Birnin Kudu Za Ta Samar Da Cibiyar Horas Da Maniyata
Published: 6th, May 2025 GMT
Karamar Hukumar Birnin Kdu tace tana nazarin samar da cibiyar horas da maniyyata aikin hajji ta dindindin a yankin domin karawa mahajjata kaimi wajen gudanar da aikin karbabbe.
Shugaban Karamar Hukumar, Alhaji Muhammad Uba Builder ya bada wannan tabbacin a lokacin rufe bitar da aka shiryawa maniyyatan yankin na Birnin kuudu.
Yana mai cewar, idan aka samar da cibiyar zata kunshi dukkanin muhimman wuraren da ake ziyarta a lokacin gudanar da aikin hajji.
Alhaji Muhammad Uba, yace za a kuma samar da ajujuwan horas da maniyyata da ofisoshin malaman bita da sauran dukkan abubuwan daya dace a cibiyar.
Kazalika, Shugaban Karamar Hukumar, ya biya malaman bitar alawus dinsu na wannan shekarar da ma kwanton na shekarar da ta gabata wanda ya gada daga gwamnatin da ta gabata.
A don haka, ya bukaci maniyyatan yankin su gudanar da addu’o’in neman zaman lafiya mai dorewa da karuwar arziki ga yankin da jihar Jigawa da ma kasa baki daya.
A jawabin da ya gabatar, jagoran malaman da suka gabatar da bitar Malam Suleiman Datti ya bukaci shugaban Karamar Hukumar ya taimaka wajen kara yiwa malaman bitar rijista a yankin.
Wasu daga cikin maniyyatan sun bayyana gamsuwa dangane da yadda Karamar Hukumar ta dauki nauyin ciyar da su na tsawon wata guda baya ga sauran hidimomin da aka yi masu.
Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, fiye da maniyyata dari ne zasu gudanar da aikin hajjin bana daga karamar Hukumar ta Birnin kudu.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Karamar Hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana
Rundunar sojin kasar Sin (PLA) ta yi sintiri a yankin tekun kudancin Sin daga ranar 3 zuwa 4 ga wata.
Kakakin rundunar PLA ta kudancin kasar Tian Junli ya bayyana a yau Litinin cewa, kasar Sin ta dauki matakin ne biyo bayan matakan Philippines na sanya kasashen dake wajen yankin cikin abun da ta kira da sintirin hadin gwiwa, wanda ke neman lalata zaman lafiya da kwanciyar hankalin yankin.
A cewarsa, dakarun rundunar ta kudancin kasar za su ci gaba da kasancewa cikin shirin ko-ta-kwana da kare ikon kasar kan yankunanta da muradunta na teku ba tare da yin kasa a gwiwa ba, yana mai cewa za a dakile duk wani matakin soja dake nemen tada hankali da rikici a yankin. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp