma suna fitar da hakkin Allah.

 

Mai martaba sarki ya samu rakiyar Galadiman Dutse da sauran ‘yan majalissar Sarki.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Kai Ziyara Ta Ta’aziyya Ga Sabon Sarkin Gusau
  • An yi wa Jalo Daudu sarautar Tafarkin Gombe
  • An yi wa Jalo Daudu a sarautar Tafarkin Gombe
  • Mai Martaba Sarkin Dutse Ya Kaddamar Da Rabon Zakka Ta Shekarar 1446
  • Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi
  • An ƙara hakimai 6 a Masarautar Katsina
  • Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Sha Alwashin Inganta Kwazon Kananan Hukumomin Jihar