An kashe mutum 6 a sabon hari a Filato
Published: 6th, May 2025 GMT
Akalla mutum shida ne aka tabbatar da mutuwarsu a wani sabon hari Karamar Hukumar Barikin Ladi da ke Jihar Filato.
’Yan bindigar sun kuma jikkata mutane da dama a hare-haren da suka kai unguwannin Marit da Gashish a ranar Litini.
Aminiya ta samu labarin cewa an garzaya da wadanda suka ji raunin asibiti, bayan harin da aka kai a yayin da mutane suke tsaka da barci a cikin dare.
Shugaban Karamar Hukumar Barikin Ladi, Hon. Stephen Pwajok Gyang, ya bayyana cewa an riga an yi jana’izar mamatan yana mai yin Allah wadai da harin.
Hajj 2025: Maniyyatan Kaduna za su fara tashi ranar 14 ga watan Mayu Wata mata ta auri maza biyu a lokaci guda a Kano NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ‘Yan Gwagwarmaya Ke Shiga Tasku A Najeriya?A yayin ziyarar dubiya da ya kai Babban Asibitin Barikin Ladi, Hon. Pwajok ya nuna takaici bisa yadda bata-gari ke mayar da hannun agogo, duk da kokarin da hukumomi ke yi na tabbatar da zaman lafiya a karamar hukumar.
Ya yi wa majinyata addu’ar samun sauki da kuma rahama ga mamata, tare da jinjina wa kokarin ’yan banga da sauran jam’an tsaro a yankin.
Wannan hari na zuwa ne makonni kadan bayan makamancinsa a yankin Bassa da Bokkos inda aka kashe sama da mutum dari ciki har da mata da kananan yara.
Hare-haren dai sun biyo bayan rahoton harbe-harbe da kuma kashe dabbobi ta hanyar guba a yankunan kananan hukumomin Bassa da Riyom da kuma Mangu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barikin Ladi hari
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kai hari sakatariyar ’yan jarida ta jihar Yobe
Wasu ’yan bindiga da ba a san ko su waye ba sun kai hari a sakatariyar Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) da ke Damaturu, babban birnin jihar Yobe, da sanyin safiyar Juma’a.
Rahotanni sun ce yayin harin, maharan sun harbi wani jami’in ɗan sanda da ke gadin sakatariyar suka ji masa rauni ƙafa.
An dakatar da shugabannin sakandare 6 a Sakkwato kan zargin cin amanar aiki Amurka ta hau kujerar-na-ƙi kan buƙatar MDD ta tsagaita wuta a GazaLamarin dai ya faru ne da misalin ƙarfe 2:00 na dare, inda maharan suka buɗe wuta.
Shugaban ƙungiyar NUJ reshen jihar, Rajab Ismail Mohammed, ya bayyana harin a matsayin abin tayar da hankali da kuma babbar barazana ga lafiyar ’yan jarida a jihar.
Ya yi kira ga jami’an tsaro da su gaggauta gudanar da bincike kan lamarin tare da gurfanar da maharan a gaban kotu.
Ƙungiyar ta kuma yi kira ga hukumomi da su ƙara ƙaimi wajen samar da tsaro ga ƙwararrun kafafen yaɗa labarai da cibiyoyin yaɗa labarai a faɗin jihar, inda ta jaddada cewa irin waɗannan hare-hare na iya kawo cikas ga ’yancin ’yan jarida da kuma samun damar yin amfani da bayanan jama’a.
Ƙungiyar ta jaddada cewa kare ‘yan jarida na da matuƙar muhimmanci ga ci gaban dimokuraɗiyya da riƙon amanar jama’a.
Yanzu haka dai dan sandan da aka harba na can a sashin gaggawa na asibitin ’yan sanda da ke Damaturu.
Rahotanni sun ce hukumomin ’yan sanda sun fara gudanar da bincike domin gano waɗanda ke da hannu a lamarin.