An kashe mutum 6 a sabon hari a Filato
Published: 6th, May 2025 GMT
Akalla mutum shida ne aka tabbatar da mutuwarsu a wani sabon hari Karamar Hukumar Barikin Ladi da ke Jihar Filato.
’Yan bindigar sun kuma jikkata mutane da dama a hare-haren da suka kai unguwannin Marit da Gashish a ranar Litini.
Aminiya ta samu labarin cewa an garzaya da wadanda suka ji raunin asibiti, bayan harin da aka kai a yayin da mutane suke tsaka da barci a cikin dare.
Shugaban Karamar Hukumar Barikin Ladi, Hon. Stephen Pwajok Gyang, ya bayyana cewa an riga an yi jana’izar mamatan yana mai yin Allah wadai da harin.
Hajj 2025: Maniyyatan Kaduna za su fara tashi ranar 14 ga watan Mayu Wata mata ta auri maza biyu a lokaci guda a Kano NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ‘Yan Gwagwarmaya Ke Shiga Tasku A Najeriya?A yayin ziyarar dubiya da ya kai Babban Asibitin Barikin Ladi, Hon. Pwajok ya nuna takaici bisa yadda bata-gari ke mayar da hannun agogo, duk da kokarin da hukumomi ke yi na tabbatar da zaman lafiya a karamar hukumar.
Ya yi wa majinyata addu’ar samun sauki da kuma rahama ga mamata, tare da jinjina wa kokarin ’yan banga da sauran jam’an tsaro a yankin.
Wannan hari na zuwa ne makonni kadan bayan makamancinsa a yankin Bassa da Bokkos inda aka kashe sama da mutum dari ciki har da mata da kananan yara.
Hare-haren dai sun biyo bayan rahoton harbe-harbe da kuma kashe dabbobi ta hanyar guba a yankunan kananan hukumomin Bassa da Riyom da kuma Mangu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barikin Ladi hari
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi
Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya amince da naɗa Hon. Ismaila Ahmed Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi, bayan rasuwar Alhaji Isa Bunuwa Madugu Ibn Kaji.
Sabon Sarkin na Gudi, Ismaila Ahmed Gadaka, ya shahara da ƙwarewa a fannoni da dama.
Sojoji sun ceto malamin Jami’a da aka sace a Taraba Ma’aikatan jinya sun dakatar da yajin aiki a faɗin NajeriyaYa taɓa zama ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Fika/Fune daga 2011 zuwa 2019, kuma kafin nan ya yi aiki a matsayin Kwamishina a Jihar Yobe daga 2007 zuwa 2010.
Gadaka, ƙwararren ma’aikacin banki ne, inda ya yi aiki da bankuna irin su UBA da Standard Trust Bank, inda ya kai matsayin Manajan Kasuwanci.
Kafin naɗa shi Sarki, ya riƙe sarautar Yariman Gudi, a masarautar.
Yanzu haka, yana shugabantar hukumar gudanarwar Kwalejin Ilimi ta Tarayya da ke Yawuri, a Jihar Kebbi, da kuma Kwamitin Kula da Ayyukan Gwamnatin a Ƙananan hukumomin Jihar Yobe tun daga 2024.
Gwamna Buni, ya bayyana cewa yana da tabbacin sabon Sarkin zai kula da martabar masarautar Gudi, ya kuma tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan al’umma.
Ya kuma aike da saƙon ta’aziyyarsa ga masarautar Gudi da iyalan marigayi Sarkin, tare da taya sabon Sarkin murna bisa wannan sarauta da ya samu.