A sanarwar da kakakinsa Mukhtar Gidado ya fitar, gwamnan ya miƙa saƙon jajantawa ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu, al’umman ƙaramar hukumar Alkaleri da ma mutanen jihar Bauchi baki ɗaya.

 

Ya yi addu’ar Allah ya jiƙan jaruman da suka rasa rayukansu a ƙoƙarinsu na kare yankunansu.

 

Gwamnan sai jaddada aniyar Gwamnatinsa na daƙile kowace irin nau’in barazanar tsaro a dukkanin faɗin jihar.

 

Ya yi kira ga jama’a da su rika zama cikin haɗin kai da bayar da gudunmawarsu ga jami’an tsaro tare da samar musu da bayanan sirri a kan lokaci da zai bada damar daƙilewa ko magance matsalolin tsaro a kan lokaci.

 

Yayin da ya ke tabbatar wa jama’a cewa gwamnati tana kan aikin haɗin gwiwa da hukumomin tsaro wajen ganin an cafko waɗanda suka aikata wannan kisan domin su fuskanci Shari’a, Gwamnan ya kuma bada tabbacin cewa zai yi ko menene domin tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyar jama’an jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

A shekarar 2023 lokacin da Gwamna Lawal ya hau mulki, Zamfara ta kasance a ƙasan jadawalin a matsayi na 36.

 

Rahoton ya nuna cewa kuɗaɗen shiga na jihar sun ƙaru da kashi 182.34%, daga naira biliyan 87.44 a 2023 zuwa naira biliyan 246.88 a 2024. Haka kuma jimillar kuɗaɗen shiga gaba ɗaya ta ƙaru zuwa naira biliyan 315.53, ƙaruwar kusan kashi 118%. Haraji da jihar ta tara ya kai kusan kashi 10.31% na jimillar kuɗaɗen shiga a 2024.

 

BudgIT ta bayyana cewa wannan ci gaban yana nuna Zamfara ta fara rage dogaro ga kuɗin kason asusun tarayya, kuma idan za a yi hasashe, jihar na da ƙarfin kai da kai idan za a kalle ta a matsayin ikon tattalin arziki mai zaman kansa.

 

A bangaren haraji, jihar ta samu naira biliyan 25.46 a 2024, ƙaruwa ce ta kusan kashi 15% daga naira biliyan 22.16 a shekarar da ta gabata. Har ila yau, kuɗaɗen FAAC sun ƙaru da sama da kashi 239%, daga naira biliyan 65.28 a 2023 zuwa biliyan 221.42 a 2024.

 

Rahoton ya kuma yi hasashe kan habakar kuɗaxen shiga marasa haraji, inda aka samu ƙaruwa sosai a bangaren lasisi, kuɗin biyan takardu da wasu hanyoyin samun kuɗaɗe. Misali, kuɗaɗen lasisi sun tashi da fiye da kashi 5,900% a shekarar 2023.

 

A ɓangaren kashe kuɗi, musammam a fannin lafiya da ilimi, rahoton ya nuna ƙarin kuɗaɗen da gwamnati ta zuba, duk da cewa akwai ƙalubalen ingantacciyar aiwatarwa. Jimillar kashe kuɗin lafiya ta tashi daga naira biliyan 4.29 a 2022 zuwa biliyan 11.88 a 2024, inda kashe kuɗi kan mutum ɗaya ya ninka fiye da biyu.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027 November 3, 2025 Manyan Labarai Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso  November 3, 2025 Labarai NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan November 3, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume
  • An kama barawo da wayoyin sata 17 a taron sauya shekar Gwamnan Bayelsa
  • Uba Sani Ya Kaddamar Da Gidaje 100 Ga Waɗanda Rikici Ya Shafa A Jihar
  • Abba ya umarci a riƙa gudanar da taron tsaro a ƙananan hukumomin Kano
  • Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan
  • ’Yan Sandan Legas sun ayyana neman Sowore ruwa a jallo
  • Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT
  • Uwargidan Gwamnan  Zamfara Ta Yaba Wa  Karamar Hukumar Gusau Bisa Shirin Tallafawa Jama’a
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano