Leadership News Hausa:
2025-06-21@01:26:49 GMT

Za A Gudanar Da Taron Tallata Fim Din “Red Silk” A Moscow

Published: 5th, May 2025 GMT

Za A Gudanar Da Taron Tallata Fim Din “Red Silk” A Moscow

A jajibirin bikin cika shekaru 80 da samun nasarar babban yakin ceton kasa a kasar Rasha, rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG, tare da hukumar kula da harkokin fina-finai ta kasar Sin, za su gudanar da bikin tallata fim din “Red Silk” wanda Sinawa da ‘yan Rasha suka shirya a birnin Moscow.

A wannan lokacin, mashirya fim din Sinawa da ‘yan Rasha, za su yi musayar ra’ayoyinsu kan yadda suka shirya fim din, tare da sanar da cewa, za a fitar da fim din a kasar Sin a watan Satumba na wannan shekara a lokacin da kasar Sin ke bikin cika shekaru 80 da samun nasarar yakin juriya na jama’ar kasar Sin kan zaluncin Jafanawa da yakin adawa da Fasistanci na duniya.

 

A matsayin sabon hadin gwiwa tsakanin Sin da Rasha a masana’antar fina-finai, fim din “Red Silk’ wanda aka yi hadin gwiwar shiryawa, an fitar da shi Rasha a ranar 20 ga Fabrairun wannan shekara. Kana an tsara fim din ne bisa abubuwan tarihi da suka faru a zahiri, kuma ya ba da labarin yadda ‘yan juyin juya hali na Sin da Tarayyar Soviet suka yi yaki kafada da kafada a shekarar 1927, inda suka yi nasarar raka muhimman takardu na sirri lami lafiya. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a kasar Sin

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

Wasu na ganin jita-jitar ta samo asali ne bayan wani abokin aikinsa na baya, Sani Sidi, ya koma jam’iyyar APC tare da magoya bayansa a Kaduna.

Amma Sambo ya ce hakan bai shafe shi ba.

Hakazalika, an shirya Sambo zai halarci bikin ƙaddamar da asibiti mai gadaje 300 da ke Kaduna a ranar Alhamis, 19 ga watan Yuni, 2025.

Ya halarci bikin kuma hakan ba yana nufin ya goyi bayan wata jam’iyya ba ne.

Ƙungiyarsa ta nanata cewa Sambo yana nan daram a cikin jam’iyyar PDP, kuma labarin sauya sheƙar nasa ƙarya ce da aka ƙirƙira domin tayar da hankali da ƙoƙarin cimma wasu muradu na siyasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
  • Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya
  • Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare
  • Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho
  • Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC
  • Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
  • Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital
  • Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
  • Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – Masana
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran