Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kaddamar da manyan jami’an likitocin kasa a shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin shekarar 2025.

 

Babban Daraktan Hukumar Alhaji Umar Ahmed Labbo ne ya bayyana haka a yayin bikin kaddamar da aikin da aka gudanar a Dutse babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa, hukumar ta kaddamar da tawagar likitocin guda 10, inda ya bukaci kungiyar da ta yi aiki da gaskiya, hakuri, da jajircewa wajen yi wa alhazan jihar hidima a kasar Saudiyya.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce aikin amana ce da bai kamata kungiyar ta dauka da wasa ba.

Ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa amincewa da wannan tawagar, inda ya nuna cewa, wannan shi ne karon farko da jihar ke tura ma’aikatan lafiya irin wannan aikin zuwa kasashen waje.

 

Ya jaddada godiya na zabarsu da kuma bukatar kare jin dadin alhazan Jigawa a duk tsawon wannan lokaci na aikin Hajji.

A nasa jawabin shugaban kwamitin yada labarai Abdulrashid Yusuf ya yi kira ga ‘yan wakilan da su ci gaba da gudanar da ayyukansu cikin himma tare da sanin ya kamata da kuma tsoron Allah.

 

Yusuf, ya yabawa gwamnatin jihar bisa kara adadin ma’aikatan lafiya zuwa 10.

USMAN MZ

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Za a dawo da dukkan Alhazai gida ranar 28 ga Yuni – NAHCON

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta tabbatar da aniyarta na dawo da dukkan Alhazan Najeriya da ke Saudiyya zuwa ranar 28 ga watan Yunin, 2025.

Rahotanni daga Hukumar NAHCON da ke birnin Makkah na cewa, alhazan Najeriya 6,528 ne suka dawo Najeriya, yayin da Kamfanin Max Air ya kammala jigilar Alhazai jirgi na 16 a ranar Talata.

Kotu ta ba da belin Natasha kan N50m kan zargin bata sunan Akpabio Ba Atiku kaɗai ba ne matsalar PDP — Gwamna Lawal

Wata sanarwa da Mataimakiyar Daraktan yaɗa labarai Fatima Sanda Usara ta fitar ta ce NAHCON tare da hukumar jin daɗin alhazai ta jiha, da kuma masu jigilar jiragen sama na shekarar 2025 suna yin duk abin da za su iya don ƙara saurin jigilar.

“Hukumar ta shirya dawo da dukkan alhazan nan da ranar 28 ga watan Yuni 2025 kuma ta ci gaba da zage damtse don jigilar.

“A cikin wannan lokaci, dukkan ƙasashen suna ƙoƙarin dawo da alhazansu a lokaci guda, kuma hakan ya haifar da tsananin buƙatar filayen jiragen sama.

“Waɗannan gurbi na Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama (GACA) da ke Saudi Arabiya ne ke kula da su, kuma a halin yanzu, ba a ware wa Nijeriya gurabe masu yawa kamar yadda ake buƙata domin tafiyar da alhazai masu yawa cikin gaggawa.

“Saboda haka, manyan masu ruwa da tsaki a harkar sufurin jiragen sama guda uku sun tsara dabarun ƙara yawan wuraren da za a samu a ƙasar.

“Ana fatan tattaunawa mai ƙarfi da mahukuntan Saudiyya za ta taimaka wajen ƙara yawan filayen jiragen.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya
  • Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
  • Kotu ta aike da dan TikTok din da ke wanka a kan titi a Kano gidan yari
  • Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare
  • Hisbah ta lalata katan 243 na barasa da wasu kayan maye a Yobe
  • Za a dawo da dukkan Alhazai gida ranar 28 ga Yuni – NAHCON
  • Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
  • HOTUNA: Yadda Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a harin Benuwe
  • Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo
  • Ma’aikatan Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna za su tsunduma yajin aiki