Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-04@21:25:59 GMT

Birnin Kudu Za Ta Samar Da Cibiyar Horas Da Maniyata

Published: 6th, May 2025 GMT

Birnin Kudu Za Ta Samar Da Cibiyar Horas Da Maniyata

Karamar Hukumar Birnin Kdu tace tana nazarin samar da cibiyar horas da maniyyata aikin hajji ta dindindin a yankin domin karawa mahajjata kaimi wajen gudanar da aikin karbabbe.

 

Shugaban Karamar Hukumar, Alhaji Muhammad Uba Builder ya bada wannan tabbacin a lokacin rufe bitar da aka shiryawa maniyyatan yankin na Birnin kuudu.

 

Yana mai cewar, idan aka samar da cibiyar zata kunshi dukkanin muhimman wuraren da ake ziyarta a lokacin gudanar da aikin hajji.

 

Alhaji Muhammad Uba, yace za a kuma samar da ajujuwan horas da maniyyata da ofisoshin malaman bita da sauran dukkan abubuwan daya dace a cibiyar.

 

Kazalika, Shugaban Karamar Hukumar, ya biya malaman bitar alawus dinsu na wannan shekarar da ma kwanton na shekarar da ta gabata wanda ya gada daga gwamnatin da ta gabata.

 

A don haka, ya bukaci maniyyatan yankin su gudanar da addu’o’in neman zaman lafiya mai dorewa da karuwar arziki ga yankin da jihar Jigawa da ma kasa baki daya.

 

A jawabin da ya gabatar, jagoran malaman da suka gabatar da bitar Malam Suleiman Datti ya bukaci shugaban Karamar Hukumar ya taimaka wajen kara yiwa malaman bitar rijista a yankin.

 

Wasu daga cikin maniyyatan sun bayyana gamsuwa dangane da yadda Karamar Hukumar ta dauki nauyin ciyar da su na tsawon wata guda baya ga sauran hidimomin da aka yi masu.

 

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, fiye da maniyyata dari ne zasu gudanar da aikin hajjin bana daga karamar Hukumar ta Birnin kudu.

 

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Karamar Hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Mun kori jami’ai fiye da 100 cikin shekara guda — DSS

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta bayyana cewa ta sallami jami’anta fiye da 100 a tsakanin shekarar 2024 zuwa 2025, a wani yunƙuri na aiwatar da gyare-gyare a cikin hukumar.

Cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, DSS ta ce jimillar jami’ai 115 ta sallama daga aiki saboda dalilai daban-daban da suka shafi aiwatar da tsare-tsaren sabunta tsarin aiki.

Fitaccen ɗan wasan tseren motoci Jenson Button zai yi ritaya Barazanar Trump: Ba ma so a ƙirƙiri wata Sudan ɗin a Nijeriya — Tuggar

Sanarwar wadda ta wallafa a shafinta na yanar gizo, ta ce an fitar da sunaye da hotunan jami’an da abin ya shafa domin ankarar da jama’a.

“A wani ɓangare na ci gaba da aiwatar da gyare-gyare a hukumar DSS, an sallami jami’ai 115. Don haka ana gargaɗin jama’a da su guji yin hulɗa da waɗannan mutanen da aka sallama daga aiki,” in ji sanarwar.

Hukumar ta ce wannan mataki na daga cikin ƙoƙarinta na tsaftace hukumar da tabbatar da ingantaccen aiki da gaskiya a tsakanin jami’anta.

Fuskokin wasu daga cikin jami’an da DSS ta sallama daga aiki

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HOTUNA: Mun kori jami’ai fiye da 100 cikin shekara guda — DSS
  • KADUNA TA ZAMA JIHAR FARKO A NIJERIYA DA TA AIWATAR DA SHIRIN SAMAR DA ABINCIN MAI GINA JIKI GA YARA – UNICEF
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • Uwargidan Gwamnan  Zamfara Ta Yaba Wa  Karamar Hukumar Gusau Bisa Shirin Tallafawa Jama’a
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Yabawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Hanyoyi A Fadin Jihar
  • Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi
  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa