Birnin Kudu Za Ta Samar Da Cibiyar Horas Da Maniyata
Published: 6th, May 2025 GMT
Karamar Hukumar Birnin Kdu tace tana nazarin samar da cibiyar horas da maniyyata aikin hajji ta dindindin a yankin domin karawa mahajjata kaimi wajen gudanar da aikin karbabbe.
Shugaban Karamar Hukumar, Alhaji Muhammad Uba Builder ya bada wannan tabbacin a lokacin rufe bitar da aka shiryawa maniyyatan yankin na Birnin kuudu.
Yana mai cewar, idan aka samar da cibiyar zata kunshi dukkanin muhimman wuraren da ake ziyarta a lokacin gudanar da aikin hajji.
Alhaji Muhammad Uba, yace za a kuma samar da ajujuwan horas da maniyyata da ofisoshin malaman bita da sauran dukkan abubuwan daya dace a cibiyar.
Kazalika, Shugaban Karamar Hukumar, ya biya malaman bitar alawus dinsu na wannan shekarar da ma kwanton na shekarar da ta gabata wanda ya gada daga gwamnatin da ta gabata.
A don haka, ya bukaci maniyyatan yankin su gudanar da addu’o’in neman zaman lafiya mai dorewa da karuwar arziki ga yankin da jihar Jigawa da ma kasa baki daya.
A jawabin da ya gabatar, jagoran malaman da suka gabatar da bitar Malam Suleiman Datti ya bukaci shugaban Karamar Hukumar ya taimaka wajen kara yiwa malaman bitar rijista a yankin.
Wasu daga cikin maniyyatan sun bayyana gamsuwa dangane da yadda Karamar Hukumar ta dauki nauyin ciyar da su na tsawon wata guda baya ga sauran hidimomin da aka yi masu.
Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, fiye da maniyyata dari ne zasu gudanar da aikin hajjin bana daga karamar Hukumar ta Birnin kudu.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Karamar Hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya ta sanar da samun nasarar cafke Ifeanyi Eze Okorienta, wanda aka fi sani da “Gentle de Yahoo”, ɗaya daga cikin manyan kwamandojin ƙungiyar IPOB, a wani samame da ta kai a yankin kudu maso gabashin ƙasar.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN ya ruwaito wata majiya daga hedikwatar rundunar sojin tana cewa an cafke Gentle de Yahoo ne yayin farmakin da sojojin suka kai a ranar Lahadi kan sansanonin ’yan ƙungiyar a cikin wani dajin da ke ƙaramar hukumar Okigwe a Jihar Imo.
An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a RibasMajiyar ta ce a yayin cafke jagoran na IPOB, an kuma ƙwato makamai da dama daga hannunsa, ciki har da bindigogi kirar Turai, harsasai, kakin sojoji da na ’yan sanda.
“Cafke wannan kwamanda babban ci gaba ne wajen murƙushe ayyukan ta’addanci da ƙungiyar IPOB ke aikatawa, musamman a yankunan da suke hana zaman lafiya,” in ji majiyar.
Kungiyar IPOB, wacce ke fafutukar ballewa daga Najeriya don kafa ƙasar Biyafara, ta kasance a gaba-gaba wajen aikata hare-hare da ta da tarzoma a jihohin kudu maso gabas, musamman ta hannun sashen rundunar da suka kafa da kansu mai suna Eastern Security Network (ESN).
Ana dai zargin cewa Eze yana ɗaya daga cikin jagororin da ke tsara harin kwantan bauna, da hana zirga-zirga a wasu sassan yankin, wanda hakan ya jefa al’umma cikin fargaba da zaman ɗar-ɗar.
Wannan nasara na zuwa ne bayan makonni kaɗan da wata kotu a ƙasar Finland ta yanke wa Simon Ekpa, wani babban jigo a ƙungiyar IPOB, hukuncin ɗaurin shekaru shida a gidan yari kan laifukan da suka shafi ta’addanci da tayar da zaune tsaye.
Masu sharhi na ganin cewa cafke Gentle de Yahoo wata alama ce da ke nuna cewa ana shirin ragargaza ƙungiyar IPOB gaba ɗaya, duk da cewar har yanzu akwai sauran rina a kaba, musamman ganin cewa wasu sassan yankin na ci gaba da fuskantar matsalolin tsaro.