A sanarwar da kakakinsa Mukhtar Gidado ya fitar, gwamnan ya miƙa saƙon jajantawa ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu, al’umman ƙaramar hukumar Alkaleri da ma mutanen jihar Bauchi baki ɗaya.

 

Ya yi addu’ar Allah ya jiƙan jaruman da suka rasa rayukansu a ƙoƙarinsu na kare yankunansu.

 

Gwamnan sai jaddada aniyar Gwamnatinsa na daƙile kowace irin nau’in barazanar tsaro a dukkanin faɗin jihar.

 

Ya yi kira ga jama’a da su rika zama cikin haɗin kai da bayar da gudunmawarsu ga jami’an tsaro tare da samar musu da bayanan sirri a kan lokaci da zai bada damar daƙilewa ko magance matsalolin tsaro a kan lokaci.

 

Yayin da ya ke tabbatar wa jama’a cewa gwamnati tana kan aikin haɗin gwiwa da hukumomin tsaro wajen ganin an cafko waɗanda suka aikata wannan kisan domin su fuskanci Shari’a, Gwamnan ya kuma bada tabbacin cewa zai yi ko menene domin tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyar jama’an jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Hisbah ta lalata katan 243 na barasa da wasu kayan maye a Yobe

A ci gaba da ƙoƙarinta na tabbatar da kyawawan halaye da kuma samar da zaman lafiya a tsakanin al’umma, Hukumar Hisbah ta Jihar Yobe ta lalata katan 243 na barasa da galan 100 na barasa da aka haɗa a gida, da aka fi sani da sukudaye.

A wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na Hukumar, Adamu Muhammad ya sanya wa hannu, ta ce an lalata barasa a Damaturu, a wani mataki na aiwatar da dokar hana sha da kayan rarraba barasa a jihar.

Guguwar ruwan sama ta yi ɓarna a Kwalejin Kimiyya da Fasaha a Kogi Tinubu na ƙaddamar da wasu ayyuka a Jihar Kaduna

Shugaban Hukumar Hisbah na jihar, Dokta Yahuza Hamza Abubakar ne ya bayyana cewa aikin ya yi dai-dai da aikin hukumar na aiwatar da dokokin da ke inganta nagarta da kare martabar al’umma.

“Shaye-shaye na haifar da barazana ga lafiyar jama’a da zamantakewar jama’a wadda akan hakan ne aka haramta sha da rarraba ta a cikin jihar a ƙarƙashin dokokin da ake da su,” in ji shi.

Dokta Yahuza ya nanata ƙudurin hukumar na samar da zaman lafiya, adalci da gyara al’umma, inda ya ce Hisbah ta kuma sasanta tare da warware wasu matsaloli a ayyukan da suka yi a baya-bayan nan.

Ya buƙaci mazauna jihar da su ci gaba da marawa ƙoƙarin hukumar baya wajen tabbatar da kyawawan ɗabi’u da mutuncin jama’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya
  • Hisbah ta lalata katan 243 na barasa da wasu kayan maye a Yobe
  • An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 
  • Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara
  • An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina
  • HOTUNA: Yadda Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a harin Benuwe
  • Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato
  • Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
  • Ambaliyar Mokwa – Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja