2025-12-14@13:19:16 GMT
إجمالي نتائج البحث: 12469

«mai albarka»:

    Shugabannin kasashen kungiyar Tattalin Arzikin kasashen Yammacin Afirka ECOWAS sun hallara a birnin Abuja na  Najeriya don bude babban taron koli da za’a fara yau Lahadi. Bayanai sun ce rashin tsaro da kuma Juye-juyen Mulki musamman masu sarkakiya da aka samu a Guinea Bissau da kuma yunkurinsa a jamhuriyar Benin shi ne ake ganin taron  zai fi mayar da hankali a yayin wannnan taron  na musamman. Taron na zuwa ne mako daya bayan yunkurin kifar da gwamnatin Benin da Shugaban kasar Patrice Talon ke jagoranta a kwatano, da kuma damuwa kan rikicin siyasa a Guinea-Bissau da tabarbarewar tsaro a arewacin kasashen gabar tekun yammacin Afirka. Wannan shi ne taron koli na farko da Shugaban kasar Sierra Leone Julius Maada Bio ke...
    Iran ta karbi bakuncin bude taron musamman da wakilan kasahen dake makwabtaka da kasar Afghanisatan tare da kasar Rasha, domin gudanarda  tattaunawa mai ma’ana a yankin da kuma bayyana irin kalubalen da ake fuskanta a kasar Afghanistan. Wannan tattaunawar ta bayyana irin mataken da za’a dauka da kuma bitar tattaunawa da aka yi kusan shekaru 2 da suka gabata, da haka yake nuna irin bukatar da ake da ita na yi sauri wajen yin aiki tare tsakanin kasashen , wanda kai tsaye zai shafi yanayin da ake ciki a kasar Afghansitan,  domin samun tabbacin da daidaito a kasar Afgahnistan ya damu dukkan yankin. Wakilai daga kasashen Pakistan, Rasha, china, Tajikistan, uzbakestan da kuma turkimanistan ne manyan jami’an su suka halarci...
    Rahotanni sun bayyana cewa sojojin Isra’ila sun karbe wani matashi bafalasdine a wani samame da suka kai a cikin dare a wani gari dake Arewacin gabar yammacin kogin Jodan da isara’ila ta mamaye, wani mazaunin yankin yace sojojin na cin karensu ba babbaka a yankin. Kamfanin dillancin labaran yankin falasdinu WAFA ya sanar cewa sojojin isara’ila sun bude wuta kan wani yaro matashi dan shekaru 16 da haihuwa Mohammad iyad  a arewa masu yammacin garin jenin inda anan take yace ga garunku nan. Yan sa’oi kafin afkuwar lamarin sojojin Isra’ila sun farma garin inda suka fara binciken gida-gida tare da harbe-harbe da harsashi mai rai, da kuma wurga gurneti, lamarin da ya jawo mayar da martani daga al’ummar garin, Kungiyar...
    Shugaban majalisar shawarar musulunci na kasar Iran Mohammad baqir Qalibaf  da kuma takwaransa na kasar Ethiopia Tagesse Chafo sun yi taron maneman labarai inda suka jaddada game da kyakkyawar alaka dake tsakanin majalisun guda biyu, da kuma kafa kwamitin hadin guiwa na tattali arzki da kuma alakar kula da iyakoki Wannan musayar ra’ayi  da aka yi tsakanin shuwagabannin majalisar kasar iran da Ethiopia yana nuna irin  muhimmancin karfafa dangantaka tsakanin Tehran da Adis Ababa a bangaren siyasa da tattalin arziki . Ethiopia tana da matsayi mai muhimmancin a yankin kahon Afrika kuma kusa da tekun bahar maliya da kuma babul mandab wuri mai muhimmancin a matakin  kasa da kasa da ake binciken jirajen ruwan kasuwanci da makamashi, wannan yasa iran...
    Rahotanni sun bayyana cewa gwamnatin kasar Ghana ta kori wasu yahudawa guda 3 daga kasar domin mayar da martani kan matakin da isra’ila ta dauka na korar yan kasarta ta filin hawa da saukar jiragen sama na Ben Gurion. Wannan mataki ya aike da wani sakon diplomasiya ne dake nuna cewa kasar Ghana a shirye take ta dauki matakin mayar da martani don kare martabar kasarta da hakkin yan kasarta kan duka wani matakin cin zarafi da isra’ila za ta dauka . Ma’aikatar harkokin wajen Kasar Ghana tace  tana kimanta duk wata dangantaka dake takaninta da kasashe don haka tana sa rana za’a girmama yan kasarta a duk mua’malar da za’a yi da su kamar yadda sauran kasashe ke sa...
    Daga Usman Muhammad Zaria Majalisar Gudanarwa ta huɗu ta Jami’ar Tarayya da ke Dutse (FUD) a Jihar Jigawa ta amince da naɗa Farfesa Ahmed Muhammed Gumel a matsayin shugabar jami’ar na huɗu. Shugaban Majalisar Gudanarwar jami’ar, Farfesa Shuaibu Oba Abdulraheem, ya bayyana cewa an bi tsari mai tsauri da cikakken bincike wajen zaɓen sabon shugaban jami’ar. A cewarsa, an tantance ’yan takara 2, inda a ƙarshe Farfesa Gumel ya fito a matsayin sabon Shugaban Jami’ar ta FUD. Farfesa Uba ya taya sabon shugaban jami’ar murna,  tare da yi masa fatan Allah Ya mishi jagora da nasara wajen sauke nauyin da aka dora masa. A nasa jawabin, sabon Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Ahmad Muhammad Gumel, ya gode wa Allah Madaukakin...
    Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Najeriya, Laftanar-Janar Shaibu ya yaba, ya bayyana cewa buɗe cibiyoyin horas da sabbin kuratan sojoji (Depot) a jihohin Kudu zai ƙara ƙarfin rundunar wajen karɓar sabbin ma’aikata a faɗin ƙasa. Laftanar-Janar Shaibu ya bayyana cewa za a buɗe sabbin cibiyoyin horas da sabbin kuratan sojojin ne a Osogbo da ke Jihar Osun da kuma Abakaliki a Jihar Ebonyi. Ya bayyana haka ne a yayin bikin yaye sabbin dakarun soji 3,439 da aka yi a Cibiyar Horas da Sabbin Kuratan sojoji (Depot) da ke Zariya, inda ya shawarce su  da su zama masu kishin ƙasa da jajircewa. Ya yaba wa sabbin sojojin bisa jajircewa, juriya da ƙwarewa da suka nuna a tsawon watannin da suka shafe...
    Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Ƙarfafa Fitar da Kayayyaki ta Ƙasa (NEPC), reshen Jihar Jigawa, ta bayyana cewa ta fara taron wayar da kan mata na tsawon kwanaki biyu kan damar kasuwancin fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje a ranar Asabar. Da yake jawabi a wajen buɗe taron, Shugaban ofishin kula da Jigawa, Alhaji Abdulkadir Aliyu, ya ce an shirya taron ne domin wayar da kan mata ’yan kasuwa game da damar shiga kasuwannin duniya. A cewarsa, manufar taron ita ce samar da ƙwararrun mata masu fitar da kayayyaki, tare da basu damar samun tallafin kasuwanci, hanyoyin sadarwar kasuwanci, da damar samun kuɗaɗen jari. Ya ce “Tsawon kwanaki biyun nan, muna fatan ƙarfafa shigar mata cikin kasuwanci ta...
    An haife ni a garin Kano, amma asalina ‘yar Adamawa ce, kuma asalina ‘yar Maiduguri ce, sannan kuma yaren Margi ce ni. Bayan na girma a Kano na fara karatu a makarantar sojoji ‘Bokabo Barrack’, daga nan muka bar ‘Katsina Road’ muka koma ‘Yar Akuwa. Na fara firamare ‘Gidan Gona Special Primary School’. Bayan nan na tafi ‘Jigawa state’ wato Malam Madori, a ‘first time’ ‘yar’uwata ta rasu. Aka canja min makaranta aka dawo da ni ‘Gobernment Secondary School Kura’, a nan na kammala aji shida. Daga nan na tafi ‘Federal Polytechnic Yola’ a nan na karasa karatuna wanda nake da diploma. A yanzu kuma ina Na’ibawa a nan na girma, a nan aka yi min aure, yanzu komai nawa...
    Yunƙurin tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, na kafa wata rundunar tsaro mai kama da Hisbah ya jawo ce-ce-ku-ce a faɗin jihar. Wannan shiri da ya kira Hisbah mai zaman kanta, an tsara shi ne domin ɗaukar ma’aikata 12,000 waɗanda gwamnatin Kano mai ci ta sallama daga a Hukumar Hisbah. Sanarwar ta haifar da ra’ayoyi mabambanta, inda wasu ke goyon baya, wasu kuma na adawa, yayin da wasu ke taka-tsantsan. Dalilin da ya sa muka ziyarci Obasanjo — Turaki Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno EFCC na ƙoƙarin daƙile muradin Malami na yin takarar gwamna — ADC Kazalika, mutane da dama na tambayar sahihancin kafa rundunar a bisa doka, manufar shirin da kuma tasirinsa ga tsaro da shugabanci...
    Sanarwar ta Sulaiman ta ƙara da cewa, asusun cibiyar ya mayar da hankali ne wajen ingantawa tare da samar da isassun kuɗaɗe don ƙarfafa wa jihohi 36 wajen samar da kula da lafiya a matakin farko mai aminci da inganci.   Sanarwar ta ce, “Jihar Zamfara ta sami kyautar Dalar Amurka 500,000 a matsayin wacce ta zama zakara a yankin Arewa maso Yamma wajen kula da cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko.   “Wannan karramawa da aka miƙa wa Gwamna Dauda Lawal, tallafi ne na haɗin gwiwa tsakanin ‘Bill and Melinda Gates Foundation, United Nations International Children’s Emergency Fund (UNICEF), Dangote Foundation da National Primary Healthcare Development Agency (NPHCDA).’   “Wannan karramawa, ta nuna a fili cewa ayyana dokar...
    Ministan Harkokin Wajen Iran ya bukaci Amurka da ta girmama al’ummar Iran da gwamnatin da ta zaba. Abbas Araghchi ya yi wadannan kalaman ne a ranar Asabar, a wata hira da ya yi da tashar talabijin ta Al Jazeera ta Qatar, a matsayin wani bangare na wani shiri da ke nazarin bangarorin yakin kwanaki 12 a watan Yuni, wanda kawancen Isra’ila da Amurka ya yi kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Ya sake nanata cewa al’ummar Iran ne kawai za su iya yanke shawara kan makomar kasarsu, yana mai shawartar Amurka da ta mutunta al’ummar Iran da kuma tsarin siyasa da ta zaba ta hanyar tsarin zabe na dimokuradiyya. Araghchi ya tuna da rashin amincewar da Iran ta dade tana yi...
    Wani dan bindiga ya kashe sojojin Amurka biyu da wani farar hula a yankin hamada na Palmyra a Syria. Kafofin yada labarai sun bayyana harin da na wani  dan bindiga daga kungiyar IS. An sanar da hakan a cikin wata sanarwa da rundunar sojin Amurka ta tsakiya (CENTCOM) ta fitar, inda ta kara da cewa an kashe dan bindigar. Shugaba Donald Trump ya yi alkawarin cewa Amurka za ta mayar da martani ga harin. Wani jami’in sojan Siriya, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce harbin ya faru ne a lokacin da jami’an Siriya da na Amurka ke taro a hedikwatar tsaron Siriya da ke Palmyra. Siriya ta yi ikirarin cewa sojojin kawancen kasa da kasa karkashin jagorancin Amurka...
    Jami’ar Brown a Amurka ta ba da rahoton mutuwar mutum biyu, tare da jikkatar guda tara dake cikin tsanani a harbin da aka yi a makarantar. An ruwaito cewa mutane da yawa sun jikkata a harbin da aka yi kusa da harabar Ivy League da ke Rhode Island. Hukumomi yankin sun bukaci jama’a da su ci gaba da kasancewa a kulle yayin da maharin ya tsere. “Zan iya tabbatar da cewa akwai mutane biyu da suka mutu da yammacin yau, kuma akwai wasu mutane takwas da ke cikin mawuyacin hali, kodayake basu cikin damuwa sosai,” in ji Magajin Garin Brett Smiley, a wani taron manema labarai. “Muna amfani da duk wata hanya da za mu iya don gano maharin in...
    Shugabannin kasashe mambobin kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) na taro a wannan Lahadi a Abuja, fadar mulkin Najeriya. Taron, zai ba da damar yin bitar batutuwan da ke ci gaba dake zaman karfa kafa wa kungiyar a hanlin yanzu. Juyin mulkin Guinea Bissau da yunkurin juyin mulkin soja a Benin, na daga cikin ajandar taron. Shugaban kungiyar na wannan karo kana kuma shugaban kasar Saliyo Julius Maada Bio ya yi tir da juyin mulkin na baya bayan nan. Batun janye sojoji kusan 200 na rundunar tsaro ta ECOWAS da aka tura Benin tun bayan yunkurin juyin mulkin a ranar 7 ga Disamba shi ma za’a tattauna a kansa. Taron zai kuma duba halin da ake ciki a...
    Juyin mulki, wani lamari ne da ya zama abun mamaki a shekarun baya amma a ‘yan shekarun nan, a iya cewa, ba abun mamaki ba ne domin ya zama tamkar ruwan dare musamman a Nahiyar Afirka.  Masoynmu masu bibiyarmu, me zai hana, mu tambayi kanmu, shin me ake nufi da juyin mulki kuma me ke kawo shi? Juyin mulki, shi ne ƙwace gwamnatin ƙasa ba zato ba tsammani kuma ba bisa ƙa’ida ba, wanda yawanci sojoji ko ƙungiya mai ƙarfi ke yi, ta hanyar amfani da ƙarfi ko barazana domin cire zaɓaɓɓun shugabanni. A wannan makon, alƙalaminmu zai karkata ne kan sharhi ga wannan muhimmin abu da ke barazana ga wanzuwar dimokuraɗiyya a yankin Afirka, duk da cewa, akwai dalilai...
    Kwamitin tsaron MDD ya gudanar da taron tattauna halin da ake ciki a Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo a jiya Jumma’a, inda ya mayar da hankali ga batun tabarbarewar yanayin tsaro a gabashin kasar, da kuma wa’adin aikin tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD dake kasar ko MONUSCO a nan gaba. A gun taron, wakilin Sin ya bukaci kungiyar ’yan tawaye ta Kongo, da ta gaggauta tsagaita bude wuta nan take, yana mai kira da a warware sabani ta hanyar tattaunawa ta gaskiya, da kuma soke takunkumi kan ayyukan MONUSCO, da kuma daidaita wa’adin aikin MONUSCO zuwa lokacin kyautatuwar yanayi a kasar, ta yadda za a tabbatar da amincin MONUSCO da kwamitin tsaron MDD. (Safiyah Ma) ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Ta Karbi...
    Kasar Sin ta karbi shaidu daga Rasha, dangane da tawagar aikin sojin kasar Japan mai lamba 731, rukunin da ya kware wajen amfani da kwayoyin cuta domin yaki, a yayin yakin duniya na biyu. A cewar hukumar koli ta tattara kayan tarihi, Sin ta samu kwafin bayanai, ciki har da takardun shari’u da aka yiwa dakaru membobin tawagar ta 731, da rahotannin bincike dangane da laifukan da tawagar ta tafka, da takardun musayar bayanan hukuma na tsohuwar tarayyar Soviet, tsakanin 11 ga watan Mayun shekarar 1939 zuwa ranar 25 ga watan Disamban 1950. Yayin yakin duniya na biyu, dakarun mamaya na kasar Japan, sun kafa wata cibiyar amfani da kwayoyin cuta domin yaki a sassa daban daban na Asiya, inda...
    Kasashen yankin sahel na AES, sun kimasa game da shirin kafa bankin da zai basu damar dogaro da kai. Shugaban kasar Mali kuma shugaban kungiyar kasashen Sahel (AES), Assimi Goïta, ya karbi tawagar ministoci kudi na kasashen kungiyar don kammala kafa Bankin na zuba Jari da Ci gaba da aka tsara don rage dogaro da kudi daga waje da kuma samar da ayyukan da ke da tasiri sosai. A lokacin wannan taron, an yi wa Shugaban kasar Mali bayani game da inda aka kwana game da shirin. Cibiyar za ta yi aiki a bangaren kudi da nufin karfafa ikon mallakar kasashen uku. Kasashen Mali, Nijar da Burkina Faso dukkansu wadanda suka raba gari da kasashen yamma musamman faransa wacce ta...
    Gidan Talbijin na Jihar Jigawa wato JTV, ya fara gudanar da gyare-gyaren doguwar eriyar yada shirye-shiryen tashar dake garin Andaza. Da yake yiwa shugaban gidan Talabijin na JTV Alhaji Abba Tukur karin bayani kan fara aikin, jagoran tawagar injiniyoyin, Injiniya Obi Onya, ya ce za su gudanar da aikin ta hanyar gano sassan doguwar eriyar da suke da matsala. Injiniya Onya ya bayyana cewar, haka kuma za su gudanar da irin wannan aikin a kananan tashoshin yada shirye-shiryen tashar dake garuruwa 3 na kananan hukumomi a Jihar. Yana mai cewar, garuruwan su ne Gumel da Hadejia da kuma Kazaure. Shugaban gidan talabijin din  wanda ya sami wakilcin Manajan Sashin injiniya na JTV, Malam Sha’aban Abubakar Tahir, ya...
    CGTN ta gabatar da kuri’un jin ra’ayin jama’ar ne ta harsunan Turancin Ingilishi, da Sifaniyanci, da Faransanci, da Larabci, da harshen Rasha. Inda masu bayyana ra’ayoyi 10,451 suka fayyace mahangarsu cikin sa’o’i 24. (Mai fassara: Saminu Alhassan) ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Damammakin Raya Tattalin Arziki Ga Duniya A Shekara Mai Zuwa December 13, 2025 Daga Birnin Sin Tsohon Jakadan Singapore A MDD Ya Jinjinawa Hangen Nesan Kasar Sin December 13, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Gudanar Da Taron Tunawa Da Kisan Kiyashin Nanjing December 13, 2025
    ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Tsohon Jakadan Singapore A MDD Ya Jinjinawa Hangen Nesan Kasar Sin December 13, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Gudanar Da Taron Tunawa Da Kisan Kiyashin Nanjing December 13, 2025 Daga Birnin Sin Kakakin Rasha: Kisan Kiyashin Nanjing Ya Nuna Zaluncin Ra’ayin Nuna Karfin Soja Na Japan December 12, 2025
    ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Damammakin Raya Tattalin Arziki Ga Duniya A Shekara Mai Zuwa December 13, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Gudanar Da Taron Tunawa Da Kisan Kiyashin Nanjing December 13, 2025 Daga Birnin Sin Kakakin Rasha: Kisan Kiyashin Nanjing Ya Nuna Zaluncin Ra’ayin Nuna Karfin Soja Na Japan December 12, 2025
    Cikin makwanni shida, dakarun na Japan sun hallaka Sinawa fararen hula, da sojoji da ba sa dauke da makamai kimanin 300,000, a wata ta’asa mafi muni da ta auku yayin yakin duniya na biyu. Memban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS Shi Taifeng, ya halarci taron tare da gabatar da jawabi. Cikin jawabin na sa, ya yi kira ga daukacin Sinawa da su zage-damtse wajen ingiza farfado da kasa, da bayar da gagarumar gudummawa ga ayyukan wanzar da zaman lafiya da ci gaban bil’adama. (Mai fassara: Saminu Alhassan) ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Damammakin Raya Tattalin Arziki Ga Duniya A Shekara Mai Zuwa December 13, 2025 Daga Birnin...
    Babban sakataren kungiyar gwgawarmayar musulunci ta Lebanon Sheikh Na’im Kassim ya bayyana cewa; Amurka ta kwana da sanin cewa, za mu kare kanmu, ko da sama da kasa za ta hade. Babban magatakardar kungiyar ta Hizbulllah Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce; Babu wanda ya isa ya kwace makaman Hizbullah saboda kare manufofin Isra’ila ko da kuwa duk duniya za ta shelanta yaki akan Lebanon. Sheikh Na’im Kassim ya kuma kara da cewa: Ku saurar da kyau ku fahimta! Kasa, da makami da rai, abu ne guda daya, don haka duk wanda yake son kwace abu daya, to dukkanin wadannan guda ukun yake son kwacewa.” Sheikh Na’im kassim ya kuma ce abinda kwace makamai yake nufi, shi ne shafe samuwarmu,...
    Jam’iyyar ADC ta zargi Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC) da amfani da siyasa wajen belin tsohon Ministan Shari’a na Tarayya, Abubakar Malami (SAN). Jam’iyyar ta ce babu wata shaida da ke nuna cewa Malami ya karya sharuɗan belin da aka ba shi. Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaran jam’iyyar na ƙasa, Bolaji Abdullahi, ya sanya wa hannu, ADC ta ce an ɗauki matakin ne jim kaɗan bayan Malami ya halarci wani taron siyasa a Jihar Kebbi. Jam’iyyar ta ce matakin da aka ɗauka ya nuna yadda aka ƙulla wani abu domin daƙile...
    Daga Usman Muhammad Zaria Majalisar Karamar Hukumar Birnin Kudu ta bada tabbacin hada hannu da bankin ajiya na Savings and Loan na Jihar Jigawa domin habaka tattalin arziki. Shugaban Karamar hukumar, Dr. Builder Muhammad Uba ya bada wannan tabbaci a lokacin da Manajan bankin, Babandi Isah Gumel ya kai masa ziyara. Builder Muhammad Uba ya ce karamar hukumar za ta ci gaba da mu’amulla da bankin wajen ganin ma’aikatan wucin gadi na bude asusun ajiya a bankin. Ya kuma bayyana farin cikinsa kan wannan ziyara da kuma karrama shi da aka yi. A jawabinsa, Manajan bankin Savings and Loan na Jihar Jigawa, Babandi Isa Gumel, ya ce sun karrama shugaban Karamar hukumar ne bisa daukar ma’aikatan wucin gadi a karamar...
    Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa, Alhaji Aminu Zakari, ya bukaci ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar  tabbatar da ganin cewa kananan hukumonin jihar 27 sun wallafa cikakken kundin kasafin kudadensu cikin zangon farko na sabuwar shekara. Alhaji Aminu Zakari wanda shi ne wakilin mazabar Gwiwa, ya bayyana haka ne lokacin tantance kiyasin kasafin kudin sabuwar shekara na ma’aikatar kananan hukumomi. Ya kuma yi kira ga ma’aikatar da ta duba batun rashin biyan albashi ga wasu daga cikin nadaddun kansiloli, kasancewar yanzu haka akwai nadaddun kansiloli 21 da ba sa samun albashin su. Ya kara da cewar, kwamitin ya samu koke kan tsallake albashin wasu ma’aikatan kananan hukumomi sakamakon aikin tantance ma’aikata na...
    Kungiyar ‘yan tawayen kasar DRC ta M23 ta kwace iko da wani gari mai muhimmanci bayan rushewar batun zaman lafiya A jiya Juma’a ne dai kasar Amurka ta zargi kasar Rwanda da cewa ta keta yarjejeniyar sulhu da zaman lafita da ta kulla da DRC, tare da cewa, abinda Kigalin take yi shi ne jefa yankin zuwa yaki. Mako daya da ya gabata ne dai aka kulla yarjejeniyar sulhu a tsakanin kasashen biyu wacce shugaban kasar Amurka Donald Trump ya bayyana cewa; Ta tarihi ce.” Tare da nuna fatan ganin an sami zaman lafiya a cikin wannan yankin wanda ya dade cikin fadace-fadace. Sai dai a ranar Larabar da ta gabata da yamma mayakan kungiyar M23 wacce Rwanda take goyawa...
    Shugaban Majalisar Shawarar musulunci ta Iran Muhammad Bakir Kalibaf wanda ya gana da takwaransa na kasar Habasha Tagseh Chapo ya bayyana cewa: Kasashen biyu da suke da alakar diplomasiyya ta tsawon shekaru 70, sun Shata hanyoyin bunkasa alakokin tattalin arziki, siyasa da al’adu. Haka nan kuma ya ce; kasantuwar kasashen biyu mambobi a cikin kungiyar Bricks yana kara dankon alakar da take tsakaninsu. Shugaban Majalisar shawarar musuluncin ta Iran Muhammad Bakir Kalibaf, ya kuma ce; A shekarar da ta gabata na kai ziyarar aiki zuwa Addib Ababa,mun gana da Mr. Tagseh Chapo, inda na gayyace shi ya kawo Ziyara Iran, kuma an yi wannan ziyarar ce dai a lokacin da kasashen biyu suke mambobi na kungiyar Bricks. Haka nan kuma...
    ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Abubuwan Da Ba Ku Ji Ba Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi December 13, 2025 Labarai Haɗin Kan Musulmai Da Kirista A Nijeriya Zai Kawo Saukin Matsalar Tsaro — Shehu Sani December 13, 2025 Manyan Labarai Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman December 13, 2025
    A gaban al’ummar kasarta, tawagar Morocco na da burin samun makoma irin ta Ibory Coast, wato nasara a gida amma ba tare da fargabar da ta fuskanta a zagayen farko ba. Amma karbar bakuncin gasar ba lallai ba ne ya zame riba ba. A cikin karo 34 da aka gudanar da gasar tun daga shekarar 1957 (ciki har da gasar farko), sau 12 ne kacal kasar da ta karbi bakuncin gasar ta yi nasara, wato kusan kashi 35% cikin dari. Tun daga 2000, Tunisia (2004), da Masar (2006) da Ibory Coast (2024) ne kawai suka yi nasara a gida. Kasar da ta fi fice a Afirka na da burin lashe kambu na takwas don kawar da bakin cikin kashin da...
    Da yake bayani dangane da jirgin sojan Nijeriya da kasar Burkino Faso ta kama, ya ce babu wani dalilin kama jirgin sojan Nijeriya, yana mai cewa duk wata kasa ta san cewa idan jirgi ya samu matsala yana iya yada zango a kasarta daga bisani idan aka gano matsalar sai ya tashi ya tafi. Akan hakan ya gargadi mahukunta kasar da su gaggauta sakin jirgin sojan Nijeriya ba tare da wani bata loka ci ba. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Abubuwan Da Ba Ku Ji Ba Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi December 13, 2025 Labarai Samarwa Sojoji Manyan Makamai Ne Mafita – Shugaban Ƙaramar Hukumar Bukuyum December 13, 2025 Manyan Labarai Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA...
    “An zabo Abubakar Dantsoho ne, daga cikin sauran wadanda aka karamma da lambar yabon bisa kokarin da yake ci gaba da yi, na bunkasa fannin sufurin Jiragen Ruwa na kasar wanda hakan ya sanya, aka kara samun fitar da kaya daga kasar nan, ta hanyar Tashoshin Jiragen Ruwa na kasa dIMODantsohoa tsarin NSW ta hanyar yin amfani da dabarar PCS domin janyo ra’ayin masu zuba jari daga ketare a Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar nan, da aka samar da kayan aiki na zamani, ” Inji sanarwar. “Akawi kuma batun kara daga darajar Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar a tsakanin hukumomin Jiragen Ruwa da ke a Afirka ta Yamma wato PMAWCA da kuma zabar Dantsoho, a matsayin mataimakin shugaban kungiyar masu...
    Sunana Hassana Yahaya Iyayi (Maman Noor) daga Jihar Kano: Laifi ai na iyayenta ne me ya sa basu yi bincike ba kafin azo wannan gabar. Ya kamata ace ana yin buncike kamar yadda a baya al’adar Malam bahushe ce buncike kafin Aure daga bangaren mijin har na matar. Wani yana gudun kar ya fadi aibin dansa ko ‘yarsa a karshe su rasa masu Aurensu, wanda hakan babbar matsala ce. Ka fadi gaskiya idan mutum ya ga zai iya to, shikenan in ba zai iya ba Allah ya kawo wani.   Sunana Khadija Auwal Koki, A Jihar Kano: Eh to, gaskiya laifin mijin ne da kuma danginsa tunda an san maganar aure ba wasa bace ya kamata ace an fadawa...
    Gwamnatin Jihar Kano ta fitar sanarwar umarnin haramta kafa wa, da  ɗaukar aiki da gudanar da duk wata ƙungiyar Hisbah mai zaman kanta a jihar, inda ta dakatar da ƙungiyar Independent Hisbah Fisabilillahi da tsohon gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ke shirin Ƙirƙirowa. Kwamishinan yaɗa labarai ne ya sanar da hakan a taron manema labarai a Kano, yana mai cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya rattaba hannu kan umarnin ne domin kare zaman lafiya da kuma kare sahihancin Hukumar Hisbah ta Jihar Kano da doka ta kafa. Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano Ƙirƙirar Hisbah Mai Zaman Kanta: Kungiyar Lauyoyi ‘Yan Kano Ta Shigar Da Tinubu Ƙara Umarnin ya bayyana cewa duk wani...
    Ya kara da cewa mutanen Batsari sun dade da wannan sana’a ta noman Rogo tun Iyaye da kakanni, wanda ya ce haka ta sanya ya baiwa hukumar bunkasa kanana da matsakaitun sana’o’i umarnin kafa masana’anta ta sarrafa Rogo a Batsari “Abin da muke gani shi ne, samar da wannan masana’anta zai kawo bunkasar tattalin arziki sannan ya rage asarar da manoma ke yi wajen samar da abinci sannan zai samar da ayyukan yi ga matasa tare da karfafa al’umma su kara shiga harkar noman Rogo” inji shi ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tattalin Arziki CBN Ya Tura Dala Miliyan 50 Don Ƙarfafa Kasuwar Musayar Kuɗaɗe November 28, 2025 Tattalin Arziki Masu Baje Koli 1,000 Za Su Baje Hajarsu A Kasuwar...
    “Dawo Nijeriya a cikin rukunin na C a kungiyar ta IMO hakan ya nuna irin zagewar kasar nan na iya tafiyar da tsare-tsare da bin ka’idojin gudanar da sufurin Jiragen Ruwa da wanzar da tsaro da kuma samar da kyakyawan yanayi, ga fannin,” Inji Dantsoho. “Wannan ci gaban, ba wai ga kasar nan ne kadai ba, har da ma ci gaban daukacin Afirka ta Yamma musamman a bangaren kara bunkasa ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa da ke a nahiyar da samar da hanyoyin kara habaka safarar kaya zuwa ketare da kuma kara bunkasa fannin tattalin arziki na teku'” A cewar shugaban. “Nijeriya a yau, ta kai wani babban mataki da duniya ke sauraronta a saboda haka, ina kara taya Nijeriya da...
    Dakarun Sojin Operation HADIN KAI sun daƙile wani hari da ’yan ta’addan ISWAP suka kai sansanin soji na Mairari da ke Jihar Borno. Harin ya fara ne daga daren ranar Juma’a zuwa safiyar Asabar. ’Yan sanda sun ba da tabbacin isasshen tsaro a zaɓen ƙananan hukumomin Borno Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEA A cewar rundunar, ’yan ta’addan sun yi ƙoƙarin shiga sansanin ta hanyar amfani da motoci biyu da suka cika su maƙil abubuwan fashewa. Jami’in yaɗa labarai na Operation HADIN KAI, Laftanar Kanal Sani Uba, ya ce sojoji sun gano motocin kuma suka tarwatsa su kafin su kai ga shiga sansanin. Rahotanni sun nuna cewa an kashe ’yan ta’adda da dama, yayin...
    Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Borno ta yi kira ga mazauna da su fito cikin kwanciyar hankali domin kada kuri’arsu a zaɓen ƙananan hukumomin da ake gudanarwa a yau Asabar. Tundunar ta tabbatar da cewa za a samar da isasshen tsaro a lokacin zaɓen da kuma bayan kammalawarsa. Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar, CP Naziru Abdulmajid, ya yi wannan kira ne a yayin wani taron tsaro mai muhimmanci da aka gudanar tare da ƙungiyoyi, kwamandojin tsaro, shugabannin sassa, da dukkan DPOs a faɗin jihar, kafin zaɓen ƙananan hukumomi da ake gudanarwa a yau Asabar, 13 ga Disamba, 2025. “Rundunar tana kira ga jama’a da su fito ba tare da wani shakka ba domin aiwatar da nauyin da ke kansu cikin...
    Jiragen yakin HKI sun kai hare-haren ta sama a yankunan kudancin labanon a ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da take yi da aka cimma tsakaninta da kungiyar Hizbullah a shekarar da ta gabata. Rikici ya kara Kamari ne bayan da isra’ila ta kai hari a makwanni biyu da suka wuce a kudancin labanon da yayi sanadiyar shahadar wani babban kwamnadan hizbullah mai suna Haytham Ali Tabataba’i. Wannan harin daya ne daga cikin shedun dake tababtar da keta harjejeniyar dakatar da bude wuta da aka cimma tsakanin isra’ila da hizbullah, adaidai lokacin da Amurka take ci gaba da goyon bayan isra’ila na neman jefa yankin cikin yaki. Jakadan Amurka a kasar labanon Michel issa ya fadi cewa...
    Adai dai lokacin da ke ta tattaunawa tsakanin Amurka da Indiya kan harkokin kasuwancin , sai ga shi a makon da ya wuce New Delhi ta karbi bakunci daya daga cikin manyan shuwagabannin dake kalubalantar gwamnatin Amurka akan nuna fin karfin a duniya. Shugaban kasar Rasha viladmir Putin ya kwashe kwanaki biyu a indiya  a wata ziyarar aiki da ya kai, kuma wannan yana zuwa ne adaidai lokacin da indiya ke fuskantar harajin da Amurka ta sanya mata na kashi 25 cikin 100  saboda ci gaba da siyan mai a hannun kasar Rasha , lamarin da ya kawo tarnaki a alakar dake tsakanin Delhi da kuma Washinton. Bugu da kari Amurka ta sanar da takunkumin ne a ranar 23 ga...
    Wani kwalekwale da ke ɗauke da fasinjoji takwas ya kife yayin da yake ƙetare kogin da ke kan iyaka da garin Gamboru na Najeriya da Fotokol a ƙasar Kamaru, inda mutane uku suka mutu. Lamarin ya faru ne da misalin qarfe 6:30 na yamma lokacin da kwalekwalen, wanda wani Mamman Nur Abbagana na Kasuwan Katako, Gamboru ke tuƙa shi ya kife a tsakiyar ruwa tare da jefa dukkan fasinjoji cikin ruwa. Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa dukkan fasinjoji takwas ’yan ƙasar Chadi ne da ke tafiya daga Jos, Jihar Filato, a kan hanyarsu ta zuwa N’Djamena, Jamhuriyar Chadi. An ceto fasinjoji biyar, waɗanda aka tabbatar da suna raye ba su mutu ba. Yadda za ku cike neman aikin jami’an...
    Rahotanni sun nuna cewa Amurka ta kakaba sabbin takunkumi kan bangaren manfetur na kasar Venuzwela da kuma iyalan shugaban kasar Nicolas Maduro da hakan ya shafi tattalin arziki, siyasa da kuma kara matsin lamba kan gwamnatin carakas. Tattalin arzikin venuzuwela ya doru ne kan man fetur don haka sabon takunkumin kai tsaye zai cutar da gwamnatin maduro ne da kudaden shigarta na asali suna fitowa ne daga man fetur, gwamnatin Amurka ta sanar da sanya sabbin takunkumi kan bangaren man fetur din kasar Venuzuwel da kuma wasu mutane Ukku yan uwan matar Moduro, Jaridar new york times ta fitar da rahoton cewa takunkumin na Amurka ya tilastawa gwamnatin moduro sayar da manfetur ta barauniyar hanya  ta hanyoyin masu shiga tsakani...
    Rahotanni sun bayyana cewa kungiyar Hamas ta fadi cewa fashewar bama-bama da rushewar gidaje da mutuwar mutane da dama a daidai lokacin da ake tsananin ruwan sama da sanyi a yankin gaza ya kara tabbatar da kisan kiyashi isra’ila kan alummar Gaza, kuma ya kara tabbatar da gazawar tsarin duniya na daukar mataki don dakatar da ita. Hamas ta ce isra’ila ce ke da alhakin duk wani bala’i da ake ciki a gaza, kuma ta soki kasashen duniya na yi gum da baki game da abubuwan dake faruwa ,don haka tana kira da a dauki matakin gaggawa domin janye killacewar da Isra’ila ta yi wa yankin don bada dama a shigar da kayayyakin agaji da kuma fara sake gina yankin....
    Rahotanni daga nijeriya sun nuna cewa Matatar Mai ta Dangote ta rage farashin fetur daga Naira 828 zuwa Naira 699 a lita. Bayanai sun nuna cewar matatar man ta rage Naira 129 Wani jami’in matatar ya ce sabon farashin ya fara aiki ne daga ranar 11 ga watan Disamba, 2025, wanda hakan ya zama karo na 20 da matatar ta ke rage farashin man fetur a bana. Ragin na zuwa ne bayan kwana kadan da shugaban kamfanin, Aliko Dangote, ya yi alkawarin ci gaba da sanyawa a sayar da fetur din a farashi mai rahusa yayin da matatar ke kara samar tare da yin gogayya da man da ake shigowa da shi daga waje. Bayan wannan sauyi, wasu manyan wuraren...
    Allah Ya yi wa Farfesa Adamu Baikie, wanda ya kasance Farfesa na farko a fannin Ilimi daga Arewacin Najeriya, rasuwa. Farfesa Adamu Bakie ya rasu yana da shekaru 94 ne a daren Jumma’a a gidansa da ke Zariya, Jihar Kaduna. Babban ɗansa, Manjo Muhammad Adamu (Ritaya), ya tabbatar da rasuwar, inda ya ce za a sanar da jama’a cikakkun bayanai da lokacin da za a gudanar da jana’izarsa daga baya. Baikie ya shahara sosai wajen gina fannin ilimi a Najeriya, inda ya yi aiki a manyan makarantu da dama. Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEA Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta Ya taɓa zama Shugaban Jami’a a wasu jami’o’in Najeriya, kuma...
    Babban Kotun Tarayya da ke Abuja ta sanya ranar 26 ga Fabrairu, 2026 domin yanke hukunci a shari’ar da Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA) ta shigar kan DCP Abba Kyari, wanda aka dakatar. NDLEA na tuhumar Abba Kyari, tsohon Shugaban Rundunar ’Yan Sanda Masu Yaƙi da Garkuwa d a Mutane (IRT), tare da ’yan uwansa biyu kan zargin rashin bayyana kadarorinsu. A ranar Juma’a Mai shari’a James Omotosho ya sanya ranar, bayan lauyoyin NDLEA, Sunday Joseph; lauyan Abba Kyari, Onyechi Ikpeazu, SAN; da lauyan ’yan uwansa, Monjok Agom, sun gabatar da hujjoji da muhawara kan tuhumar. A cikin tuhumar da ta ƙunshi laifuffuka 23, NDLEA ta ce ta gano kadarori 14, ciki har da manyan shaguna,...
    Shugaba Masoud Pezeshkian ya bayyana kudurin Iran na aiwatar da yarjejeniya hadin gwiwa da Rasha a wani taro da takwaransa na Rasha Vladimir Putin. Pezeshkian ya yi wannan furuci ne a ranar Juma’a a gefen taron kasa da kasa kan zaman lafiya da amana a babban birnin Turkmenistan na Ashgabat. Shugaban Iran ya bayyana gamsuwarsa da habaka dangantakar Tehran da Moscow kuma ya yaba da goyon bayan Rasha ga Jamhuriyar Musulunci a cikin tarukan kasa da kasa. Da yake magana game da yarjejeniyar hadin gwiwa da Iran da Rasha suka sanya wa hannu a ranar 17 ga Janairu, 2025, inda ya ce, “Mun kuduri aniyar aiwatar da yarjejeniyar.” A nasa bangare shugaba Putin, a nasa bangaren, ya ce dangantakar Rasha...
    Majalisar Dinkin Duniya ta amince da wani daftarin kuduri da ke neman Isra’ila ta bada damar shigar da agajin jin kai ba tare da wani sharadi ba zuwa Zirin Gaza. Kudurin da aka zartar a ranar Juma’a, ya yi kira ga Isra’ila da ta kare cibiyoyin Majalisar Dinkin Duniya tare da bin dokokin kasa da kasa. An gabatar da wannan matakin ne a matsayin martani ga ra’ayin da Kotun Duniya ta ICJ, ta bayar ga Isra’ila. Yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma a tsakanin kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas da Isra’ila, wacce ta fara aiki a ranar 10 ga Oktoba, 2025, ta wajabta wa Isra’ila bude iyakoki domin ba da damar shigar da abinci, mai, da kayayyakin jin kai ba...
    Gwamnatin Jamhuriyar Benin, ta fitar da sammacin kame dan fafatukar nan Kemi Seba da ya shahawa wajen kalubalantar siyasar faransa a kasashen Afrika. Matakin dai an zuwa ne kasa da mako guda bayan yunkurin juyin mulki da aka yi wa Shugaba Patrice Talon, wanda ya girgizar kasar. Kotun Jamhuriyar Benin ta bayar da sammacin kama, Kemi Seba da Sabi Sira Korogone, shugaban kungiyar ‘Yantar da Jama’a (MPL), bisa zargin goyan bayan ayyukan ta’addanci” da kuma “tunzura mutane su yi bore.” Mutanen biyu za su iya fuskantar hukuncin daurin shekaru biyu zuwa biyar a gidan yari da kuma tarar miliyan goma na CFA, a cewar wata majiyar shari’a. Shi dai Kemi Seba, ya fitar wani bidiyo a ranar 7 ga Disamba...
    Daga Usman Muhammad Zaria  Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da naira biliyan 2.6 domin gudanar da ayyukan Hajjin shekarar 2026. Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta Jiha da aka gudanar a gidan gwamnati da ke Dutse, babban birnin jihar. A cewarsa, majalisar ta amince da kashe sama da naira biliyan 2 da miliyan 651 domin ayyukan Hajjin 2026, biyo bayan gabatar da bukatar da Sakataren Gwamnatin Jihar (SSG) ya yi. Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce za a yi amfani da kudaden ne a bangarorin sufuri da jijigilaAlhazai, jin dadinsu, ayyukan lafiya da kuma shirye-shiryen gudanarwa. Sauran bangarorin...
    Gwamnatin Jihar Kano, ta haramta kafa Hukumar Hisbah mai zaman kanta tana, wadda tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje, yake ƙoƙarin kafawa. Gwamnatin ta ce kafa hukumar ya saɓa da doka, kuma zai iya zama barazana ga zaman lafiya a jihar. Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago A cikin wata takarda da Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya sanya hannu a ranar 8 ga watan Disamba, 2025, gwamnatin ta ce ta gano an fara ɗaukar mutane aiki a hukumar ba tare da neman izini ba. Gwamnatin ta ce hakan ya saɓa wa Dokar Hukumar Hisbah ta Jihar Kano. Da yake zantawa da ’yan jarida,...
    Daga Usman Muhammad Zaria  Aikin rigakafin watan Disamba a karamar hukumar Sule-Tankarkar ta jihar Jigawa ya samu gagarumar nasara, yayin da iyaye suka fito kwansu da kwarkwata domin tabbatar da cewa an yi wa ’ya’yansu cikakken rigakafi. Wasu daga cikin iyayen da suka kawo ’ya’yansu domin karbar rigakafin yau da kullum da na shan inna sun bayyana jin dadinsu kan yadda aka gudanar da aikin cikin kwanciyar hankali.   Daya daga cikinsu, Malama Ummahani Danbala, ta ce an wayar da kan jama’a sosai ta hannun mata ’yan sa-kai a unguwarsu, inda aka karfafa gwiwar iyaye mata su kawo ’ya’yansu domin karbar rigakafin yau da kullum da na shan inna. Malam Yunusa, wani mai sa ido a karamar hukumar, ya...
    Daga Usman Muhammad Zaria  Ma’aikatar ilimi matakin farko ta jihar Jigawa ta ce za ta kashe fiye da naira miliyan dubu 18 domin gudanar da harkokinta a sabuwar shekara. Kwamishinan ma’aikatar, Dr. Lawal Yunusa Danzomo ne ya bayyana haka lokacin da yake kare kiyasin kasafin kudin 2026 a gaban kwamatin ilimi matakin farko na majalisar dokokin jihar Jigawa. Dr. Lawan Yunusa Danzomo ya ce zasu mayar da hankali ga aikin gina ajujuwa da gyaran wadanda suka lalace. Za kuma a samar da littatafan darussa da tebura da kujeru domin inganta harkokin koyo da koyarwa. Hakazalika za a  gina bandakuna da samar da ruwan sha da wutar lantarki da tsaro. Danzomo, ya ce aiwatar da haka zai yi matukar tabbatar da...
    Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta yi kiyasin kashe naira miliyan dubu 3 domin gudanar da aikace-aikacenta a lokacin aikin Hajjin 2026. Shugaban hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka lokacin da ya ke kare kiyasin kasafin kudin sabuwar shekara a gaban kwamatin harkokin addini na majalisar dokokin jihar Jigawa. Alhaji Ahmed Umar Labbo yace hukumar za ta sayi motar daukar marasa lafia wato ambulance domin dawainiya da mahajjatan da za su gamu da rashin lafiya a lokacin hajji a kasa mai tsarki. Yana mai bayyana cewar za a yi amfani da wasu daga cikin kudaden wajen kaiwa da komowa yayin aikin hajji. Sai kama masauki ga ma’aikatan hukumar da ma’aikatan...
    Mai horar da Ƙungiyyar Ƙwallon Ƙafa ta Liverpool, Arne Slot ya ce zai sanya Mohammed Salah cikin jerin ’yan wasan da za su bugawa Liverpool wasa da Brighton a ranar Asabar. Slot wanda ya samu saɓani da Salah kan ajiye shi a benci a wasanni uku a jere, ya ce yana da yaƙinin cewa, Salah zai ci gaba da bugawa ƙungiyar wasa. 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya Ya kuma ƙara da cewa, zai ci gaba da tattaunawa da ɗan wasan domin ya ci gaba da taka leda a Anfield. Salah mai shekara 33, baya cikin jerin ‘yan wasan da suka doke Inter Milan a Italiya...
    Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanninta a Jihar Gombe, inda ta jaddada muhimmancin haɗin kai da farfado da jam’iyyar tun daga matakin ƙananan hukumomi zuwa jiha gabanin zaɓen 2027. Taron ya halarta bayan zuwan wakilai daga dukkanin ƙananan hukumomin jihar. Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno Mambobin jam’iyyar sun yaba da yadda komai ya gudana cikin lumana da tsari, abin da suka ce alama ce ta daidaito a cikin jam’iyyar. Elder Ambrose Ismail Mairungu ne, ya zama sabon shugaban NNPP na jihar, yayin da Yakubu Adamu Tela, ya zama mataimakinsa. Abdullahi Ali Mohammed, ya samu kujerar sakataren jiha, sannan Hon. Amatiga Yila Naboth (ACG)...
    Sakatare Janar na majalisar dinkin duniya Antonio Guterres, ya ce za su gana da bangarorin da ke rikici da juna a Sudan a birnin Geneva, sai dai shugaban bai bayyana  ranar da za a yi wannan tattaunawar ba. Guterres ya bayyana hakan ne a lokacin zantawarsa da kafar talabijin ta Al Arabiya da ke Saudiyya wadda ta tattauna da shi game da yunkurin da majalisar ke yi ba ganin an sasanta rikicin na Sudan. Sai dai Tattaunawar na zuwa ne a dai dai lokacin da mayakan RSF ke ci gaba da kwace yankuna a cikin kasar tare da kisan fararen hula da dama, da kuma tilastawa miliyoyin barin matsugunansu. Tun a tsakiyar watan Afrilun shekarar 2023 ne yaki ya barke...
    Babban mai shigar da kara a kuntun duniya mai hukumta manyan laifuka Karim Khan ya fadi cewa gwamnatin Birtaniya ta yi barazanar yanke tallafin da take bawa kotun da kuma ficewa daga matsayin dake taimakawa wajen samun tallafi, idan kotun ta ci gaba da tafiya da sammacin da ta fitar na kama prime ministan israila banjamin Natanyahu Khan yayi watsi da kiran da aka yi masa na ya jinkirta, yace babu wasu alamu dake nuna cewa isra’ila za ta bawa kotun ICC hadin kai ko kuma canza halayyarta a yankin Gaza, bayan da tel aviv ta fara musanta kisan kare dangi da ta yi a yankin gaza a watan oktoban shekara ta 2023 Sai dai fayel din da khan ya...
    Shugaban kasar Iran Masud pezeshkiyan a wajen taron zaman  lafiya na turkmanistan ya bayyana cewa siyasar kasashe masu karfin fada aji a yammacin Asiya ne suka bawa isra’ila wata dama ta musamman  ta kai hare-hare gaba gadi, da hakan ya bata damar kai harin soji kan kasashen yankin ciki har da kasar iran ba tare da fuskantar wani sakamako ba. Har ila yau shugaba peszeshkiyan da yake bayani a wajen taron zaman lafiya a garin Ashgabat na kasar Turkministan ya kara da cewa harin da Isra’ila ta kai wa iran a watan yuni da  ya kai ga shahadar mutane da dama da basu san hawa ba balle sauka ya samu kyakkawar tarba ne ma mai makon yin Allah wadai Yace...
    Rahotanni sun bayyana cewa shugaban kasar Iran Mas’ud pezeshkiyan ya jaddada game da mihummanci sanya hannun jari da kuma hadin guiwa a iyakoki, a matsayin abubuwan da ya fi mayar da hanakli akai a lokacin ganawarsa da shugaban kasar iraki Abdul latif rashid a gefen taron kasa da kasa na zaman lafiya a kasar Turkmenistan Tehran da Bagadaza sun dauki hadin guiwa a matsayin babban ginshikin zaman lafiya a yankin da kuma kariya daga tsangwama daga kasashen ketare  musamman Amurka da Isra’ila wadanda ke neman raba kan kasashen musulmi da kuma kawo cikas ga hadin guiwar tattalin arziki da siysa. Ana shi bangaren shugaban kasar Iraqi ya fadi cewa iran itace makwabciya mafi muhimmanci don muna da alakar tsaro mai...
    Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƙasa (NLC) a najeriya ta bayyana cewa za ta gudanar da zanga-zangar kasa baki ɗaya a ranar 17 ga Disamba, 2025, domin nuna damuwarta kan taɓarɓarewar tsaro a Nijeriya. Wannan sanarwa ta fito ne daga sakon da NLC ta aikawa dukkanin majalisun jihohi a ranar 10 ga Disamba, bayan taron NEC da ta gudanar a ranar 4 ga watan. Kungiyar ta nuna damuwarta kan karuwar hare-haren ƴan bindiga  da satar mutane da ke ci gaba da addabar al’umma. NLC ta mayar da hankali musamman kan sace ɗalibai mata a wata makarantar kwana da ke Jihar Kebbi a ranar 17 ga Nuwamba, inda ta bayyana mamaki cewa an janye jami’an tsaro daga makarantar kafin harin. Ta ce wannan...
    Ɗan wasan gaban Ƙungiyyar Ƙwallon Ƙafa ta Galatasaray ɗan asalin Najeriya, Victor Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasa na bana, a bikin bayar da kyaututtuka ta GQ Türkiye na maza na 2025. Ɗan wasan mai shekara 26 ya sami kyautar mafi girma a bikin da aka gudanar mai ban sha’awa. Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699 Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai Ya sami kyautar ne saboda rawar da ya taka a Galatasaray a kakar wasa ta bara, inda ya zura ƙwallaye 37 kuma ya taimaka wajen zura ƙwallo sau bakwai a wasanni 41, wanda hakan ya sa Galatasaray ta lashe gasar Turkiya. Osimhen ya karya tarihin Galatasaray na zama ɗan wasan da ya...
    Matatar man Dangote ta sake rage farashin man fetur ɗin da take sayar da man, inda ta rage farashin man fetur ɗin daga Naira 828 zuwa Naira 699 kan kowace lita. Bayanan farashin da aka wallafa a shafin  kasuwancin farashin man fetur a Petroleumprice.ng a ranar Juma’a sun nuna cewa matatar ta aiwatar da wani bita na baya-bayan nan, inda ta rage farashin man da N129 a kowace lita – ragin kashi 15.58 cikin 100. Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a Katsina Wani jami’in matatar man da ya zanta da manema labarai bisa sharaɗin sakaya sunansa saboda ba shi da izinin yin tsokaci a bainar jama’a, shi ma...
    Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin Shirin na duniyarmu a yau shiri wanda yake kawo maku labarai masu muhimmanci a makon da ya gabata, wadanda suka shafi siyasa tattalin arziki zamantakewa tsaro da sauransu. Sannan daga karshe idan akwai lokaci mu ji ra’ayin masana dangane da su. Da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu. ///…Madallah, masu sauraro labarimmu na farko a wannan Shirin shi ne, dangane da furucin jakadan Amurka na musamman a kasar Tom Barrack wanda ya bayyana ‘shirin Amurka na 5’ dangane da siyasar Amurka a kan kasar Iran ya wargaje bayan rashin nasarar da ta fuskanta a yankin kwanaki 12 na watan yunin da ya gabata. Kamfanin dillancin...
    A ci gaba da al’adar fiye da shekaru 30, Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi ya ziyarci kasashen Afirka da dama a tsakanin 5-11 ga watan Janairun 2025 don sake tabbatar da dangantakar diflomasiyya da kuma binciko sabbin hanyoyin hadin gwiwa. Wannan ziyarar ta sake tabbatar da manufar ci gaba da cin moriyar juna a tsakanin bangarorin biyu.   Baje kolin tattalin arziki da ciniki na Sin da Afirka na hudu a Changsha An gudanar da wannan taron baje kolin na hudu daga 12 zuwa 15 ga watan Yunin bana a Changsha, babban birnin lardin Hunan. Baje kolin ya tattaro kusan kamfanonin Sin da Afirka 4,700, kuma an baje kolin kayayyakin Afirka sama da 800 daga kasashe da dama....
    Dakarun Sojin Operation Whirl Stroke (OPWS), sun kashe wasu mutum uku da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, yayin wani samame da suka kai a Ƙaramar Hukumar Ukum, a Jihar Binuwai. Mai magana da yawun OPWS, Laftanar Ahmad Zubairu, ya ce sojojin sun samu bayanan sirri kuma suka yi aiki tare da ’yan sandan Zaki-Biam. Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a Katsina Maharan sun kafa shinge a kan hanyar Aturuku–Wembe–Ayati, inda suke tare matafiya suna ƙwace musu kayayyaki. Da sojoji suka isa wajen, maharan sai suka fara harbe-harbe, wanda hakan ya sa sojojin suka buɗe musu wuta. Hakan ya yi sanadin mutuwar uku...
    ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Hukuncin Kisa Kan Maryam Sanda December 12, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja December 12, 2025 Manyan Labarai NLC Ta Shirya Zanga-Zangar Rashin Tsaro A Faɗin Ƙasa Ranar 17 Ga Disamba December 12, 2025
    Alkalin ya kuma bayyana cewa ba daidai ba ne bangaren zartarwa ya yi rangwame ga hukuncin kisa yayin da har yanzu ana da karar daukaka kara a gaban kotu. Don haka, kotun ta kori daukaka karar Maryam Sanda gaba ɗaya tare da tabbatar da hukuncin kisa da kotunan ƙasa suka yanke mata. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja December 12, 2025 Manyan Labarai NLC Ta Shirya Zanga-Zangar Rashin Tsaro A Faɗin Ƙasa Ranar 17 Ga Disamba December 12, 2025 Manyan Labarai Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP December 12, 2025
    “Umarna ga jami’an tsaro har yanzu ita ce cewa dole ne a ceto dukkan daliban da sauran ‘yan Nijeriya da aka yi garkuwa da su a fadin kasar nan, a dawo da su gida cikin aminci. Dole ne mu tabbatar da an kirga duk wanda lamarin ya rutsa da shi. “Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da aiki tare da Jihar Neja da sauran jihohi don tsare makarantu da kuma samar da ingantacciyar muhalli mai aminci da dacewa domin karatun ‘ya’yanmu. “Daga yanzu, jami’an tsaro tare da gwamnonin jihohi dole su hana afkuwar garkuwa da mutane a nan gaba. Ya kamata yaranmu su daina zama abin hari ga mugayen ‘yan ta’adda da ke kokarin dakile iliminsu tare da jefa su...
    Kotun Kolin Najeriya ta soke afuwar da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya yi wa Maryam Sanda, inda ta ce shugaban ya wuce makadi da rawa ta hanyar yin afuwa ga wacce har yanzu kararta ke gaban kotu. A hukuncin da aka yanke ranar Juma’a, kotun ta yanke hukunci da rinjayen alƙalai huɗu cikin biyar, inda ta tabbatar da hukuncin kisa da Babban Kotun Abuja ta yanke, kuma Kotun Daukaka Kara ta tabbatar. ‘Haduwata da masu garkuwa da ɗan uwana a dajin Zamfara’ Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa An yanke wa Sanda hukunci ne a shekarar 2020 bisa laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello, a lokacin rikicin cikin gida a gidansu da ke Abuja. Kotun ta yi watsi...
    Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƙasa (NLC) ta bayyana cewa za ta gudanar da zanga-zangar ƙasa baki ɗaya a ranar 17 ga Disamba, 2025, domin nuna damuwarta kan taɓarɓarewar tsaro a Nijeriya. Wannan sanarwa ta fito ne daga saƙon da NLC ta aikawa dukkanin majalisun jihohi a ranar 10 ga Disamba, bayan taron NEC da ta gudanar a ranar 4 ga watan. Kungiyar ta nuna baƙin ciki kan ƙaruwar hare-haren ƴan daba da satar mutane da ke ci gaba da addabar al’umma. NLC ta mayar da hankali musamman kan sace ɗalibai mata a wata makarantar kwana da ke Jihar Kebbi a ranar 17 ga Nuwamba, inda ta bayyana mamaki cewa an janye jami’an tsaro daga makarantar kafin harin. Ta ce wannan lamari...
    Wani mazaunin Kano, Namadi Bawa, ya bayyana yadda ya shiga cikin daji a Jihar Zamfara domin kai kudin fansa ga ’yan bindiga da suka sace ɗan uwansa, inda ya tarar da su cikin mawuyacin hali na rashin lafiya, kafin daga bisani ya samu ya kubutar da shi. A tattaunawar mutumin da Aminiya, y ace an sace ɗan uwan nasa ne a Gusau babban birnin jihar Zamfara, a kan hanyarsa ta dawowa daga Sakkwato.A cewar Namadi, ɗan uwansa ya ci karo da shingen da ya yi kama da na jami’an tsaro a hanya, sai dai daga baya aka gano ’yan bindiga ne suka yi masa kwantan bauna tare da wasu fasinjoji. “Sun kira ni suka tambaya ko na san ɗan uwana,...
    Shugaban kasar Iran Masoud Pazeshkian, a ganawarsa da tokwaransa na kasar Turkmenietan Gurbanguly Berdimuhammedow a birnin Ashg’abat ya ce, a halin yanzu, fiye da duk wani lokaci – tana bukatar amintaccen madogara, zaman lafiya da kuma hadin kai. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto shugaban yana yabawa kasar Turkmenistan kan shirinta karban bakwancin taro dangane da hadin kai da kuma amintaccen madogara da kuma zaman lafiya nan gama a birnin Ashg’abad . A zantawar shuwagabannin kasashen biyu sun bukaci karfafa diblomasiyya tsakanin kasashen biyu, da tattaunawa tsakanin kasashen yankin a kan duk wani al-amari da ya taso a tsakaninsu. Shugaban Pezeshkian ya ce, wannan shi ne abinda duniya ta rasa kuma take bukata a yau. Dole ne...
    Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026” Masana a Taron Abuja na Tattaunawa kan Tattalin Arziki Kasa da ake wa lakabi da Abuja Economic Dialogue 2025 da Kamfanin Ignite Capital ke shiryawa duk shekara da haxin gwiwar Kamfanin Innovision Global Consulting sun yi hasashen cewa, za a samu saukar kayan masarufi da Karuwar samar da ayyukan yi a faxin kasa a shekara mai zuwa ta 2026. Masana tattalin arzikin da suka yi fashin baki kan yadda tattalin arzikin Nijeriya ke tafiya a cikin watanni tara da suka gabata, a taro sun haxa da Dakta Paul Arinze, Shugaban Kamfanin Bincike da Nazari kan harkokin tattalin arziki mai suna Pedestal Africa da Dakta...
    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’il Baqai ya bada sanarwan cewa Tehran zata dauki bakoncin wasu kasashen yankin don tattaunawa dangane da harkokin tsaro a kasashen yankin musamman tsakanin Afganisatan da Pakistan. Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Baghae na fadar haka a safiyar yau Jumma’a ya kuma kara da cewa kafin haka kasashen Qatar, Turkiya da Saudiya sun yi kokarin sasanta kasashen Afganistan da Pakisatan dangane da rikice-rikicen da ke aukuwa tsakanin kasashen biyu a cikin yan watannin da suka gabata. Ya ce gwamnatin kasar Iran tana son ganin an kawo karshen duk wata rigima tsakanin kasashen yankin saboda tana shafar al-amura da dama a yankin. Labarin ya kara da cewa taron wanda za’a gudanar...
    Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bada sanarwan cewa ya amince ya ziyarci birninBeirut babban birnin kasar Lebanon tare da gayyatar tokwaransa na kasar Lebanon Yusuf Rajji, kuma kwana guda bayanda da Rajji ya ki amincewa ya zo tehran don tattaunawa tsakanin kasashen biyu. Shafin yanar gizo na labarai ‘The National’ ta kasar Amurka ya ce Rajji ya bayyana halin da ake ciki a kasarsa a matsayin dalilin da zai hana shi zuwa Tehran. Ya kuma bada shawarar su hadu da Aragchi a wata kasa don tattaunawa kai tsaye kan shirin gwamnatin kasar na kwance damarar kungiyar Hizbullah. Aragchi ya ce ya fahinci cewa HKI ce ta hana Rajji zuwa Tehran, amma shi zai je birnir Beirut don...
    Shugaban hukumar makamashin Nukliya na kasar Iran Mohammad Islami ya bayyana cewa, kasar zata ci gaba a fannonin ilmi guda 6 na fasahar nukliya wato Fission, Fussion, Lasers, fasahar Quantum, da kuma Plasma duk tare da barazanar yaki, ko na siyasa ko kuma yakin kwakwalwan da makiya suke wa kasar. Yace, matsayin  JMI a bayyana yake, kan cewa ba zata daina aikin ci gaba a fannonin ilmin makamashin nukliya don samun ci gaba a bangarorin kiwon lafiya da magunguna ba da wasu bangarorin ci gaba ba. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Islami yana fadar haka, a wani bukin kaddamar wasu sabbin kayakin aikin wadanda aka samar a cikin gida wadanda suka hada da ‘Plasma-Based drug synthesis...
    PDP wanda ke da gwamnonin 11 bayan zaben 2023, yanzu tana da biyar kawai tare da karin wasu suna nuna suna son barin jam’iyyar. Yawancin gwamnonin da suka sauya sheka a cikin wannan lokaci sun koma APC, yayin da jam’iyyar Accord ta samu guda daya. Gwamnonin da suka bar PDP zuwa APC su ne Umoh Eno na Akwa Ibom da Sheriff Oborebwori na Delta da Douye Diri na Bayelsa da Peter Mbah na Jihar inugu. Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas, ya dade yana son barin PDP kuma yanzu yana jiran lokaci mai ya yi ne ya shiga APC. Akwai fargaba cewa gwamnonin Caleb Muftwang na Jihar Filato da gwamnan Zamfara, Dauda Lawal ma na iya canza sheka. Gwamnonin PDP kadai...
      A Legas farashin shinkafa ya fadi sosai A kasuwannin Mushin da Daleko, farashin buhun shinkafa kilo 50 da ake sayar da shi a da Naira N75,000 cikin Nuwamba, a yanzu ya dawo Naira 54,000.   Jihar Delta A Jihar Delta, musamman a Asaba, farashin kayan abinci ya daidaita a manyan kasuwanni irin su Kasuwar Oko (Hausa), Midwifery Market da Ogbogonogo Market, sai dai a kasuwannin mako-mako na kauyuka. Bincike a babban birnin jihar ya nuna cewa farashin muhimman kayan abinci ya dan daidaita, amma ‘yan kasuwa da masu sayayya sun nuna damuwa kan karancin kudin da ake da shi don sayayya. Kwandon tumatir da ake sayarwa Naira 5,000 a wasu watanni da suka gabata, yanzu ya sakko Naira 4,000....
    Wata rana, Abu Huraira (RA) yunwa ta kama shi matuka, har yazu wurin mimbarin Annabi SAW da ke cikin masallacin Annabi, sai ya fadi a wurin, duk wadanda suka zo wurin suka ganshi, sai suce Allah Sarki, wane ba shi da lafiya har sai da Annabi ya zo ya ganshi, sai yace masa, Abu Hurairah kana jin yunwa ko? Sai ya amsa da eh. Take Annabi SAW ya ce masa, biyo ni zuwa daki na. Annabi yasa aka kawo masa nono a dan koko kamar yadda aka saba, Abu Hurairah yana jira a ce masa ya sha, sai Annabi SAW ya ce masa ya kira ‘yan uwansa Ahlul suffati, kuma jama’a ne masu yawa, da isowarsu, Annabi SAW ya sa...
    Da yake zantawa sa wakilinmu jim kadan bayan Kamala atisayen, mataimakin Babban Kwamandan Hukumar Tsaron Daji na kasa (NFSS) mai kula da Ayyuka, Manjo Muhammad Abubakar Abdullahi mai nurabus, ya ce hukumar na kara samun kaimi wajen amfani da sabbin dabaru da tsare-tsare don kare dazukan kasar. DCG Mohammed, ya bayyana suna gudanar da irin wannan atisayen musamman duk karshen shekara na Arewa maso yamma bisa umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na samar da ingantaccen tsaro a dazukan Nijeriya. Ya bayyana cewa NFSS za ta ci gaba da tallafa wa hukumomin tsaro domin lalata maboyar ’yan bindiga da sauran miyagu da ke cikin dazukan kasar. DCG Mohammed ya bayyana cewa bayan kammala atisayen, za a tura dakaru daban-daban zuwa muhimman...
    Hukumar zaben kasar Habasha ta sanar da cewa za a yi manyan zabukan kasar a ranar 1 ga watan Yuni na 2026. Shugabar hukumar zaben kasar ta Habasha Melatwork Hailu ta fada wa kafafen watsa labarun kasar cewa; Ana gudanar da ayyukan ne a yanzu domin tsara wuraren da za a yi zabukan da samar da rumfunan zabe a cikin rassan da za a kada kuri’a.” Har ila yau shugabar hukumar zaben kasar ta Habasha ta ce, jam’iyyun siyasar kasar sun sami horon da ya dace domin bayyana da tallata manufofinsu ga jama’ar kasar.  Sai dai yin zabe a kasar ta Habasha yana fuskantar kalubale mai yawa. Kasar dai ba ta dade da fitowa daga yakin basasa ba wanda aka...
    A nan za mu iya cewa, wannan zunzurutun kudaden da za su tara har Naira biliyan 19 a wata daya, ya zama wajibi alummar yankin su sauya, na dakile matsalar domin kuwa, ‘yan Nijeriya, sun gaji batun ana tara dimbin kudade, domin magance wata matsala a kasar, amma daga, a karkatar da su, zuwa wata sabga, ta da ban. Kazalika, batun ba wai kawai na tara wadannan zunzurutun kudaden ba ne, amma babbar ahaure’yan ambayar a nan ita ce, shin wa zai tafiyar da wadanda kudaden ? kuma shin, takamai-mai, wacce daga cikin matsalar ta tsaron, za a tunkarar? ta yaya za a kashe kudaden tare da fayyace yadda aka kashe su? Matukar gwamonin, ba su bayar da wata gamsasshiyar...
          ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa December 11, 2025 Daga Birnin Sin Kamfanonin Sin Sun Kera Tare Da Sayar Da Motoci Sama Da Miliyan 31 Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamban Bana December 11, 2025 Daga Birnin Sin Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4 December 11, 2025
    Wani abun lura ma a nan shi ne yadda a matsayinta na kasa mai tasowa ta farko a tarihin duniya da ta cimma nasarar samun wadata cikin lumana, Sin ta samar da wata taswira mai inganci, wadda sauran kasashe masu tasowa za su iya bi domin raya kansu cikin lumana, kuma karkashin hakan ne take ta fitar da shawarwari na ingiza ci gaban duniya bi da bi, irinsu shawarar raya jagorancin duniya da kasar ta gabatar a baya bayan nan. Shawarar da masharhanta da yawa ke ganin na da ma’anar gaske, wajen ingiza adalci, da daidaito a tsarin cudanyar mabanbantan sassan duniya. A gani na tun da har kasar Sin ta kai ga gina tsari mai gamsarwa na raya kai...
    Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya zargi ‘yan siyasan Nijeriya da zagon kasa ga ci gaban kasar ta hanyar daukar mukaman gwamnati a matsayin gadon gidansu a maimakon amanar jama’a. Da yake jawabi a ranar Laraba a yayin taro karo na 15 mai taken, “ya Isa haka” da ya gudana a jihar Legas, Sanusi II ya ce manyan ‘yan siyasa a fadin Nijeriya, suna ci gaba da yin zagon kasa ga ci gaban kasa saboda suna fifita kansu, iyalansu da abokan huldarsu fiye da kasar da ‘yan kasarta. Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci Katsina Ta Amince Da Bayar Da Alawus Na Naira 30,000 Duk Wata Ga Malaman Karkara Ya yi...
    Masana’antun kirar motoci na kasar Sin, sun samar tare da sayar da motocin da suka haura miliyan 31 cikin watanni 11 na farkon shekarar bana, wanda hakan ke shaida irin ci gaban da suka samu ta fuskar fitar da hajoji. A cewar wasu alkaluma daga kungiyar kamfanonin kirar motoci na kasar Sin, tsakanin watan Janairu zuwa Nuwamban bana, adadin kirar motoci a Sin ya karu da kaso 11.9 bisa dari kan mizanin shekara, zuwa sama da motoci miliyan 31.23, yayin da alkaluman sayar da su ya karu zuwa kusan miliyan 31.13, wanda ya shaida karuwar kaso 11.4 bisa dari kan mizanin shekara. Kazalika, alkaluman na watanni 11, sun shaida yadda yawan kirar motoci masu aiki da sabbin makamashi a kasar...
    Ya ce, wanda ake kara ya nema kuma an bashi kudin fansa har Naira miliyan 15 daga iyalan wanda aka kashe kafin su kashe shi.   “Sun bugi wanda aka kashe a kai da ƙirji da sanda sannan daga baya suka binne gawar a gidan Adamu da ke Dawakin Kudu,” in ji mai gabatar da kara ga kotun.   Da take yanke hukunci, Mai Shari’a Aisha Mahmoud ta ce masu gabatar da kara sun tabbatar da hujjoji game da karar da suka shigar a kan Adamu ba tare da wata shakka ba.   “Ina yanke wa Adamu hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda ya buga wa wanda aka kashe sanda a kansa da ƙirjinsa, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa....
    Bankin duniya ya fitar da sabon hasashensa kan tattalin arzikin Sin a bana a jiya Alhamis, inda ya daga na kasar Sin da maki kaso 0.4. Bankin ya ce manufofin kudi masu inganci sun sun taimaka wa harkokin sayayya da na zuba jari. Haka kuma, bukatu daga kasashe masu tasowa sun ingiza fitar da kayayyaki daga kasar. Daraktar sashen kula da harkokin Sin da Mongolia da Korea na bankin duniya, Mara Warwick, ta ce ci gaban kasar Sin a shekaru masu zuwa zai kara dogara kan sayayya a cikin gida. Kuma baya ga dabarun kashe kudi na gajeren lokaci, inganta gyare-gyaren tsarin kyautatawa al’umma da samar da kyakkyawan muhallin kasuwanci, ka iya taimakawa kara kwarin gwiwa da shimfida tubalin juriya...
    Hukumar kwallon kafa ta Nigeria (NFF) ta taya Osimhen murnar samun wannan babbar nasarar a kwallon kafa ta hanyar sanya hoton Osimhen a babban shafinsu na Facebook da yake da mabiya fiye da miliyan daya, Osimhen na daga cikin yan wasan da kocin tawagar ta Super Eagles Eric Chelle ya gayyata domin buga gasar kofin kasashen Afirka da za a buga a Morocco a shekara mai zuwa. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Salah Ba Ya Cikin ‘Yan Wasan Liverpool Da Za Su Kara Da Inter Milan December 8, 2025 Wasanni Shirye-shiryen Fara Kofin Afirka: Abin Da Ya Kamata Ku Sani December 7, 2025 Wasanni Liverpool Ba Ta Yi Min Adalci Ba – Muhammad Salah December 7, 2025
    Tafarkin samun ci gaba mai karfi da inganci, da karuwar kuzarin kirkire-kirkire da ci gaba da fadada bude kofa, su ne suka hadu suka samar da wani sabon matsayi ga tattalin arzikin kasar Sin a taswirar tattalin arzikin duniya. Ci gaba mai inganci da fadada bude kofa, ba muhimman jigon ne dake ingiza tattalin arzikin Sin kadai ba, har da nuna yanayin sauyawar abubuwan dake haifar da ci gaba a duniya. Wani nazari da kafar CGTN ta gudanar ta kafar intanet, ya nuna yadda masu bayar da amsa daga fadin duniya suka yi imanin cewa, tattalin arzikin Sin ya samu ci gaba ta kowace fuska ba tare da tangarda ba, lamarin da ya samar da tabbaci ga tattalin arzikin duniya....
    A cewar Musa, shirye-shiryen sun hada da jigilar kayayyakin tafiya, masaukai da kammala yarjejeniyar ciyarwa da hukumomin da suka dace a Kasar ta Saudiyya.   A cewarsa, adadin mahajjatan da suka yi rajistar ya hada har da jami’an gwamnati. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II December 11, 2025 Labarai Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano December 11, 2025 Manyan Labarai Katsina Ta Amince Da Bayar Da Alawus Na Naira 30,000 Duk Wata Ga Malaman Karkara December 11, 2025
    Mahukuntan kasar Sin sun gudanar da taron koli, na tattauna aikin raya tattalin arzikin kasar, don tsara abubuwan da za a aiwatar a shekarar 2026 dake tafe. An gudanar da taron ne a jiya Laraba da yau Alhamis, inda shugabannin kasar suka tantance abubuwa mafiya muhimmanci, wadanda za a aiwatar, dangane da raya tattalin arzikin kasar a shekara mai kamawa. Cikin muhimmin jawabi da ya gabatar yayin taron, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya waiwayi aikin raya tattalin arziki da Sin ta aiwatar a shekarar nan ta 2025, tare da fayyace halin da tattalin arzikin kasar ke ciki, da ma aikin da aka tsara gudanarwa a shekara mai zuwa. Yayin taron, an yi amannar cewa shekarar 2025 ta fita daban,...
    Ministan Harkokin Waje na Jamhuriyar Benin, Olushegun Adjadi Bakari, ya ce kimanin sojoji 200 daga Najeriya da Ivory Coast yanzu haka na cikin kasar shi a matsayin wani ɓangare na aikin tsaro don tallafa wa gwamnati. Ƙaramar ƙasa ta Yammacin Afirka ta girgiza da yunƙurin juyin mulkin da bai yi nasara ba a ranar Lahadi, wanda ya sa Najeriya, Faransa da Ivory Coast suka tashi tsaye wajen goyon bayan gwamnatin farar hula. Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota “A halin yanzu akwai kusan sojoji 200 da suka zo don ba da taimako ga rundunar tsaron Benin a cikin aikin sharewa da tsaftacewa,” in ji Olushegun Adjadi Bakari ga ’yan...
    Jam’iyyar PDP a ranar Alhamis ta tabbatar da mutuwar mataimakin gwamnan jihar Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo. Jam’iyyar ta tabbatar da rasuwar ce a cikin wata sanarwa da sakatarenta yada labaranta na kasa, Kwamared Ini Ememobong, ya fitar. Rahotanni sun ce Ewhrudjakpo ya yanke jiki ya faɗi a ofishinsa da ke gidan gwamnati, Yenagoa, a ranar Alhamis, inda aka garzaya da shi zuwa Cibiyar Lafiya ta Ƙasa (FMC) da ke Yenagoa. Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis. An haifi Ewhrudjakpo ranar ranar biyar ga watan Satumban 1965, a ƙauyen Ofoni da ke Ƙaramar Hukumar Sagbama, Jihar Bayelsa. Ya rasu yana da shekaru 60. Kodayake ba a san ainihin dalilin faɗuwarsa ba, majiyoyi sun ce ya faɗi ne ba zato ba...
    Ministan harkokin wajen Turkiya Hakan Faidan ne ya bayyana cewa; kasarsa za ta iya daukar nauyin wararen matsalar Falasdinu, kuma a shirye take ta aike da sojoji zuwa yankin na Gaza idan bukatar hakan ta taso. Fidan ya fada wa kamfafen watsa labaru cewa; Tukriya a shirye take ta yi duk abinda za ta iya yi, ta kuma dauki nauyin da ya dace akan batun Falasdinu. A can Amurka kuwa, manzon musamman na Amurka akan harkokin yammacin Asiya, Barrack ya  fada wa jaridar  “Jerrusalem Post” cewa: Kasar Turkiya tana da sojoji masu karfi, kuma tana hulda da Hamas, a dalilin hakan shigarta cikin rundunar da za a aike Gaza, zai yi amfani.” A ranar 18 ga watan Nuwamba ne dai...
    Shugaban kasar Rasha Vladmir Putin ya tattauna ta wayar tarho da takwaransa na kasar Venezuela Nicholay Maduro ta wayar tarho inda ya bayyana masa cikakken goyonbaya bisa barazanar da kasar take fuskanta daga Amurka. Fadar mulkin kasar ta Rasha ta ce, shugabannin kasashen biyu sun yi musayar ra’ayi akan hanyoyin bunkasa alaka a tsakaninsu. Tun a baya, a yayi wani zama da kwamitin tsaro na MDD ya yi, wakilan kasashen Venezuela, Rasha da China, sun yi tir da yadda Amurka take jibge sojiji a yankin Carriebia, tare da bayyana hakan a matsayin barazana ga zaman lafiyar duniya. Kasashen uku sun kuma bayyana wajabci kare hurumin kasar Venezuela da kuma kaucewa tsoma baki a harkokin cikin gidanta. Share 0 0 votes...
    Ministan taron  Haramtacciyar Kasar Isra’ila Ben Gafir ya sha alwashin rushe kabarin Sheikh Izzuddin al-Kassam dake kusa da birnin Haifa. Ben Gafir ya wallafa hotonsa na tsokana a shafinsa n asada zumunta a kusa da makwancin shahararren malamin addinin mususuluncin tare da motar buldoza a kusa da shi, tana rusa wata hema da aka gina daura da kabarin, wacce mutane suke yin salla a cikinta da kuma yin addu’oi. Sheikh Izzuddin al-Kassam  da reshen soja na Hamas ke dauke da sunansa, malamin addini ne wanda ya yaki Birtaniya da ‘yan sahayoniya a lokacin da suke share fagen gina haramtacciyar kasar Isra’ila. Ya yi shahada ne dan lokaci kadan gabanin shelanta kafuwar wannan haramtacciyar kasa a 1948. Makwancinsa ya a garin...