Aminiya:
2025-05-01@16:06:25 GMT

Zargin Tinubu: Gaskiya Naja’atu ta fada kan Nuhu Ribadu —El-Rufai

Published: 6th, February 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya goyi bayan Hajiya Naja’atu Muhammad a rikicinta da Mashawarcin Shugaban Kasa kan Sha’anin Tsaro, Nuhu Ribadu.

Rikicin ya kunno kai ne bayan Naja’atu ta bulla a wani bidiyo inda take kushe Nuhu Ribadu ads aiki a gwamantin Tinubu alhali a lokacin da yake Shugaban Hukumar Yaki da Masu Karya Tattalin Arzikin Kasa (EFCC), ya soki Tinubu da zargin sa da almundahana a yayin taron Majalisar Zartaswa ta Kasa (FEC).

Bayan haka ne Ribadu ta hannun lauyansa Ahmed Raji (SAN), ya bukaci ta janye kalaman nata tare da neman afuwarsa, yana mai barazanar maka ta kotu idan ba ta janye ba, domin kalaman nata na neman zubar masa da kima.

Amma duka da haka, Naja’atu, wadda tsohuwar Kwamishina ce a Hukumar Kula da Aikin Dan Sanda (PSC) ta tsaya kai da fata, cewa ba za ta janye ba ballanta na da ba da hakuri.

NAJERIYA A YAU: Tasirin Yankan Angurya A Rayuwar Mata Ɗan sanda ya harbe kansa har lahira a Nasarawa Gobara ta yi ajalin almajirai 17 a Zamfara
Naja’atu ta kara da cewa a shirye take, ko Kotun Duniya zai kai ta, domin tana da kwararan hujjoji da za ta kare abin da ta fada.

Ana cikin haka ne, El-Rufai ya bayyana cewa gaskiya ne maganar da Naja’atu game da zargin da Nuhu Ribadu ya yi kan Tinubu gaskiya ne.

El-Rufai a wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta ya bayyana cewa yana nan Ribadu ya yi wadannan kalamai a taron FEC, lokacin shi El-Rufai yana Ministan Abuja.

Ya ce da alama “Nuhu na fama da matsanciyar cutar matuwa,” inda ya kara da cewa akwai rubutattun hujjoji da ke tabbatar da kalaman Naja’atu, ciki har da takardun Majalisar Dattawa a shekarar 2006.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje

Shugaban kasar Iran ya nuna murnarsa da yin maraba lalai da masu zuba hannun jari daga kasashen waje a Iran

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana Iran a matsayin dandalin da ta dace wajen zuba hannun jari da gudanar da harkar kasuwanci, yana maraba da masu zuba hannun jari na kasashen waje da ‘yan kasuwa na duniya da su shiga harkokin tattalin arziki da zuba hannun jari a Iran.

A yayin bikin bude baje koli karo na bakwai na baje kolin kayayyakin da Iran ke fitarwa zuwa kasashen ketare (Iran Expo 2025) a safiyar yau Litinin, shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi maraba da baki na kasashen waje da suka halarci wannan baje kolin, yana mai cewa, “Ko da yake ana gabatar musu da wani hoto na daban da ya yi hannun riga da hakikanin Iran da al’ummar kasarta a ketare, amma Iran kasa ce mai karbar baki, kuma al’ummarta masu tausayi da nuna jin kai.”

Yana mai jaddada cewa: Iran wata kafa ce da ta dace da zuba hannun jarin kasuwanci da yawon bude ido na ketare, Pezeshkian ya bayyana cewa da wannan karfin, kuma ta hanyar ciniki, zuba hannun jari, da hadin gwiwa, za a iya samar da makoma mai haske ga duniya, mai cike da tsaro da zaman lafiya.

Ya kuma yi nuni da cewa: Yake-yaken da suka gani a duniya sun samo asali ne sakamakon rashin mutunta hakkokin bil’adama da na kasashe, Pezeshkian ya jaddada mutunta yankin kasar Iran da hakkokin kasashe, yana mai bayyana Shirin Iran na gudanar da duk wani hadin gwiwa a fannin kimiyya, tattalin arziki, siyasa, da zamantakewa da duniya, da kuma mika ilimi ga sauran kasashe ba tare da iyakancewa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Gwamnan Neja Ya Ki Halartar Bikin Ranar Ma’aikata, Ana Zargin Akwai Takun Saka
  • Al’umma Sun Shiga Fargaba Yayin Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Sun Kashe Limamin Da Suka Sace A Zamfara
  • Tinubu Ba Ya Tsoma Baki A Ayyukan EFCC – Olukoyede
  • AU ta janye takunkumin da ta ƙaƙaba wa Gabon
  • Tinubu zai ziyarci Katsina
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai