Gwamnan Bauchi Ya Yi Allah-wadai Da Kisan ‘Yan Banga A Alkaleri
Published: 6th, May 2025 GMT
A sanarwar da kakakinsa Mukhtar Gidado ya fitar, gwamnan ya miƙa saƙon jajantawa ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu, al’umman ƙaramar hukumar Alkaleri da ma mutanen jihar Bauchi baki ɗaya.
Ya yi addu’ar Allah ya jiƙan jaruman da suka rasa rayukansu a ƙoƙarinsu na kare yankunansu.
Gwamnan sai jaddada aniyar Gwamnatinsa na daƙile kowace irin nau’in barazanar tsaro a dukkanin faɗin jihar.
Ya yi kira ga jama’a da su rika zama cikin haɗin kai da bayar da gudunmawarsu ga jami’an tsaro tare da samar musu da bayanan sirri a kan lokaci da zai bada damar daƙilewa ko magance matsalolin tsaro a kan lokaci.
Yayin da ya ke tabbatar wa jama’a cewa gwamnati tana kan aikin haɗin gwiwa da hukumomin tsaro wajen ganin an cafko waɗanda suka aikata wannan kisan domin su fuskanci Shari’a, Gwamnan ya kuma bada tabbacin cewa zai yi ko menene domin tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyar jama’an jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dattawa ta kafa kwamitin lura da gwamnan riƙo na Jihar Ribas
Majalisar Dattawa ta kafa kwamiti mai mambobi 18 domin sanya idanu kan yadda gwamnan riƙo na Jihar Ribas Vice Admiral Ibok Ete Ibas mai ritaya ke tafi da aikinsa.
Majalisar ta ce ta ɗauki matakin ne a wani yuƙuri na ƙarfafa shugabanci na gari ba tare da rufa-rufa ba a jihar da ke kudu maso kudancin Najeriya.
Alƙaluman sakamakon jarabawar bana — JAMB Friedrich Merz ya zama sabon shugaban gwamnatin JamusShugaban Majalisar Dattawan, Godswill Akpabio ya sanar yayin zaman majalisar na yau Talata cewa kafa kwamitin na da matuƙar mahimmancin wajen sa ido kan abubuwan da ke faruwa a jihar.
Shugaban masu rinjaye Opeyemi Bamidele ne shugaban kwamatin, yayin da mambobin kuma sun haɗa da Adamu Aliero, da Osita Izunaso, da Osita Ngwu, da Kaka Shehu, da Aminu Abass, da Tokunbo Abiru, Adeniyi Adebire.
A wannan Talatar ce shi ma Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas Tajudeen ya sanar da cewa za su kafa kwamitin da zai jiɓanci tabbatar da sulhu kan rikicin siyasa da ya yi wa Jihar Ribas dabaibayi.
Abbas wanda ya ce kwamitin wanda za su yi tarayya da Majalisar Dattawa wajen kafa shi zai ƙunshi wasu manyan ƙasar nan da ake mutuntawa domin tabbatar da wanzuwar dimokuraɗiyya a jihar.
Ana iya tuna cewa a watan Maris ne Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas sakamakon abin da ya kira “karyewar doka da oda” wanda ya auku sanadiyyar rikicin siyasa tsakanin Gwamna Similanayi Fubara na PDP mai adawa da tsohon Gwamna Wike mai ƙawance da APC mai mulki.