Aminiya:
2025-05-06@14:54:57 GMT

An kashe mutum 6 a sabon hari a Filato

Published: 6th, May 2025 GMT

Akalla mutum shida ne aka tabbatar da mutuwarsu a wani sabon hari Karamar Hukumar Barikin Ladi da ke Jihar Filato.

’Yan bindigar sun kuma jikkata mutane da dama a hare-haren da suka kai unguwannin  Marit da Gashish a ranar Litini.

Aminiya ta samu labarin cewa an garzaya da wadanda suka ji raunin asibiti, bayan harin da aka kai a yayin da mutane suke tsaka da barci a cikin dare.

Shugaban Karamar Hukumar Barikin Ladi, Hon. Stephen Pwajok Gyang, ya bayyana cewa an riga an yi jana’izar mamatan yana mai yin Allah wadai da harin.

Hajj 2025: Maniyyatan Kaduna za su fara tashi ranar 14 ga watan Mayu Wata mata ta auri maza biyu a lokaci guda a Kano NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ‘Yan Gwagwarmaya Ke Shiga Tasku A Najeriya?

A yayin ziyarar dubiya da ya kai Babban Asibitin Barikin Ladi, Hon. Pwajok ya nuna takaici bisa yadda bata-gari ke mayar da hannun agogo, duk da kokarin da hukumomi ke yi na tabbatar da zaman lafiya a karamar hukumar.

Ya yi wa majinyata addu’ar samun sauki da kuma rahama ga mamata, tare da jinjina wa kokarin ’yan banga da sauran jam’an tsaro a yankin.

Wannan hari na zuwa ne makonni kadan bayan makamancinsa a yankin Bassa da Bokkos inda aka kashe sama da mutum dari ciki har da mata da kananan yara.

Hare-haren dai sun biyo bayan rahoton harbe-harbe da kuma kashe dabbobi ta hanyar guba a yankunan kananan hukumomin Bassa da Riyom da kuma Mangu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barikin Ladi hari

এছাড়াও পড়ুন:

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

Lamarin ya tayar da hankali a unguwar, inda wasu matasa suka yi yunƙurin kai farmakar Saudat.

Amma jami’an tsaro sun isa wajen a kan lokaci, suka ceci amaryar tare da kai ta wajen hukuma.

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 6 A Ƙauyukan Filato, Sun Jikkata Wasu
  • AU, ta yi tir da harin baya bayan nan a tashar ruwan Sudan
  • Amurka sake kai sabon hari kan kasar Yemen
  • Boko Haram ta kashe sojoji 4 a Yobe
  • Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna
  • An Kammala Zaben Kananan Hukumomi A Kasar Lebanon A Yau Lahadi
  • Dakarun Kai Daukin Gaggawa Sun Kashe Fararen Hula Kusan 300 A Hare-Haren Baya-Bayan Nan A Sudan
  • Boko Haram ta kashe sojoji huɗu a Yobe