Birnin Kudu Za Ta Samar Da Cibiyar Horas Da Maniyata
Published: 6th, May 2025 GMT
Karamar Hukumar Birnin Kdu tace tana nazarin samar da cibiyar horas da maniyyata aikin hajji ta dindindin a yankin domin karawa mahajjata kaimi wajen gudanar da aikin karbabbe.
Shugaban Karamar Hukumar, Alhaji Muhammad Uba Builder ya bada wannan tabbacin a lokacin rufe bitar da aka shiryawa maniyyatan yankin na Birnin kuudu.
Yana mai cewar, idan aka samar da cibiyar zata kunshi dukkanin muhimman wuraren da ake ziyarta a lokacin gudanar da aikin hajji.
Alhaji Muhammad Uba, yace za a kuma samar da ajujuwan horas da maniyyata da ofisoshin malaman bita da sauran dukkan abubuwan daya dace a cibiyar.
Kazalika, Shugaban Karamar Hukumar, ya biya malaman bitar alawus dinsu na wannan shekarar da ma kwanton na shekarar da ta gabata wanda ya gada daga gwamnatin da ta gabata.
A don haka, ya bukaci maniyyatan yankin su gudanar da addu’o’in neman zaman lafiya mai dorewa da karuwar arziki ga yankin da jihar Jigawa da ma kasa baki daya.
A jawabin da ya gabatar, jagoran malaman da suka gabatar da bitar Malam Suleiman Datti ya bukaci shugaban Karamar Hukumar ya taimaka wajen kara yiwa malaman bitar rijista a yankin.
Wasu daga cikin maniyyatan sun bayyana gamsuwa dangane da yadda Karamar Hukumar ta dauki nauyin ciyar da su na tsawon wata guda baya ga sauran hidimomin da aka yi masu.
Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, fiye da maniyyata dari ne zasu gudanar da aikin hajjin bana daga karamar Hukumar ta Birnin kudu.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Karamar Hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina
Da take aiwatar da rahotannin sirri cikin gaggawa, rundunar hadin gwiwa da ta kunshi jami’an ‘yansandan Nijeriya, Sojoji, jami’an kula da jama’a na jihar, da ’yan banga na yankin sun bi sawun barayin da suka tsere zuwa Dutsen Falale da ke yankin Kurfi-Safana inda aka yi musayar wuta mai tsanani, wanda ya yi sanadin mutuwar ‘yan bindigar 12.
Sai dai kuma, yayin da yake yabawa wannan bajinta da jajircewa da jami’an tsaron suka yi, Dakta Mua’zu ya bayyana matukar alhininsa game da rasuwar wani dan banga mai suna Alhaji Danmalam wanda ya rasa ransa a fafatawar.
Bugu da kari, soja guda ya samu raunuka kuma a halin yanzu yana samun kulawa a Asibiti.
Alhaji Danmalam ya rasu ne sakamakon harbin bindiga a cibiyar kiwon lafiya ta matakin farko da ke Charanchi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp