’Yan kungiyar asiri: Mutum 95 sun shiga hannu a Edo
Published: 3rd, May 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jihar Edo ta kama mutane 95 da ake zargi da ayyukan ƙungiyoyin asiri.
An kama mutanen ne a wani farmaki da aka kai kan masu aikata laifukan da suka shafi kungiyoyin asiri a garin Benin City da kewaye a makon da ya gabata.
Kwamishinan ’yan sanda, Monday Agbonik, ya bayyana cewa an gurfanar da 64 daga cikin wadanda ake zargin suna da alaka da kungiyoyin Maphites, Eiye, da Aye kuma ake zarginsu da kisan gilla da aka yi kwanan nan a rikicin kungiyoyin asiri.
Kayan da aka ƙwato sun hada da bindigogi biyu ƙirar gida, bindiga guda mai tashi daya, da harsashi 24.
’Yan sandan sun shawarci iyaye da su kula da ayyukan ’ya’yansu kuma sun gargadi matasa da kada su shiga kungiyoyin da ba bisa ka’ida ba wadanda ke kawo hatsari ga rayuwarsu.
Bincike na ci gaba da gudana kan sauran wadanda ake zargin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda kungiyar asiri zargi
এছাড়াও পড়ুন:
An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran
Isra’ila ta tabbatar cewa an garzaya da ’yan ƙasarta aƙalla 154 asibiti bayan sabbin hare-haren ramuwar gayya da Iran ta kawo mata.
Ma’aikatar lafiyar Isra’ila ta ce aƙalla mutum huɗu daga cikin waɗanda aka kai asibitin suna cikin halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai, wasu biyar kuma na samun kulawa ta musamman saboda tsananin tashin hankali.
Alkaluman da ma’aikatar ta fitar sun nuna cewa mutum 130 daga cikin majinyatan sun samu raunuka marasa tsanani a sakamakon hare-haren.
Wannnan na zuwa ne a yayin da Iran ta ci gaba luguden rokoki a matsayin ramuwar gayya a sassan Isra’ila a a ranar Talata.
Isra’ila ta ce Iran ta lashe mata mutane akalla 24.
A ɗaya ɓangaren kuma Iran cewa harin tsokana da Isra’ila ta kai mata ya yi ajalin kimanin mutum 224.