Aminiya:
2025-08-02@11:27:39 GMT

’Yan kungiyar asiri: Mutum 95 sun shiga hannu a Edo

Published: 3rd, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Edo ta kama mutane 95 da ake zargi da ayyukan ƙungiyoyin asiri.

An kama mutanen ne a wani farmaki da aka kai kan masu aikata laifukan da suka shafi kungiyoyin asiri a garin Benin City da kewaye a makon da ya gabata.

Kwamishinan ’yan sanda, Monday Agbonik, ya bayyana cewa an gurfanar da 64 daga cikin wadanda ake zargin suna da alaka da kungiyoyin Maphites, Eiye, da Aye kuma ake zarginsu da kisan gilla da aka yi kwanan nan a rikicin kungiyoyin asiri.

Kayan da aka ƙwato sun hada da bindigogi biyu ƙirar gida, bindiga guda mai tashi daya, da harsashi 24.

’Yan sandan sun shawarci iyaye da su kula da ayyukan ’ya’yansu kuma sun gargadi matasa da kada su shiga kungiyoyin da ba bisa ka’ida ba wadanda ke kawo hatsari ga rayuwarsu.

Bincike na ci gaba da gudana kan sauran wadanda ake zargin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda kungiyar asiri zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki

Babban magatakardar kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Kassim ya bayyana cewa; Hizbullah tana yin aiki ne ta fuskoki biyu; na farko gwgawarmaya da HKI, sai kuma a fagen Siyasa a cikin gida.

Shugaban kungiyar ta Hizbullah wanda ya gabatar da jawbai a jiya domin girmama babban kwamandan kungiyar Hizbullah Shahid Sayyid Fu’ad Shukr ya ce; An zabi shugaban kasa Joseph Aun ne bayan da aka dauki shekaru ba tare da shugaban kasa ba a kasar. Kuma kungiyar gwagwarmaya ta tabbatar da cewa ginshiki ne a fagen siyasa, wacce ta saukaka yadda aka zabi shugaban kasar da kafa gwamnati.”

Har ila yau Sheikh Naim Kassim ya yi bayani akan yadda gwagwarmaya ta kafu a cikin kasar Lebanon a matsayin mayar da martani ga mamayar HKI, ta kuma cike gibin da sojoji su ka bari, da a karshe a 2000 ta kori HKI daga cikin Lebanon.

Sheik Na’im Kassim ya kuma ce; Gwgawarmaya wani nauyi ne da rataya akan kowa, ba wai zabi ba ne,kuma lokacin da aka yi aiki a tsakanin gwgawarmaya, soja da al’umma an cimma nasarori masu yawan gaske.

Babban  magatakardar kungiyar ta Hizbullah sheik Na’im Kassim ya kuma ce; Batun makaman dake hannun kungiyar Hizbullah wani batu ne da ya shafi cikin gidan kasar Lebanon, don haka ba shi da wata alaka da HKI.”

Akan batun kwance damarar yakin kungiyar ta Hizbullah, Sheikh Na’im Kassim ya ce, duk wanda yake son ganin hakan ta faru, to yana yi wa Isra’ila aiki ne.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata July 31, 2025 Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila July 31, 2025 Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba July 31, 2025 Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku   July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Ansarullah: Amurka Tana Da Hannu A Ta’asar Da HKI Take Aikatawa A Gaza
  • Kungiyar Wasan Taekwondo Ta Guragu Ta Iran Ta Zama Zakara A Asiya Karo Na 10 A Jere
  • Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa
  • Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa
  • Kungiyar AU Ta Yi Watsi Da Kafa Gwamnatin Adawa Da Kungiyar RSF Ta Yi A Sudan
  • Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
  • Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Kwara Ta Kwashe Mabarata Daga Titunan Jihar Su 94
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya