Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kaddamar da manyan jami’an likitocin kasa a shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin shekarar 2025.

 

Babban Daraktan Hukumar Alhaji Umar Ahmed Labbo ne ya bayyana haka a yayin bikin kaddamar da aikin da aka gudanar a Dutse babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa, hukumar ta kaddamar da tawagar likitocin guda 10, inda ya bukaci kungiyar da ta yi aiki da gaskiya, hakuri, da jajircewa wajen yi wa alhazan jihar hidima a kasar Saudiyya.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce aikin amana ce da bai kamata kungiyar ta dauka da wasa ba.

Ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa amincewa da wannan tawagar, inda ya nuna cewa, wannan shi ne karon farko da jihar ke tura ma’aikatan lafiya irin wannan aikin zuwa kasashen waje.

 

Ya jaddada godiya na zabarsu da kuma bukatar kare jin dadin alhazan Jigawa a duk tsawon wannan lokaci na aikin Hajji.

A nasa jawabin shugaban kwamitin yada labarai Abdulrashid Yusuf ya yi kira ga ‘yan wakilan da su ci gaba da gudanar da ayyukansu cikin himma tare da sanin ya kamata da kuma tsoron Allah.

 

Yusuf, ya yabawa gwamnatin jihar bisa kara adadin ma’aikatan lafiya zuwa 10.

USMAN MZ

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Sanata Buba ya ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobi kyauta

Sanatan Bauchi ta Kudu, Shehu Buba Umar ya ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobi da kuma takin zamani kyauta ga al’ummar mazaɓarsa.

Da yake ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobin garin Goɗɗiya da ke Ƙaramar Hukumar Bogoro, Sanata Buba ya ce, “A bana, za mu yi allurar rigakafin dabbobi 85,000 a wannan yankin na Majalisar Dattawa.”

Ya ce a baya an yi wa dabbobi kimanin 40,000 allurar rigakafin a fadin yankin.

“Na yi imanin cewa wannan abu ɗaya ne daga ayyukan wakilci wa mutanenmu manoma da makiyaya. ’Yan Najeriya ne kamar mu duka, suna zaɓe mu, kuma suna ba da gudummawa sosai ga tattalin arzikin ƙasar nan.

“Wannan ba wani abu ba ne na musamman amma na yi imanin cewa wani abu ne da muke yi wa makiyaya da manoma.”

Ya ce alluran rigakafin na kyauta na da nufin kare rayuwar dabbobi, da ƙara haɓaka kiwonsu, da kuma tabbatar da lafiyarsu da wadatar abinci a ƙananan hukumomi bakwai da ke Shiyyar Bauchi ta Kudu.

“Wannan aikin wata babbar alama ce da ke nuna aniyarmu ta kare lafiyar dabbobinmu, da kare lafiyar al’ummarmu, da kuma martaba tattalin arzikinmu.

“Za a gudanar da wannan aiki a dukkanin ƙananan hukumomin bakwai na shiyyar Sanata na Bauchi ta kudu, inda za a yi wa shanu, tumaki da awaki a kowace ƙaramar hukuma alluran rigakafin.

“Ƙwararrun likitocin dabbobi da masana kimiyyar kiwon lafiyar dabbobi za su yi aiki tare da shugabannin al’umma, masu dabbobi, da sauran masu ruwa da tsaki don tabbatar da cewa wannan aikin ya samu nasara a a kowace ƙaramar hukuma.”

Wani mai ruwa da tsaki a mazaɓar Dass, Tafawa Valewa da Vogoro Alhaji Aminu Tukur ya buƙaci manoman yankin da su fito da dabbobinsu domin yin rigakafin.

Tukur ya yi kira ga Sanatan da ya gina cibiyar koyar da sana’o’i a yankin domin rage yawan matasa marasa aikin yi, ya kuma shawarce shi da ya riƙa bibiyar aikin hanyar Gwamnatin Tarayya da tsohon Shugaban Majalisar Wakilai Yakubu Dogara ya fara da ba a ƙarasa su ba.

Makiyaya da dama da suka ci gajiyar allurar sun yaba da yadda Sanata Buba ya jajirce wajen inganta harkokin kiwon dabbobi da lafiyarsu, da tallafa wa manoma ta hanyar ingantattun tsare-tsare da kuma daukar matakai cikin lokaci. Sun nuna jin daɗinsu bisa bayar da tallafin a kan lokaci.

Sankaran ya kuma fara rabon takin zamani buhu 4,200 samfurin NPK kyauta ga manoma.

Ya ce an dauki matakin ne don tallafa wa ayyukan noma da inganta amfanin gona ga manoman yankin.

Sanatan ya ce shirin na da nufin ƙarfafa wa manoma gwiwa domin su sami damar rage ƙalubalen da ake fuskanta wajen samar da abinci tare da inganta adadi da ingancin amfanin gona ga al’ummar gundumar.

Ya gode wa kwamitin rabon kayayyakin tare da shawartar su da su tabbatar da adalci tare da raba kayan ga manoma na gaskiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanata Buba ya ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobi kyauta
  • An Kaddamar Da Shirin Dashen Itatuwan Dabino Miliyan 50 A Jigawa
  • Makon Kiwon Lafiyar Uwa da Ɗa ya Samu Gagarumar Nasara a Karamar Hukumar Gwarzo
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Duba Titi Mai Tsawo Kilomita 49
  • Gwamnan Kano Ya Kaddamar da Shirin Dashen Bishiyoyi
  • Gwamnatin Jigawa Ta Dauki Manyan Matakan Kare Jihar Daga Ambaliyar Ruwa
  • Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar
  • Mai Martaba Sarkin Dutse Ya Kaddamar Da Rabon Zakka Ta Shekarar 1446
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Sha Alwashin Inganta Kwazon Kananan Hukumomin Jihar