2025-05-21@16:30:43 GMT
إجمالي نتائج البحث: 3334

«Hajiya Asta Shehu Timta»:

(اخبار جدید در صفحه یک)
    Iran ta yi kira da a kawo karshen neman shafe wata al’umma daga kan doron kasa tare da kawo karshen rashin hukunta shugabannin ‘yan sahayoniyya Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi kakkausar suka kan hare-hare da laifukan da gwamnatin ‘yan sahayoniyya take ci gaba da yi a cikin ‘yan kwanakin nan a zirin Gaza, yana mai kira da a kawo karshen kisan kiyashi da rashin hukunta shugabannin gwamnatin ‘yan shayoniyya da kuma gurfanar da su a gaban kuliya don hukunta su. Baqa’i ya yi ishara da laifuffukan da ba a taba ganin irinsa ba da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta yi kan al’ummar Falastinu da ba su da kariya a Gaza da Yammacin Gabar Kogin Jordan, ya...
    Wani hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum 37 a ƙauyen Gbajibo-Mudi da ke Ƙaramar Hukumar Kaiama ta Jihar Kwara. Hatsarin wanda ake fargabar ya auku ne a sanadiyar ɗaukar fasinjoji fiye da kima ya faru ne da yammacin ranar Alhamis da ta gabata. Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027? Ainihin abin da ya faru da ɗan wasan Nijeriya Taiwo Awoniyi Lamarin na zuwa ne watanni bakwai bayan aukuwar makamancinsa wanda ya janyo asarar fiye da mutum 106 a jihar. A cewar wani mazaunin yankin, kwale-kwalen wanda ya ɗauko fasinjoji kimanin 150 ya kife ne a tsakiyar ruwa. Bayanai sun ce waɗanda lamarin ya rutsa da su na komawa gida ne bayan cin kasuwa a tsallake...
    Hukumomin kasar za su fitar da gamsasshen bayani mai dauke da sababbin tsauraran matakan, wadanda za su kunshi na mallakar izinin karatu da aiki a Birtaniya. Sakataren harkokin baki na Birtaniya Ybette Cooper ta bayyana wa BBC cewa lokaci ya yi da za su rage daukar ma’aikatan jinya daga kasashen waje. Ta ce wannan matakin zai taimaka wajen rage kusan mutum 50,000 wadanda ba kwararru ba ne sosai da suke shiga kasar daga kasashen ketare a duk shekara. Firaministan ya ce sababbin matakan za su taimaka wajen “sake mallake bakin iyakokin kasarmu.” Idan aka dabbaka sabbin matakan nan da gwamnatin kasar za ta dauka, ‘yan kasashen mutane daga kasashen Nijeriya da Pakistan da Sri Lanka za su fuskanci kalubale wajen...
    Dare da aka zubar da jini mafi muni a Gaza: Sama da Falasdinawa 80 ne suka yi shahada a sassa daban-daban na Zirin Sojojin mamayar Isra’ila suna ci gaba da aiwatar da kisan kiyashi kan fararen hula a yankuna daban-daban na zirin Gaza, inda suka yi sanadiyyar shahadan sama da Falasdinawa 80, kuma mafi yawansu a wani kisan kiyashi da aka yi wa ‘yan gudun hijira a yankin Al-Mawasi na Khan Yunus da ke kudancin zirin Gaza, bayan da aka jefa bama-bamai da kona tantunansu a kusa da Asibitin kwararru na Kuwait, baya ga kisan kiyashi a duk fadin yankin. Majiyoyin Falasdinawa sun ce an kona mutane 36, yawancinsu mata da kananan yara, bayan da sojojin mamayar Isra’ila suka yi...
    Sojojin Libiya sun ‘yantar da fursunoni da dama daga gidajen yari na sirri da ke karkashin dakarun Tallafawa da Wanzar da Kwanciyar hankali na Kasar Sojojin kasar Libya a birnin Tripoli fadar mulkin kasar sun ‘yantar da fursunoni da dama da ake tsare da su a gidajen yari na sirri karkashin hukumar “Tallafawa da wanzar da zaman lafiya” bayan sun kwace iko da wasu helkwatar tsaro a babban birnin kasar. ‘Yanto fursunonin ya biyo bayan fitar da faifan bidiyo da sojojin Libiya da ma’aikatar harkokin cikin gidan kasar suka yi ne da ke nuna lokacin da aka ‘yantar da fursunonin. Hotunan sun nuna akwai dakunan tsare mutane ba bisa ka’ida ba da kuma gidajen yari da ake amfani da su...
    Sauran sassan da aka gyara da kuma saka kayan aiki sun haɗa da sashen Kulawa da Mata (ANC), ɗakin tiyata, ɗakin X-ray, sabon ginin hukunta asibiti, masallaci, gidan Babban Daraktan Lafiya (gidaje mai ɗakuna 3), da kuma sashen kula da yara, da dai sauransu.   A yayin jawabinsa a wajen ƙaddamar da aikin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, an kammala gyaran gine-ginen tare da sanya dukkan kayan aikin kiwon lafiya cikin kwangilar cikin watanni 12. Gwamnan ya ce, “A shekarar da ta gabata ne aka fara gyaran wannan asibitin, kuma wani kamfanin cikin gida ne aiwatar da kwangilar.   “Saba hannun jarin ya mayar da asibitin zuwa wurin kiwon lafiya na zamani tare da na’urori na zamani, wannan ba...
    An yi wa ɗan wasan gaba na ƙungiyar Nottingham Forest, Taiwo Awoniyi allurar barci mai nauyi domin taimaka masa murmurwa daga tiyatar da aka yi masa. Bayanai sun tabbatar cewa an garzaya da ɗan wasan ɗan asalin Nijeriya asibiti ne domin yi masa tiyata a ranar Litinin, bayan ya samu mummunan rauni a cikinsa a wasan da suka tashi canjaras, 2-2 da Leicester a Gasar Premier ta Ingila. Motar da aka shekara 10 ana tara kuɗinta ta ƙone bayan awa 1 da sayen ta Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027? Alamu sun nuna cewa rayuwar ɗan wasan mai shekara 27 ba ta cikin haɗari, kuma allurar barcin da aka yi masa za ta taimaka ne...
    A cewarsa, baban dalilin da ya sa suke wannan aiki shi ne, domin a rage wa al’umma musamman masu karamin karfi wahalwalun da suke sha wajen neman lafiya. Malam Hussaini ya yi kira ga sauran kungiyoyi da masu hannu da shuni da su ba da tasu gudummawa wajen irin wannan aiki ta yadda za su taimaka wa kokarin gwamanti kan harkokin kiwon lafiya. Wasu daga cikin wadanda suka amfana da wannan taimako na aikin kaba sun yaba da kokarin wannan gidauniya, inda suka ce hakan zai taimaka wa kokarin gwamanti da sauran kungiyoyi da masu hannu da shuni da su yi ko yi da wannan gidauniya. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun...
    Babbar Jam’iyyar hamayya ta PDP ta ce, ta soma ɗaukar matakan ɗinke ɓarakar da ta dabaibaye ta a ’yan shekarun nan. Matakin baya-bayan nan shi ne na taron masu ruwa da tsaki da jam’iyyar ta gudanar. Guguwar raba Masarautar Katsina ta kunno kai Tinubu ya isa Rome don rantsar da sabon Fafaroma Shin ko hakan zai kawo ƙarshen matsalolin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan faɗuwa zaɓen 2023? Daga cikin matsalolin da suka kunno kai a cikin babbar Jam’iyyar adawa ta PDP tun bayan faduwarta zaɓe a 2023 shi ne yin baram-baram a kan yadda za ta dinke barakar da aka samu a lokacin zaben fidda-gwani da rikicin shugabanci a matakai daban-daban da kuma kasa tsayawa da kafarta domin samar...
    Bayan da wani matashi ɗan shekara 33 ɗan kasar Japan mai suna Honkon ya yi tarin kuɗi na tsawon shekaru 10 don siyan motar da yake mafarki — na wata sabuwar mota ƙirar Ferrari 458 Spider — sai ya zauna yana kallon yadda motar take ƙonewa cikin sa’a ɗaya da tuƙa ta a karon farko. Kafofin sada zumunta na ƙasar Japan sun yi sharhi game da rahoton baƙin ciki na Honkon, matashin da ya kasance mai shirya wakoki, wanda ya kashe makudan kuɗi game da mafarkin sayan motarsa ta Ferrari, sai dai ya kalle ta tana ci da wuta a ranar da ya tuƙa ta a karon farko. ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno Guguwar raba Masarautar...
    Ya ce da Kwankwaso bai yi tunanin samar da jami’ar Wudil ba, da wannan alherin ba za a same shi ba, suna gode wa sauran wadanda suke ba da gudummawa wajen habakar wannan jami’ar. Alhaji Abdukadir ya yi kira ga magoya baya da masu tasowa cewa idan suka sami dama su yi koyi da jagoran Kwankwasiyya, wanda ya kafa jami’o’i guda biyu a Jihar Kano bayan makarantu na gaba da sakandare guda 24 da ya samar da kuma tura dalibai talakawa karatu kasashen waje da mafi yawa sun gama suna amfanar da ci gaban al’umma. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu...
    Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya caccaki kalaman shugaban Amurka Donald Trump na baya-bayan nan a ziyarar da ya kai a kasashen yankin Gulf na Farisa, yana mai cewa kalaman abin kunya ne a gare shi da dukkan Amurkawa, kuma bai cancanci amsa ba. Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana hakan ne lokacin da ya karbi bakuncin kungiyar masu bayar da ilimi daga sassan kasar.   Ya kara da cewa wasu kalaman na Trump ba su ma isa a mayar da martani ba, yana mai kiransu da cewa abin kunya ne ga shi kansa shugaban Amurka da kuma wulakanci ga al’ummar Amurka. ‘’Ikirarinsa na cewa yana son samar da zaman lafiya da tsaro, zencen...
    An gudanar da zanga-zangar nuna goyon baya ga al’ummar Falasdinu a sassa daban-daban na duniya, a yayin zagayowar cika shekaru 77 da ranar ‘’Nakba’’ cewa da masifa. A Faransa da Ingila duk an gudanar da wannan zanga zanga a wasu sassan kasar. A cikin jerin gwanon, an daga allunan da ke dauke da sakonni irin su “Falasdinu za ta rayu!” » ko “Dakatar da kisan kiyashi a Gaza”. “Nakba ba wani lamari ne da ya faru a baya ba, yana ci gaba da faruwa ta hanyar korar jama’a, da amfani da bama-bamai,” kan al’ummar Gaza. Masu zanga-zangar sun yi Allah wadai da tabarbarewar al’amuran jin kai a zirin Gaza tun bayan barkewar yakin kisan kiyashi da Isra’ila ta kaddamar a...
    Iran ta yi kakkausan suka game da hare-haren da Isra’ila ke ci gaba da kaiwa kan kasar Yemen tana mai danganta su da babban laifin yaki. Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa hare-haren da gwamnatin Isra’ila ke kai wa kan ababen more rayuwa na tattalin arzikin kasar Yemen da kuma cibiyoyin jama’a sun zama “laifi na yaki da cin zarafin bil’adama.” A cikin wata sanarwa da ya fitar a wannan Asabar, Esmail Baghai ya yi kakkausar suka kan hare-haren da gwamnatin Isra’ila ke kaiwa kan manyan tashoshin jiragen ruwa na kasar Yemen. Ya kara da cewa hare-haren da aka kai a tashar jiragen ruwa ta Hudaydah, Ras Issa da kuma Salif na kasar Yemen, ya zama babban...
    Aƙalla manoma 50 ne suka rasu, sakamakon wani mummunan hari da ‘yan ta’addan ISWAP suka kai garin Malam Karanti da ke Ƙaramar Hukumar Kukawa, a jihar Borno. Majiyoyi sun ce mayaƙan sun afka wa manoma yayin da suke noma da kamun kifi, duk da cewar suna biyan haraji kafin yin noma. Tinubu ya isa Rome don rantsar da sabon Fafaroma Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta sani “Sun mallaki takardun izini daga kwamandan ISWAP da ke kula da yankin Malam Karanti har zuwa Dawashi. Sun jima suna samun kariya daga Amir Akilu, wanda shi ne kwamandan yankin,” in ji wani mazaunin yankin. Sai dai harin ya faru ne a lokacin da kwamandan bai kasance a...
    Hukumar kula da ayyukan sama jannati ta kasar Sin ta ce masu bincike sun tabbatar da wata sabuwar halitta da aka samu a cikin tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin, wanda aka yi wa lakabi da Niallia Tiangongensis   A watan Mayun 2023 ne, tawagar ‘yan sama jannati ta kumbon Shenzhou-15 ta gano wani samfurin halitta a cikin tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin yayin da take cikin da’irarta. An kuma adana ta cikin yanayi mai sanyi, sannan daga bisani aka kawo ta duniyar dan Adam domin gudanar da nazari. Kuma bayan binciken kimiyya da ya shafi nazarin sauyawar yanayinta da tsarin kwayar halittarta da sauransu, masana sun tabbatar da cewa sabuwar halitta ce da ba a taba...
    Farfesa Radda ya ce an cire ‘yan takara masu yawa da suka cencenta saboda rashin adalci, duba da cewa sun cika dukkan sharadan da ya dace wajen neman mukamin shugabancin makarantar.  Haka kuma, Farfesa Bichi ya ce zargin da ake masa ba gaskiya ba ne, yana mai cewa an gudanar da zaben cikin gaskiya da adalci kamar yadda doka ta tanada. Dukkan ‘yan takarar sun bayyana gamsuwarsu kan shigowar gwamnatin tarayya cikin lamarin, inda suke yi kira ga ministan ilimi ya sake duba dukkan matakan da da aka bi domin yin gaskiya kamar yadda dokar makarantar ta tanada.    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye...
    Amma mu tambayi kanmu, shin da gaske wannan ita ce hakikanin manufar? Amma bari mu yi la’akari da wannan hasashen mu gani, ko shi ne ya fusata Amurka ta maka harajin kashi 100 bisa 100 kan fina-finai da ake shigar da su daga kasashen waje ko kuma wadanda aka shirya a ketare? Akwai wani kirkirarren fim mai suna ‘Ne Zha 2’ da masana’antar shirya fina-finai ta kasar Sin ta shirya a baya-bayan nan. Kamfanin dillancin labarai na AFP ya bayar da rahoton cewa, wannan fim ya zama na farko da ya samar da Dala biliyan 1 a kudin tikitin shiga a kasuwar cikin gida kadai. Bugu da kari, wannan adadi, ya haura sama da Dala biliyan 2 a kudaden shiga...
    Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya isa birnin Rome na Ƙasar Italiya domin halartar bikin rantsar da sabon Fafaroma, Leo na XIV. Za a gudanar da bikin ne a wajen wani taron addu’a da ake kira “solemn mass” a ranar Lahadi, 18 ga watan Mayu. Crystal Palace ta lashe kofin FA na farko a tarihinta Ban sauya sheƙa ba, makircin siyasa da ƙarya ake min — Kwankwaso  An tarbi Shugaba Tinubu a filin jirgin sojin Mario De Bernardo, inda jakadiyar Najeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu, da jami’an diflomasiyya daga Vatican da ofishin jakadancin Najeriya suka tarbe shi. Tinubu ya samu gayyata ta musamman daga Sakatare Janar na Vatican, Cardinal Pietro Parolin. A cikin wasiƙar gayyatar, Fafaroma Leo XIV ya bayyana cewa ya...
    Farfesa Radda ya ce an cire ‘yan takara masu yawa da suka cencenta saboda rashin adalci, duba da cewa sun cika dukkan sharadan da ya dace wajen neman mukamin shugabancin makarantar.  Haka kuma, Farfesa Bichi ya ce zargin da ake masa ba gaskiya ba ne, yana mai cewa an gudanar da zaben cikin gaskiya da adalci kamar yadda doka ta tanada. Dukkan ‘yan takarar sun bayyana gamsuwarsu kan shigowar gwamnatin tarayya cikin lamarin, inda suke yi kira ga ministan ilimi ya sake duba dukkan matakan da da aka bi domin yin gaskiya kamar yadda dokar makarantar ta tanada.    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Jagoran juyin juya halin musulunci a nan Iran Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya yi watsi da wasu kalaman shugaban kasar Amurka Donal Trump a ziyar da ya kammala a wasu kasashen larabawa na yankin Tekun farisa, ya kuma bayyana wasu kalamansa a matsayin kungiya ga kansa da kuma mutanen Amurka. Har’ila yau Jagoran ya kara da cewa da dama daga cikin maganganunsa basu cancanci maida martani ba. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jagoran yana fadar haka a yau Asabar, a lokacinda yake ganawa da wasu malaman makaransu daga larduna daban daban na kasar, a Husainiyyar Imam Khonaini (q) a nan Tehran. Jagoran ya kara da cewa : Trump yace yana son amfani da karfin da Amurka...
    Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa  aiwatar da yarjeniyar zaman zaman lafiya wadanda aka cimma tsakanin kasashen Armenia da kuma Azerbaijan da gaggawa zai tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a tsakanin kasashen biyu. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ta nakalto Aragchi yana fadar haka a lokacin ganawarsa da sakataren majalisar koli ta tsaron kasar  Armenia, Armen Grigoryan  wanda yake ziyarar aiki a nan Tehran a yau Asabar. Ministan ya kara da cewa JMI zata tabbatar da cewa an aiwatar da sulhu tsakanin kasashen biyu da gaggawa saboda tana dasawa da kasashen biyu makobta gareta. A cikin watan Maris da ya gabata ne kasashen Armenia da Arzerbaijan suka amince a rubuta yarjeniyar...
    Cikin jawabin da ya gabatar ta bidiyo, mataimakin ministan kula da al’adu da yawon bude ido na kasar Sin Rao Quan, ya ce dawowar rubuce-rubucen na Wuxing Ling da Gongshou Zhan, na tabbatar da cewa za a iya nazarta da kare wadannan kayayyakin gargajiya masu daraja yadda ya kamata a mahaifarsu. (Fa’iza) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Kwanan nan ne Majalisar Dinkin Duniya ta fitar da rahoton dake sabunta hasashen yanayin tattalin arzikin duniya gami da makomarsa na shekara ta 2025 a tsakiyar shekarar da muke ciki, inda rahoton ke ganin kara harajin kwastam da rashin sanin tabbas game da manufofin cinikayya sun janyo tabarbarewar makomar tattalin arzikin duk duniya, tare da haifar da tarin kalubaloli ga kasa da kasa, musamman kasashe masu tasowa, ciki har da kasar Sin. Rahoton na hasashen cewa, saurin karuwar tattalin arzikin duniya na bana, zai ragu zuwa kaso 2.4 bisa dari, yayin da saurin karuwar cinikayya zai ragu zuwa kaso 1.6 bisa dari. Kana, rahoton na ganin cewa, daidaita manufofi gami da hadin-gwiwar kasa da kasa, na da muhimmanci gaya ga...
    Jagoran jam’iyyar NNPP, Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ƙaryata wani rahoto da ke yawo cewa yana shirin shiga sabuwar haɗakar siyasa. A wani gajeren saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Asabar, Kwankwaso ya bayyana rahoton a matsayin “karya, ba shi da tushe kuma makircin wasu ‘yan siyasa ne.” Riƙaƙƙun ’yan daba da dilolin ƙwaya 31 sun shiga hannu a Kano Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta sani Ya gargaɗi jama’a da ka da su yarda da irin waɗannan labarai marasa tushe. “An jawo hankalina kan wani rahoto wanda ke bayyana matsayina a haɗin gwiwar siyasa a Najeriya. “Ina so na fayyace cewa irin waɗannan rahotannin ƙarya ne, ba su da tushe kuma...
    Kwamitin Haɗin Gwiwa na Jihar Kano kan Tsaro da Gyaran Matasa, ya kama ’yan daba 31 a wani samame da ya gudana a unguwanni bakwai a jihar. An kai samamen ne daga ranar 10 zuwa 14 ga watan Mayu, 2025 ƙarƙashin jagorancin Dokta Yusuf Ibrahim Kofar Mata. Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta sani Jami’an tsaro sun daƙile harin Boko Haram sun kashe mayaƙa 5 a Borno Unguwannin da aka kai samamen sun haɗa da Ɗorayi, Ja’in, Sharada, Unguwar Dabai, Dukawa, Kabuga, Kofar Mata da sauransu, wuraren da suka yi ƙaurin suna wajen aikata laifuka. Daga cikin waɗanda aka kama, mutum 25 ana zargin ’yan daba ne, yayin da shida ake zarginsu dallacin miyagun ƙwayoyi....
    Tsafta tana kasancewa wani muhimmin ɓangare na rayuwar mace. Duk da cewa galibi ana alaƙanta tsafta da kyawun gani ko ƙamshi, sai dai a zahirin gaskiya tsafta ta wuce gaban haka ce. Ita ce turbar zaman lafiya a gidan aure, makamin janyo soyayya, da ginshiƙin lafiyar jiki da tunani. Hajj: Ranar Lahadi za a fara jigilar maniyyatan Katsina zuwa Saudiyya Gwamnatin Kano ta haramta ‘Ƙauyawa Day’ a lokacin bikin aure Wasu matan na iya cika ido da kwalliya a wajen biki ko taro, amma su kan bar gidansu cikin ƙazanta da rashin tsafta. A wasu lokuta kuma, akwai matan da rashin tsaftarsu ke janyo mutuwar aurensu, rashin kulawa da miji, ko kuma sa mijin ya ɗauki matakin ƙaro aure. Tsafta...
    Mayaƙan ƙungiyar ISWAP sun yi wa manona da masunta aƙalla 15 yankan rago a yankin Baga da ke Ƙaramar Hukumar Kulawa ta Jihar Borno. Rahotanni sun bayyana cewa mayaƙan na ISWAP sun kutsa yankin ne bayan zagargaza da tarwatsa sojoji suka yi wa maɓoyarsu da ke Dajin Sambisa. Shaidu sun bayyana cewa a ranar Laraba da manoman da masunta suka tafi gonakinsu da wurin yin su ne suka yi arba da mayaƙan ƙungiyar da suka yi musu kisan gilla. Sun bayyana cewa dai da mayaƙan suka tafi da manoman zuwa ƙauyen Malam Karanti, da suka kwace, sa’annan sun yi musu yankan rago. Jami’an tsaro sun daƙile harin Boko Haram sun kashe mayaƙa 5 a Borno Budurwa ta guntule mazakutar saurayinta...
    A Premier League, kungiyoyi sun gama sanin Man United ciki da waje. “Dalili shi ne su kan hadu sau biyu duk shekara. Sun san abin da za su tarar game da ‘yanwasan United din da kuma filin wasanta, a gasar zakarun Turai kuma, akasari wannan ne karon farko da suke zuwa filin wasa na Old Trafford da kuma karawa da United. Ba su san yadda ya kamata su tunkare su ba” in ji shi. Sai dai ya ce Manchester United dole sai ta yi da gaske a kan kungiyarTottenham saboda duka daga Ingila suka fito kuma sun hadu da su sau uku a wannan kakar duka Tottenham tana samun nasara kuma Tottenham din ta san lagon Manchester United sosai saboda...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Shugaban kasar Iran ya jaddadacewa: Sun yi Imani da tattaunawa, amma ba su jin tsoron duk wata barazana Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa: Tabbas Iran tana gudanar da zaman tattaunawa da Amurka amma ba ta tsoron duk wata barazanarta, yana mai nuni da kalaman Trump da ke cin karo da juna, wani lokaci yana magana kan zaman lafiya sannan a wasu lokutan yana barazana da yaki. A jawabin da ya gabatar a wajen bikin cika shekaru biyu da samun nasarar tawagar “Rukunin Jirgin Ruwa na 86” na sojojin ruwan Iran, shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yaba da sadaukarwar da jaruman da suka yi wannan hidimar, yana mai cewa: “Suna alfahari da kasancewar dakarunsu, yana mai...
    Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Kiyaye ci gaba da sarrafa sinadarin yuraniyon da tushen kayan aikin makamashin nukiliya ba abubuwa ba ne da za a tattauna a kansu Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana cewa: Iran a shirye take ta samar da kwarin gwiwa dangane da ci gaba da zaman lafiya a shirinta na makamashin nukiliya, amma ba za ta iya tauye hakkin jama’ar Iran na halal da kuma hakkinsu na samar da makamashin nukiliya cikin lumana ba, ciki har da inganta sinadarin yuraniyom domin zaman lafiya ba. A wata ganawa ta hadin gwiwa da tare da tawagar babban taron kasa da kasa na Pugwash da hukumar makamashin nukiliya ta Iran ta shirya a yammacin...
    Asusun kula da kananan yara “UNICEF” na Majalisar Dinkin Duniya ya sanar da cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kashe yara 45 a Gaza cikin kwanaki biyu kacal Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya bayyana cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kashe kananan yara 45 a Zirin Gaza a cikin kwanaki biyun da suka gabata, kuma wani abin tunatarwa shi ne cewa: Yara a Gaza na shan wahala da farko, suna fama da yunwa kowace rana kuma suna fuskantar hare-haren wuce gona da iri da muggan makamai kan mai uwa da wabi.” A cikin wata sanarwa da Asusun ya fitar a ranar Juma’a, ya jaddada yi kira da a kawo karshen wahalhalu da kashe-kashen yara a kullum....
    Tsohon fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ya ce: Fira ministan Netanyahu ya yi sakaci da rayuwar yahudawa a cikin aikinsa don haka hambarar da gwamnatinsa ita ce mafita Tsohon Fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila Ehud Barak ya yi kira da a hambarar da Benjamin Netanyahu da gwamnatinsa, yana mai zarginsa da yin sakaci wajen kubutar da fursunonin yahudawa da suke hannu ‘yan gwagwarmaya a Zirin Gaza. Barak ya ce: Netanyahu yana sakaci da rayuwar fursunonin yahudawa da ake tsare da su a Gaza domin faranta wa masu tsattsauran ra’ayi a gwamnatinsa rai.” Ya bayyana shi a matsayin mai sakaci wajen gudanar da ayyukansa, da kuma ci gaba da kisan kiyashi a Zirin Gaza domin karecmanufofin siyasa saboda neman...
    An samu bullar rikicin da ba a taba ganin irinsa ba a dangantaka tsakanin Aljeriya da Faransa Rikicin ma’aikatan harkokin diflomasiyya tsakanin Aljeriya da Faransa ya dawo kan gaba a fagen dakaddamar da ke tsakaninsu. Rikici dai na kara kamari ne tsakanin Aljeriya da Faransa, tun daga rikicin korar ‘yan kasar Aljeriya daga Faransa zuwa rikicin korar ma’aikatan diflomasiyyar Faransa daga Aljeriya. Kasashen biyu sun tsaya a gaban nauyin tarihin mulkin mallaka ba tare da shawo kan shi ba. Aljeriya ta gayyaci mukaddashin jakadan Faransa domin sanar da shi aniyarta ta korar karin jami’an Faransa da ke aikin taimakon wucin gadi daga kasarta. Wannan kiran ya biyo bayan maimaita cin zarafi mai tsanani da bangaren Faransa ya yi ne, yana...
    Sai ya ce “Na riga na amsa wannan tambayar amma har yanzu kana sake maimaita ta. Idan dai za a iya tunawa, ‘yan jarida 43 mazauna Kaduna ne suka halarci taron, ciki har da wasu ‘yan jarida daga wasu jihohin da suka raka gwamnonin nasu. Don haka, ba daidai ba ne a ce na hana ‘yan jarida shiga taron gwamnonin Arewa. Duk jaridun kasar nan sun je a wurin. Duk gidajen rediyo da talbijin na Kaduna suna wurin. Duk wakilan manyan gidajen Talabijin da Rediyo da ke wajen Kaduna su ma suna nan. Kada ka dauki maganata a wani bangare daban, je ka bincika. Duk wadannan labarai ne irin na teburin mai shayi. Ni kuma ban sani ba. Abin da...
    “Dangote ya taka muhimmiyar rawa wajen kawo ci gaba wanda ya cancanci yabo. Muna kan tattauna yadda za a kawo karshen rigimar. Nan gaba, za mu yi aikin hadin gwiwa domin tabbatar da samar da wadataccen mai ga al’ummar Nijeriya,” in ji shi. Ya nuna cewa ta hanyar zaman sulhu za su kawo karshen matsalar, “Nan gaba kadan ba za ku ji wata rigima tsakanin NNPCL da matatar mai ta Dangote ba. Za mu yi aikin hadin guiwa domin amfanuwar ‘yan kasa.” Ojulari ya kuma yi tsokaci kan faduwar farashin danyen mai a duniya a baya-bayan nan, wanda ya rage kudaden shiga da ake sa ran Nijeriya za ta samu. “Wannan raguwar ta shafi kasafin kudin Nijeriya tun da babban...
    Habakar matsayi na kasafin kudi ya inganta a cikin 2024, ta hanyar habaka kudaden shiga. Gibin kasafin kudi ya ragu daga kashi 5.4 na kudin shiga a shekarar 2023 zuwa kashi 3.0 na kudin shiga a shekarar 2024, babban ci gaban da aka samu sakamakon karuwar kudaden shiga na daukacin tarayyar kasar, wanda ya karu daga naira tiriliyan 16.8 a shekarar 2023 (7.2 na kudaden shiga) zuwa kimanin naira tiriliyan 31.200. Rahoton ya kara da cewa hauhawar farashin kayayyaki ya tsaya tsayin daka amma ana sa ran zai fadi zuwa matsakaicin shekara da kashi 22.1 cikin 100 a shekarar 2025, yayin da tsayin daka mai tsayi ya tabbatar da amincin manufofin kudi tare da rage tsammanin hauhawar farashin kayayyaki. Ko...
    Sai dai dan majalisar wakilai Ali Isah na (PDP, Gombe), bai amince da matsayin Madaki ba. Ya ce sanya shugaban kasa na a tsarin karba-karba a cikin kundin tsarin mulkin kasar zai samar da adalci da sanin ya kamata ga dukkan shiyyoyin siyasar kasar nan. Dan majalisa Sada Soli na (APC, Katsina), yayin da yake adawa da kudurin, ya ce dokar da aka gabatar “Na da illa sosai ga hadin kan kasa.” Ya ce sanya ka’idar shugabancin karba-karba a cikin kundin tsarin mulkin kasar zai kai ga samar da abubuwa bisa cancanta. “Hakan zai iya sanya muradun yanki da na kabilanci a gaba su zamo mafi cancanta. Zai karfafin zabin mutanen da za su iya tsayawa takara kuma zai kara...
    Wata mata da age zargin ta cije mazakutar saurayinta ta shiga hannun ’yan sanda. Rundunar ’Yan Sandan Jihar Ribas ta kama matar mai shekara 43 ne bayan ta yi wa masoyin nata wannan aika-aika ne a lokacin da suke rikici a cikin gida a unguwar Mile 3 da ke yankin Diobu a garin Fatakwal babban birnin jihar. Lamarin wanda ya afku a ranar Alhamis, ya girgiza mazauna titin Bishop Okoye mai yawan jama’a lokacin da aka samu labarin lamarin. A cewar majiyoyi, rikicin ya fara ne lokacin da masoyin matar ya nemi kwanciya da ita. An bayar da rahoton cewa matar ta ƙi amincewa da buƙatar saurayin nata, inda ta zarge shi da yin amfani da ƙwayoyin masu ƙara kuzarin...
    Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu ta sanar da cewa adadin wadanda suka yi shahada a yakin da Isra’ila ke ci gaba da yi a zirin Gaza ya kai 53,119 tun daga ranar 7 ga Oktoba, 2023. Adadin ya karu ne sakamakon wasu hare-haren Isra’ila na baya baya nan wanda ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa 93 wayewar safiyar Juma’a. A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a, ma’aikatar ta ce an kuma mika wasu mutane fiye da 200 da suka jikkata zuwa asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya a zirin Gaza, biyo bayan hare-haren wuce gona da iri da sojojin Isra’ila suka kai a yankuna da dama. A cikin sa’o’i 24 da suka gabata, an sami rahoton mutuwar mutane 109 da...
    “Amma sai ku ga cewa daya bayan daya, mun magance yawancin wadannan matsalolin. Har yanzu akwai sauran aiki a gabanmu, amma muna kan samun nasarori.” Da yake jawabi a wajen taron, wakilin AON, Obiora Okonkwo ya yi maraba da wannan sabon ci gaban, inda ya bayyana cewa zai inganta ayyukansu. A cewarsa, “Abin da muke gani a nan a yau wani babban ci gaba ne daga jerin abubuwa da dama.” Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Adadin kudaden harkar soji a nahiyar Afirka a bara, musamman a Aljeriya da kasashen kawancen Sahel, ya karu. A cewar wani bincike da Cibiyar Nazarin Zaman Lafiya ta Duniya ta Stockholm (SIPRI) ta gudanar, kashe kudaden soji a Afirka ya karu zuwa dala biliyan 52.1 a shekarar 2024 a fadin Nahiyar, wanda ya karu da kashi 3 bisa 100 a shekarar 2023 da kuma karuwar kashi 22 cikin 100 a shekarar 2015. A cewar rahoton na SIPRI, kudaden da ake kashe wa sojojin na Arewacin Afirka ya kai dala biliyan 30.2 a shekarar 2024, ya kuma karu da kashi 4 cikin 100 a shekarar 2024. Kudaden da Aljeriya da Maroko kadai suka kashe ya kai kashi 90% na adadin kudaden...
    A lokacin da yake jawabi a wurin ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya bayyana cewa da hawansa mulki a watan Mayun 2023, ya ci karo da tsarin kiwon lafiya da ya tabarbare saboda rashin kulawa. Ya ce, “Gwamnatinmu, ƙarƙashin ginshiƙan shirye-shiryen ceto, nan da nan ta fara tantance abubuwan da asibitoci ke buƙata, inda sakamakon ya zama abin tsoro kuma ya nuna akwai jan-aiki. “Alal misali, a jihar da ke da mutane kusan miliyan 6 tare da tarin ƙalubale, na’urar duban ɗan tayi ɗaya ce kawai a cikin dukkan cibiyoyin da gwamnati ta mallaka, kuma shi ma duk faci ne a jikinsa da salataf ko’ina! Nan take na ayyana dokar ta-baci a bangaren kiwon lafiya don dawo da ababen more rayuwa, samar...
    Aƙalla mutum biyar ne sun jikkata bayan da gobara ta tashi a gidan man Nobpet da ke kusa da mahaɗar Sojojin Sama a garin Fatakwal, Jihar Ribas. Gobarar ta kuma ƙone sama da motoci takwas da aka ajiye kusa da ofishin Hukumar Sufuri ta Jihar Ebonyi. Sojoji sun kashe ’yan bindiga da ƙwato shanun sata 1000 a Taraba  Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro Ma’aikatan kashe gobara na Jihar Ribas tare da haɗin gwiwar na Sojojin Sama ne suka yi aiki tare har suka iya kashe gobarar. Ɗaya daga cikin waɗanda abin ya shafa, Emmanuel Ninyaegwu, wanda direba motar haya ne, ya ce motarsa mai ɗaukar fasinja 18 ta ƙone gaba ɗaya. Ya...
    Ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriryar musulunci ta Iran ta sanar da cewa, saboda yadda Amurka take bai wa ‘yan sahayoniya cikakken goyon baya ne, ya sa su cigaba da aikata laifuka na kisan kiyashi akan mutanen Gaza. Bayanin da ma’aikatar harkokin wajen ta Iran ta fitar, ya zo ne  saboda tunawa da zagayowar lokacin da aka kori Falasdina aka kirkiri HKI, wanda ake kira da “Nakba” ta bayyana cewa; Falasdinawa ne suke da hakkin ayyana makomarsu,kuma nauyi ne na doka da halin kwarai akan kasashen duniya su takawa HKI birki akan kisan kiyashin da take yi a Gaza. Bayanin ya sake jaddada kira da gabatar da masu hannu a kisan kiyashin al’ummar Gaza a gaban kotu domin su fuskanci sakamakon laifukan...
    A cewarsa, ba ga wannan akwai shirin kawo sauyi kan manyan kalubale da suka hada da lalata na’urorin wutar lantarki, gudanarwa, matsalolin yankuna da suke janyo cikas ga gudanar da ayyuka. Ya umarci hukumar kula da wutar lantarki a Nijeriya (NERC) da ta tabbatar kamfanonin rabar da wutar lantarki sun bayar da hadin kan da ake bukata domin samun nasarar gudanar da aikin. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Shugaban hukumar Spain Pedro Sanchez ya bayyana ” Isra’ila” da cewa; “Mai Kisan Kiyashi Ce,” wacce kasarsa ba za yi mu’amala da ita ba. Fira ministan na kasar Spain ya bayyana hakan ne a matsayin mayar da martnni ga wani dan majalisar kasar daga yankin Catalonia, Gabrel Rovian yana wanda ya tuhume shi da cewa, yana huldar kasuwanci da Isra’ila,alhali tana yi wa mutanen Gaza kisan kiyashi. Kafafen watsa labarun Spain sun ce wannan shi ne karon farko da firma ministan kasar ya bayyana abinda Isra’ila take yi da cewa kisan kiyasn kare dangi ne. HKI ta fusata akan furucin da Fira ministan Spain tare da kiran jakadan kasar  domin nuna masa rashin amincewa.
    Da safiyar yau Juma’a ne dai jami’an tsaron kasar Chadi su ka kai wani farmaki na   kama tsohon fira minista kuma jagoran ‘yan hamayyar siyasar kasar Succès Masra. Jam’iyyar hamayya da Masra yake jagoranta, ta bayyana abinda jami’an tsaron su ka yi wa jagoran nata da cewa, garkuwa ce.  Ita kuwa hukumar kasar ba ta fitar da wani bayani akan kamun Masra ba,wanda shi ne ya zo na uku a zaben shugaban kasar da aka gudanar a shekarar da ta gabata. A yayin wancan zaben dai shugaban ‘yan hamayyar siyasar ya  riya cewa shi ne wanda ya lashe zaben,amma kuma daga baya ya amince da sakamakon da hukumar zabe ta sanar duk da cewa yana cike da kura-kurai kamar yadda...
    Sojojin da suke aiki a ƙarƙashin rundunar birget ta 6 da ke garin Jalingo a Jihar Taraba sun kashe ’yan bindiga biyu tare da ƙwato shanu guda dubu ɗaya daga hannun ɓarayin shanu. Muƙaddashin Daraktan yaɗa labarai na rundunar sojoji ta birget ta 6 da ke garin Jalingo, Kyaftin Oni Olubodunde ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a garin Jalingo a ranar Juma’a. Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo An kama wasu da haramtattun buhunan takin zamani 20 a Borno Ya ce, nasarar ƙwato shanu tare da kashe ’yan bindigar ya kasance ne biyo bayan wani bayanan sirri da rundunar ta samu dangane da shuguban wasu guggun ’yan bindigar akan bubura talatin...
    Shugaban jam’iyyar NNPP na ƙasa, Dokta Agbo Gilbert Major, ya tabbatar da cewa tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Rabi’u Musa Kwankwaso, ba ya tare da jam’iyyar tun watan Yunin 2023. Ya ce Kwankwaso ya fice daga NNPP tare da mabiyansa na Kwankwasiyya. Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — Atiku A yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a shirin ‘Daily Politics’ na Trust TV, Dokta Major ya ce: “Kwankwaso ya zama tarihi a jam’iyyar NNPP. Ya zo a wani lokaci, sannan ya tafi da nasa mutanen. “Bisa tsarinmu da kuma hukuncin kotu daga Abiya da Abuja, ba ya cikin jam’iyyar tun 2023.” Shugaban jam’iyyar ya kuma...
    Kididdigar da ma’aikatar kula da harkokin masana’antu da sadarwa ta kasar Sin ta yi, ta nuna cewa, tsakanin watan Janairu zuwa Afrilun bana, adadin yarjejeniyoyin da suka shafi fasaha da aka kulla ya kai dubu 228 a kasar Sin, wadanda suka shafi Yuan triliyan 1 da biliyan 600, adadin da ya karu da kaso 13.3 bisa dari, idan aka kwatanta da na makamancin lokacin a bara. Lamarin da ya nuna cewa, kasuwar fasaha ta kasar Sin tana bunkasuwa yadda ya kamata.   A matsayin daya daga cikin muhimman kasuwanni 5 na kasar Sin, bunkasuwar kasuwar fasaha tana da muhimmanci ga aikin kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da sana’o’i. Kididdigar ta nuna cewa, a shekarar 2024, jimillar kudaden da aka samu daga...
    A ranar Asabar ne Shugaban Najeriya  Bola Tinubu zai tashi daga Abuja zuwa birnin Rome na ƙasar Italiya bisa gayyatar da sabon Fafaroma Leo XIV ya aike masa. A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Alhamis, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya sanar da cewa, shugaba Tinubu zai yi bulaguron ne tare da manyan jagororin ɗariƙar Katolika na Najeriya domin halartar bikin rantsar da sabon fafaroman wanda shi ne na 267. Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro An kama wasu da haramtattun buhunan takin zamani 20 a Borno A cewar Onanuga, Cardinal Pietro Parolin ya aike da goron gayyata daga Fafaroma Leo XIV, wanda...
    Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya buƙaci sojojin Najeriya su ƙara jajircewa wajen yaƙar matsalolin tsaro da ke addabar ƙasar nan. Ya ce zaman lafiya, dimokuraɗiyya, da ci gaban tattalin arziƙi duk suna dogara ne da tsaron ƙasa. An kama wasu da haramtattun buhunan takin zamani 20 a Borno Mutum ɗaya ya rasu a rikicin manoma da makiyaya a Yobe Tinubu, ya bayyana hakan ne yayin wani bikin ƙaddamar da sabbin jiragen sama guda biyu ƙirar Agusta 109 Trekker a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja. Bikin ya kasance wani ɓangare na bukukuwan cika shekaru 61 da kafuwar Rundunar Sojin Saman Najeriya. Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ne, ya wakilci Tinubu a wajen bikin. Ya ce Najeriya na...
    Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta kama wasu mutane uku da ake zargi ɗauke da buhuna 20 na haramtattun takin zamani samfurin “Urea”. An bayyana hakan ne a wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Borno DSP, Nahum Kenneth Daso ya fitar a ranar 15 ga Mayu, 2025. Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — Atiku Gwamnatin Katsina za ta gina birnin dawakai na farko a Afirka Rundunar kai ɗaukin gaggawar (RRS), ƙarƙashin jagorancin Kwamishin ‘Yan sandan jihar CP Yusufu Mohammed Lawal ne ta kama waɗanda ake zargin a ranar 13 ga Mayu, 2025, da misalin ƙarfe 11:30 na safe a unguwar Tashan Journey, Maiduguri. Waɗanda ake zargin sun haɗa da, Shamsuddeen Rabiu mai kimanin shekara 35,...
    Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya ce tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ne ya murƙushe ƙungiyar Boko Haram lokacin da ta fara bayyana a shekarar 2002. Atiku, wanda ya yi mataimakin shugaban ƙasa daga 1999 zuwa 2007, ya bayyana hakan ne a wata ganawa da masu ruwa da tsaki daga Jihar Kogi a birnin Abuja. Gwamnatin Katsina za ta gina birnin dawakai na farko a Afirka Ƙungiya mai alaƙa da Alƙa’ida ta yi iƙirarin kashe sojoji 200 a Buarkina Faso Ya bayyana cewa lokacin da Boko Haram ta fara tayar da hankali a Jihar Yobe, Obasanjo ya kira shi domin neman shawararsa. Atiku, ya bayar da shawarar a kira shugabannin tsaro a ba su wa’adin daƙile lamarin, ko su...
    Wani rikici da ya ɓarke tsakanin manoma da makiyaya a ƙauyen Chikuriwa da ke Ƙaramar Hukumar Nangere a Jihar Yobe, ya yi sanadin mutuwar mutum ɗaya tare da jikkata wasu. Rahotanni sun nuna cewa rikicin ya faru ne da yammacin ranar Litinin, 13 ga watan Mayu, 2025 bayan da wani makiyayi ya shigar da shanunsa cikin gonar wani manomi, abin da ya tayar da rikici. Yajin aiki: Jami’ar KASU ta shiga rudani BUA ya yi alkawarin karya farashin shinkafa A lokacin da rigimar ta ɓarke, an harbi wani manomi mai suna Babayo Maina Osi da kibiya a goshinsa, wanda hakan ya jikkata shi. Wata majiya daga ƙauyen ta ce rikicin ya ƙazanta sosai har ya rikiɗe zuwa faɗa tsakanin manoma...
    Shugaban Runkunin Kamfanin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya bayyana shirinsa na karya farashin shinkafa a Najeriya, yana mai cewa nan gaba kadan wadanda suka saye shinkafar suka boye suna jiya ta yi tsada, za su tafka mummunar asara. Dan kasuwar ya kuma bayyana cewa suna tattunawa da Shugaban Kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, kan hanyoyin da za su bi domin ganin sun daidaita farashin siminti. BUA ya bayyana haka ne a yayin ganawarsa da manema labarai jim kadan bayan wata ganawa da ya yi da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a Fadar Shugaban Kasa. “Farashin kayan abinci na saukowa a Najeriya kuma muna yin duk abin da za mu iya na ganin cewa mun mara wa gwamnati baya a kan hakan,”...
    “Wannan ya ba wasu jihohi fiye da goma sha daya ‘yancin kai, tare da karin wadanda ake sa ran za su biyo baya. Wadannan jihohin yanzu suna iya shiga cikin masana’antar wutar lantarki, daga samarwa har zuwa isarwa, rarraba, har ma da samar da mitoci.” “Na biyu, dole ne mu magance rashin ingancin ababen more rayuwa, wanda ya taru a cikin shekaru 60 da suka wuce saboda rashin kula da rashin isasshen zuba jari don farfado da tsarin zamanantar da wutar lantarki.” Ministan ya kuma jaddada bukatar cike gibin mita na sama da kashi 50 bisa dari, yana mai cewa shirin shugaban kasa yana nufin cimma wannan ta hanyar girka mita miliyan 18 a cikin shekaru biyar masu zuwa. Ya...
    Jami’ar Jihar Kaduna (KASU) ta shiga rudani a ranar Alhamis bayan da aka samu rahotanni masu karo da juna game da matsayin yajin aikin da reshenta na Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ke yi. Shugaban Jami’ar, Farfesa Abdullahi Ibrahim Musa, ya gudanar da taron manema labarai inda ya sanar da cewa ASUU-KASU ta dakatar da yajin aikin nata, kuma za a ci gaba da karatun nan take. Ya danganta matakin janye yajin aikin da shiga tsakani da Gwamna Uba Sani ya yi, wanda ya amince da biyan Naira miliyan 50 miliyan don walwalar ma’aikata, tare da fitar da N146 miliyan don biyan wasu albashin da aka rike da kuma alawus-alawus na shirin koyon makamar aiki na dalibai (SIWES). Farfesa Musa ya...
    Adepoyigi an sace shi ne da ƙarfe 10:00 na dare yayin da yake ƙoƙarin ajiye motarsa a gidansa da ke Ifon. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    A yayin da Babbar Sallah ke ƙara ƙaratowa, ’yan kasuwar dabbobi sun bayyana fargaba game da yiwuwar farashin raguna da sauran dabbobin lauya zai yi tashi gwauro a Najeriya. Wannan na zuwa ne bayan da gwamnatin sojin ƙasar Jamhuriyar Nijar ta sanya takunkumin wucin gadi kan fitar da dabbobi zuwa ƙetare, gami da yawaitar sace-sacen dabbobi a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya. A farkon watan nan na Mayu ne Gwamnatin Nijar ta sanar cewa matakin na da nufin daidaita farashi dabbobin layya a cikin gida da kuma tabbatar da wadatarsu ga al’ummarta —waɗanda mafi rinjaye Musulmi ne — kafin zuwan Babbar Sallah a farkon watan Yuni. Haramcin ya shafi fitar da shanu da tumaki da awaki da raƙuma, tare da...
    Harajin ya kuma kai kasa da kimanin kaso 11 a cikin dari, wanda ya kai kasa da wanda ake karba, idan aka kwatanta da duniya. “Abinda muka yi shi ne, mun cire daukacin ma’aikatan da karbar kasa kaso uku a cikin darei a cikin tsarin na karabar harajin,” Inji tsohon Shugaban LLP. Ya shedawa manyan Malaman Makaranta  da Jami’an da ke katbar haraji hakan ne, a wani taro da aka gudanar a jihar Legas Nijeriya dai, ta kasance kasar da sama da alumominta miliyan 8o, ke fama da kangin talauci. Hakan ya kuma kara haifar da hauhawan farashin kayan masarufi, musamman yadda kayan suka tashi a 2024, kafin su sauka zuwa kaso 24.2 a cikin dari. Kazalika, hauhauwan farashi da...
    Majiyar kiwon lafiya a zirin Gaza ta bayyana cewa daga safiyar jiya Alhamis zuwa karfe 12 dare HKI ta kashe falasdinawa 143 tare da amfani da jiragen saman yaki tankunan yaki ta kasa da kuma jiragen ruwa yaki. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa bayan tsakiyar dare ma sojojin yahudawan sun kashe wasu karin mutane 21 wato a safiyar yau Jumma’a, a sansanin yan gudun hijira na Jabaliya. wato sa’o’ii 5 bayan tsakiyar dare a kuma lokacin bada wannan labarin. Labarin ya kara da cewa a wasu hare haren guda biyu a Khan Yunus sojojin yahudawan sun kashe falasdinawa 5 wasu daga cikinsu yara. Gwamnatin Hamas a Gaza, ta bayyana cewa, tun lokacinda sojojin yahudawan suka...
    Ma’aikatar kiwon lafiya a kasar Saudia ta kaddamarda wata manhaja don kula da lafiyan mahajjata a hajjin bana, wanda aka tarjamata zuwa harsuna 8 a duniya. Shafin yanar gizo na labarai Arabnews ya nakalto kamfanin dillancin labaran Saudi Press Agency (SPA) na fadar haka a yau Jumma’a.  Ya kuma kara da cewa harsunan da ake samun manhajar a ciki suna hada da Arabiyya, Inglishi, Faransaci, Urdu, Farisanci, Indonesia, Malay da kuma Turkanci. Manufar wannan manhajar ita ce bada shawara ga mahajjata kan yadda zasu kula da lafiyarsu a cikin wannan lokacinda Hajji na bana, wanda yake zuwa tare da zafi sosai. Da farko manhajan ya bukaci mahajjata su yi amfani da laima don rage zafin da ke fadawa a kansu....
    Haramun ne ga mai harama namiji ya daura duk wani abu dinkakke, sai dai hirami kawai. Amma idan bai samu hirami ba, babu laifi ya daura wando kamar yadda Abdullahi bin Abbas (RA) ya ruwaito daga cikin hudubar da Annabi (SAW) ya yi a ranar Arfa. Idan mai harama bai samu silafas ba, zai iya sanya takalmi sawu-ciki, amma ya yanke shi zuwa karkashin idon sawunsa kamar yadda ake wa khuffi. Wannan duk an haramta ne ga namiji. Amma ita mace babu abin da ya haramta mata illa sanya turare, nikabi da safar hannu, kamar yadda Abdullahi bin Umar (RA) ya ruwaito daga Manzon Allah (SAW). Haka nan kar ta sanya kayan da aka yi musu rini da turare, amma...
    Kyaftin Shehu Iyali, tsohon mataimaki na musamman kan sufurin jiragen sama a zamanin tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo da Goodluck Jonathan, ya rasu. Kyaftin Shehu Iyal ya rasu ne a ranar Alhamis bayan ya yi fama da jinya. Kafin rasuwarsa shi ne shugaban kamfani jiragen sama mai suna Afri Air. Marigayin yakasance jigo a harkar sufurin jiragen sama a Najeriya kuma ya tuka shugabannin ƙasa. Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin Sambisa NAJERIYA A YAU: Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027? A shekarar 1977 Kyafin Shehu Iyal ya kammala karatun digiri ɗinsa a Jami’ar Ahmadu Bello kafin daga bisani ya shiga Kwalejin Koyon Tuƙin Jiragen Sama (NCAT) da ke Zariya. Kafin rasuwarsa ya riƙe...
    Wata ƙungiyar ’yan ta’adda mai alaƙa da ƙungiyar Alƙa’ida ta ɗauki alhakin kashe sojoji 200 a ƙasar Burkina Faso. Ƙungiyar mai suna Jama’at Nusrat al-Islam wal-Muslimin (JNIM), ta ɗauki alhakin kai hari a Djibo, arewacin Burkina Faso, tana mai cewa ta kashe sojoji 200. Wannan ikirarin, wanda cibiyar SITE Intelligence Group mai hedkwata a Amurka ta ruwaito a ranar Alhamis, ya biyo bayan iƙirarin JNIM na baya da ta yi na kashe sojoji 60 a harin. SITE Intelligence Group, wacce ke sanya idanu kan ayyukan ƙungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi ta intanet, ta nuna cewa harin wani bangare ne na ƙaruwar ayyukan JNIM a Burkina Faso a cikin watan da ya gabata, wanda ya haifar da asarar rayuka da dama. Ɗaukar...
    Wakilan kafafen yada labaran, sun tattauna kan kalubalen da fannin aikin noman kasar ke fuskanta da suka hada da rashin samar ainahin bayanai kan abin da ya shafi aikin noma. Rashin bayar da ingantaccen dauki ga fannin daga bangaren gwamnati, kalubalen rashin tsaro da zabar wasu ‘yan lelen kafafen yada labarai, musaman da gwamnatin kasar ke yi, wajen bayar da tallace-tallacen da suka shafi bangaren aikin noma, inda suka yi nuni da cewa, kafafen yada labarai; sun dogara ne kacokan a kan samun tallace-tallace, wanda akasari shi ne ke rike da su. Sun kuma bukaci a samar wa da kafafen yada labaran kasar, wata hanyar sadarwa ta bai daya, musamman domin su kara wallafa rahotannin da suka shafi ayyukan gwamnatin...
    Sojojin Najeriya sun kai wani mummunan harin ramuwar gayya kan sansanonin ’yan ta’adda a Dajin Sambisa, inda suka kashe mayaƙa da dama tare da tarwatsa maɓoyar miyagun. Sojoji sun ƙaddamar da wannan farmaki ne bayan kisan abokan aikinsu huɗu da ’yan ta’adda suka yi a farkon wannan makon. Kai tsaye sojojin suka kai hari kan sansanonin ’yan ta’addar da ke Garin Malam Ali da Garin Glucose da kuma da Ukuba, waɗanda ke cikin Dajin Sambisa. Wannan matakin da aka ɗauka ya biyo bayan jerin hare-hare da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne suka kai a ranar Talata kan sansanonin sojoji guda uku a Rann da Gajiram da kuma da Dikwa a Jihar Borno, wanda ya yi sanadiyar mutuwar sojoji hudu....
    A nan gaba za ayi bayani kan ilimin da muhimmancin da yake da shi ga mutane daidaikai,da kuma al’umma.Kai har ma dalilin da yasa aka samu nau’ukan ilimi daban-daban da kuma gamsassun daliliai na lamurran ilimi.   Minene Ilimi? World Vision a shekarar (2021)ya bayyana ilimi a matsayin wata hanya ce da mutane suka karuwa da ilimi ko kuma ya san wani labara wanda yana zama ilimi sannu a hankali. Bugu da kari wurin koyon ilimi ya zama shi ma wuri ne da mutum/ mutane za su bunkasa dabarunsu na rayuwa da sua kasance dole,su gane dokoin da suka kasance dole ne a sansu,su gane yadda za su gabatar da hukuncin da ya dace mai kuma amfani, su kuma gane...
    Mun bijoro da wannan batun kalubalen da manoman ke ci gaba da fuskanta ne, musamman duba da cewa, kakar noman bana, ta karato, musamman ganin cewa, an fara samun saukar Ruwan sama, a wasu sassan kasar nan, inda kuma tuni, mahara suka mamaye wasu yankunan kasar da ake yin noma. Akasarin fadin kasar nan, musamman a yankunan Arewa ta Tsakiya da Arewa maso Yamma duba da cewa, wadannan yankunan biyu, sun yi fice wajen yin noma, amma abin takaici, ‘yan bindiga daji, ‘yan ta’adda da kuma wasu Fulani Makiyaya, sun mayar da wadannan yankunan fagen daga, inda suka kashe manoma da kuma lalata amfanin gonakansu. Bugu da kari, wadannan bata garin sun kuma kone wasu gidajen alumomin da ke a...
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Jam’iyyar NNPP wadda Dakta Boniface Aniebonam ya kafa a shekarar 2001, ta samu ƙarfi sosai a Jihar Kano bayan tsohon Gwamna Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya shiga cikinta a shekarar 2022 tare da mabiyansa na Kwankwasiyya. Shigowarsa ta farfaɗo da jam’iyyar, inda ta samu gagarumar nasara a zaɓen 2023 ta hanyar lashe kujerar gwamna da wasu kujerun majalisa. Sai dai rikicin cikin gida da na shugabanci sun dabaibaye jam’iyyar, wanda hakan ya haddasa ficewar wasu manyan ’ya’yanta zuwa APC, lamarin da ke haifar da tambaya kan makomar NNPP a Kano. Shin NNPP za ta kai labari a Kano, musamman bayan ficewar wasu jiga-jiganta? NAJERIYA A YAU: Kuskuren JAMB Da Ya Haddasa Faduwar Ɗalibai...
    Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Sun yi imani da tattaunawa da zaman lafiya ba tare da mika wuya ga barazana ba A yayin ganawarsa da masu fafutukar siyasa da zamantakewa a lardin Kermanshah da ke yammacin kasar Iran a jiya Alhamis, shugaban na Iran Masoud Perzeshkiyon ya ce za a gudanar da shawarwari kan shirin makamashin nukiliyar Iran cikin karfin gwiwa da mutunta juna, yana mai jaddada wajabcin rashin mika wuya ko mika kai ga duk wata barazana. Shugaba Pezeshkiyon ya jaddada cewa yin shawarwari ɗaya ne daga cikin ka’idodin hankali da zurfin tunani, amma ba a kan kowane farashi ba. Dole ne a gudanar da shawarwari cikin aminci da mutuntawa tare da bin ka’idojin kasa da kare kima....
    Ministan Harkokin Wajen Iran ya jaddada cewa: Ƙarfin tsaron Iran da makamanta masu linzami suna ba su ƙarfin gwiwa Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya bayyana cewa, da a ce Amurka za ta iya lalata cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, da ba za ta shiga zaman tattaunawa ba, yana mai jaddada cewa: Iran ta dogara da karfin sojanta, kuma shi ne ya tilasta wa makiya zaman tattaunawa da ita. A ziyarar da ya kai wajen baje kolin littafai na birnin Tehran, Araqchi ya ce dangane da tattaunawa wand aba na kai tsaye ba da Amurka: Idan da a ce Amurka na da karfin lalata cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, da ba ta shiga tattaunawa ita ba. Araqcgi ya kara da cewa:...
    Jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa: Amurka tana da hannu dumu-dumu a muggan ayyukan da gwamnatin ‘yan shayoniyya suka aikata nakisan kare dangi a Gaza Jakada kuma wakilin dindindin na Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya Amir Sa’ed Irawani ya yi nuni da ire-iren laifuffukan da gwamnatin ‘yan sahayoniyya suke ci gaba da aikatawa kan al’ummar Falastinu, yana mai bayyana wadannan laifuka a matsayin wani misali karara na kisan kiyashi yana kuma daukar Amurka a matsayin babbar kawa a aikata wadannan muggan laifuka. A yayin zama na musamman a Majalisar Dinkin Duniya a yammacin jiya Alhamis kan batun boren Falasdinawa “Ankaba” na musamman ya bayyana cewa: Gwamnatin yahudawan sahayoniyya tana so da cikakken goyon baya...
    Rundunar sojin Yemen sun kai hari kan filin jirgin saman Ben Gurion da makami mai linzami Rundunar sojin Yemen ta sanar da kaddamar da farmakin soji kan babban filin tashin jiragen saman Ben Gurion da ke yankin Jaffa da aka mamaye, domin jaddada goyon baya ga al’ummar Falastinu da ake zalunta da kuma yin nuna kiyayya ga kisan kiyashin da makiya ‘yan  sahayoniyya suke yi wa ‘yan uwansu a Zirin Gaza. Kakakin rundunar sojin Yemen Birgediya Janar Yahya Sari’e ya bayyana cewa: Don goyon bayan al’ummar Falastinu da ake zalunta da ‘yan gwagwarmaya da kuma nuna rashin amincewa da kisan kiyashin da makiya ‘yan sahayoniyya suke yi kan ‘yan uwansu a yankin Zirin Gaza, sojojin Yemen suna ci gaba da...
    Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta shirya wata zanga-zanga da Falasdinawa ke jaddada cewa: babu halacci ga ‘yan mamaya kuma al’ummar Falastinu za su ci gaba da gwagwarmaya Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta jaddada cewa: Haramtacciyar kasar Isra’ila ba ta da halacci ko kuma wani ikon mallakar wani yanki na Falasdinu da ta mamaye, kuma al’ummar Falastinu za su ci gaba da kare kansu ta hanyar gudanar da gwagwarmaya har sai sun kwato dukkanin Falastinu tare da kafa kasar Falasdinu mai cikakken ‘yanci kai wacce Qudus zata kasance a matsayin babban birninta. A yayin bikin cika shekaru 77 da kafuwar Nakba, -boren Falasdinawa na farko- kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta bayyana cewa: “Ba za a yi wani sabon...
    A cewarsa, yanzu haka ana sayar da shinkafa kimanin naira 60,000 kan kowane buhu, buhun fulawa kan naira 55,000, da masara a kan Naira 30,000.   Ya yi bayanin cewa, kafin zartar da umarnin rage harajin kwastam kan kayayyakin abinci, ‘yan kasuwa kan sayen kayan abinci tun yana gona su boye, sannan su sayar da shi a farashi mai tsada. Ya kara da cewa, “Amma a yanzu, wannan shirin ya kare, yanzu masu irin wannan halin, asara kawai suke kirgawa Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu...
    Majalisar wakilai za ta binciki yadda aka samu mummunar faduwa a jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire (UTME) ta 2025 da hukumar shirya jarabawar (JAMB) ta gudanar kwanan nan. Hakan ya biyo bayan amincewa da kudirin da dan majalisa, Adewale Adebayo ya gabatar a zauren majalisar a ranar Alhamis. Da yake gabatar da kudirin, ya koka da cewa, da yawa daga cikin daliban, sun yi tafiya mai nisa domin zana jarabawar UTME a cibiyoyin jarabawar. Amma abin takaici, sai ga sakamakon ya fito da koma baya da yawa. Duk da cewa, hukumar JAMB ta amince cewa, tangardar na’ura ce ta janyo faduwar amma akwai bukatar a binciki hukumar. Idan za a iya tunawa, sakamakon jarabawar UTME na 2025 da JAMB...
    Shugaban kasar Iran Massoud Pezeshkian, ya mayar da martani ga shugaba Donald Trump na Amurka, yana mai cewa Iran kasa ce son zaman lafiya ba yaki ba. Zaman lafiya muke nema, ba yaki ba; Su ne ke haifar da rikici. Muna fatan samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin kasar nan da ma makwabtanmu, inji shugaba Pezeshkian. Muna neman ‘yan uwantaka da daidaito tsakanin kasashen Azarbaijan, Rasha, Afghanistan, Pakistan, Iraki da Saudiyya, in ji shugaban na Iran a, yayin da yake ishara da kalaman Trump. Trump yana ganin zai iya yi mana barazana, ya sanya mana takunkumi, da kuma yin magana game da hakkin dan Adam, amma a lokaci guda suna da hannu a tashe-tashen hankula da laifuffuka a...
    Iran ta bayyana cewa za ta yi zama gobe Juma’a da kasashen nan na turai guda uku da ake kira E3, wato Biritaniya, Jamus da kuma Faransa kan shirinta na nukiliya. Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmail Baghai ya bayyana cewa, a ranar Juma’a 16 ga watan Mayu ne za a yi shawarwari karo na hudu da Teheran da kasashen Turan da suka kulla yarjejeniyar nukiliyar 2015. Ya ce za a gudanar da taron ne a birnin Istanbul na kasar Turkiyya. Babban ajandar taron dai shi ne ci gaba da tuntubar juna da kasashen uku, musamman kan shawarwarin dake tsakanin Tehran da Washington. Ya zuwa yanzu dai Iran da kasashen turai sun gudanar da shawarwari guda uku kan batun nukiliyar...
    Shugaban Majalisar Dokokin Iran Mohammad Baqer Qalibaf ya ce kamata ya yi kasashen Iran da Aljeriya su hada kai wajen kai kayan agaji a zirin Gaza da yaki ya daidaita. Qalibaf ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da shugaban majalisar al’ummar kasar Aljeriya Ibrahim Boughali a ranar Laraba a birnin Jakarta na kasar Indonesiya, a gefen taron ‘yan majalisar dokokin na kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta PUIC karo na 19. Ya jaddada muhimmancin samar da hadin kai wajen tunkarar hare-haren wuce gona da iri da Isra’ila ke yi a Falasdinu da kuma maido da hakkokin al’ummar Falastinu da ake zalunta a zirin Gaza. Qalibaf ya yi kira ga kasashen musulmi da su hada kai su nemo...
    A ranar Alhamis din nan, wasu hadiman shugaban kasa kan harkokin yada labarai sun kai ziyara hedikwatar hukumar ta NOA inda suka yi amfani da damar wajen lekawa daya daga cikin kayayyakin tarihin Nijeriya a baya – ofishin marigayi shugaba Shagari. Bayan kammala ziyarar, daya daga cikin hadiman shugaban kasa kan harkokin yada labarai, Temitope Ajayi, ya wallafa hotunan a shafinsa na Facebook domin bayyana abin da suka gani. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    A makon nan ne aka ga hotunan Sheikh Alƙali Zariya ya halarci zauren tattaunawa na fitacciyar jarumar Kannywood, Hadiza Aliyu Gabon, wanda ake kira ‘Gabon Talkshow’, abin da ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta. Gabon Talkshow dandali ne da jaruma Hadiza ke gayyatar mashahuran jarumai da mawaƙa domin tattauna game da rayuwarsu da ayyukansu a masana’antar nishaɗi. Tsaro: Tinubu ya ƙaddamar da rundunar tsaron daji a faɗin Najeriya Hauhawar farashi ya ragu zuwa kashi 23.71 — NBS Bayyanar Sheikh Alƙali a wannan dandali ya jawo suka mai tarin yawa daga al’umma. Wasu na ganin bai dace da matsayin malami irinsa ya halarci irin wannan dandali ba, domin ba wajen ilmantarwa ba ne ko karantarwa. A cewar wasu, hakan zai...
    Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wata mata mai shekara 21 mai suna Fatima Salisu da ake zargi da safarar makamai, biyo bayan samun bayanan sirri. Kakakin rundunar ’yan sanda, Ramhan Nansel ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis. Ganduje ya halarci Majalisar Wakilai don sheda ’Yan Majalisa 2 zuwa APC Sabon Hari: An kashe makiyayi da shanu sama da 100 a Filato Kakakin ya ce an kama Fatima ne da laifin safarar alburusai ta yankin Keana da Doma a cikin Jihar Nasarawa don taimakon masu aikata laifuka a Katsina, inda take zaune. “Cikin gaggawa kan bayanan sirri da aka samu, Kwamishinan ’yan sanda CP Shetima J. Mohammed, ya ba da umarnin tura sashin yaƙi da masu garkuwa da...
    Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da kafa sabuwar rundunar masu tsaron daji a faɗin ƙasar nan domin tinkarar matsalolin tsaro da ke ƙaruwa a cikin dazukan Najeriya. A ƙarƙashin wannan sabon shiri, za a ɗauki sama da mutane 130,000 aiki da za su samu horo na musamman da kayan yaƙi na zamani domin kare dazuka guda 1,129 da ke sassa daban-daban na ƙasar nan. Hauhawar farashi ya ragu zuwa kashi 23.71 — NBS Mutum 2 sun shiga hannu zargin yi wa ƙananan yara fyaɗe a Gombe Wannan na cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai da hulɗa da jama’a, Sunday Dare, ya fitar a shafinsa na X. Sanarwar ta bayyana cewa an...
    Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ziyarci zauren Majalisar Wakilai a ranar Alhamis domin ganewa idanunsa ficewar wasu mambobi biyu na Jam’iyyar adawa ta NNPP zuwa jam’iyya mai mulki ta APC. ’Yan majalisar biyu, sun haɗa da: Dan Majalisar Wakilai, Abdullahi Sani Rogo mai wakiltar mazaɓar Rogo/Karaye da kuma Ɗan Majalisar Wakilai Kabiru Alhassan Rurum mai wakiltar mazaɓar tarayya ta Rano/Bunkure/Kibiya, sun sauya sheƙa a ranar Alhamis. Sabon Hari: An kashe makiyayi da shanu sama da 100 a Filato Dalilin da ya sa gwamna Bala ya yi ƙoƙarin mari na – In ji Minista Hakazalika mamba mai wakiltar mazaɓar Ijesha Oriade/Obokun na Jihar Osun, Wole Oke, ya kuma bayyana ficewarsa daga jam’iyyar adawa ta PDP zuwa APC....
    An ce, ‘yan bindigar sun yi galaba a kan masu gadin fadar, inda suka tafi da sarkin zuwa wani wuri da ba a san ko ina ne ba.   Da take tabbatar da faruwar lamarin, rundunar ‘yansandan jihar Kogi ta ce, an fara gudanar da bincike, inda ta ce rundunar hadin gwiwa da ta kunshi jami’an tsaro da ‘yan banga na yankin sun fara farautar ganowa tare da kubutar da sarkin.   Sai dai shugaban karamar hukumar Yagba ta yamma, Hon. Tosin Olokun ya yi Allah-wadai da sace Sarkin. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da...
    Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS), ta bayyana cewa hauhawar farashi a Najeriya ya sauka kaɗan a watan Afrilu 2025 zuwa kashi 23.71, daga kashi 24.23 da aka samu a watan Maris. Wannan na nuna cewa hauhawar farashi ya ragu idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, inda a watan Afrilun 2024 aka samu kashi 33.69. Sabon Hari: An kashe makiyayi da shanu sama da 100 a Filato Wuta ta kashe ɓarawon wayar lantarki a Jigawa Wannan ragi da aka samu a watan Afrilu ya kai kusan kashi 10. Har ila yau, hukumar ta ce hauhawar farashi daga wata zuwa wata ya ragu a watan Afrilu, inda aka samu kashi 1.86, ƙasa da kashi 3.90 da aka samu a watan...
    Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya bayyana abin da ya janyo saɓani tsakaninsa da Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, a lokacin da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya kai ziyara jihar. A watan Afrilu, rahotanni sun bayyana cewa Mataimakin Gwamnan Bauchi, Muhammad Auwal Jatau, ya mari Minista Tuggar a cikin mota yayin da suke kan hanyar zuwa fadar Mai Martaba Sarkin Bauchi. Wuta ta kashe ɓarawon wayar lantarki a Jigawa Najeriya ba za ta koma mulkin soja ba — Gowon Amma Mataimakin Gwamnan ya musanta faruwar hakan. Da yake zantawa da BBC Hausa, Tuggar ya ce saɓanin ya samo asali daga wajen Gwamna Bala Mohammed ba daga wajen mataimakinsa ba. “Muna cikin mota tare da Mataimakin Shugaban Ƙasa,” in ji...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    A yau Alhamis ne dai kakakin ma’aikatar harkokin wajen jamhuyriyar musulunci ta Iran Dr. Isma’ila Baka’i, ya bayyana damuwar kasar akan halin da ake ciki a birnin Tripoli na kasar Libya wanda ya yi sanadiyyar kashe mutane masu dama, tare da yin kira da a kawo karshen zubar da jini. Dr. Baka’i ya yi ishara da nauyin da ya rataya a wuyan dukkanin wadanda suke da hannu a fadace-fadacen da suke faruwa a cikin babban birnin kasar ta Libya, sannan ya bukace su da su taimaka wajen dawo da zaman tsaro a cikin kasar. Haka nan kuma ya bukace su da su koma kan teburin tattaunawa mai maimakon amfani da karfi, su kuma kaucewa bai wa kasashen waje damar tsoma...
    Shugaban kasar Amurka wanda yake Ziyara a kasar Katar ya sanar da cewa gwamnatinsa tana son ganin tattaunawar da ake yi da Iran ta yi nasara, kuma ya yi Imani da cewa ana gab da kulla yarjejeniya da ita. Shugaban kasar ta Amurka ya kuma ce da akwai ci gaba sosai a cikin tattaunawar da ake yi a tsakanin Amurka da Iran akan shirinta na makamashin Nukiliya.  Shugaban kasar ta Amurka dai ya bayyana hakan ne dai a lokacin da yake Magana da manema labaru a birnin Doha na kasar Katar. Da yake Magana akan yakin kasar Ukiraniya da Rasha,  shugaban kasar ta Amurka ya kuma bayyana imaninsa da kusancin kawo karshen yakin tare da cewa yana kokarin ganin an...
    A jiya Laraba ne dai da aka rattaba hannu akan wata yarjejeniya a tsakanin sarkin Katar Tamim Bin Hamad ali-Thani da kuma shugaban kasar Amurka Donad Trump wanda ya kai Ziyara kasar. Shugaban kasar Amurka wanda ya bayar da labarin kulla wannan yarjejeniya ya kusa sanar da cewa, kasar ta Katar za ta sayi jiragen sama marasa matuki samfurin Mq-9 daga Amurka. Gabanin isarsa kasar ta Katar, shugaban kasar ta Amurka ya fara yada zango ne a kasar Saudiyya inda ya sami kyakkyawar tarba daga mahukuntanta, tare da kuma da kulla yarjejeniyar kasuwanci ta billiyoyin daloli. Saudiyyar ta yi alkawalin zuba hannun hajri a can Amurka da kudaden da su ka kai dala biliyan 500 zuwa biliyan 600. Haka nan...
    ’Yan bindigar da suka yi garkuwa da Shugaban Jami’iyyar APC a Ƙaramar Hukumar Ose a Jihar Ondo, Nelson Adepoyigi, sun riƙe mutanen da suka kai musu kuɗin fansarsa, sa’annan suka ƙara ƙudin fansar da suka nema da ninki shiga. A ranar Litinin da dare ne ’yan bindiga suka yi awon gaba da Honorabul Nelson Adepoyigi a ƙofar gidansa inda suka nemi kuɗin fansa naira miliyan 100 kafin daga bisani a daidaita a kan miliyan biyar. Majiyoyin sun a lokacin da yake ƙoƙarin shiga gida ne maharan suka far masa suka fito da shi daga cikin motarsu, sa’annan suka make shi da gungumen ice sa’annan suka tafi da shi. Wani makusanci ga waɗanda suka kai kuɗin ya bayyana cewa, “Bayan daidaitawa...
    Tashar talabijin din almayadin ta watsa labarin dake cewa, daga safiyar yau Alhamis zuwa yanzu, adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun haura 40,mafi yawancinsu daga yankin Khan-Yunus. Tun da safiyar yau Alhamis ne dai sojojin HKI su ka fara kai hare-hare a yankuna mabanbanta na Gaza da su ka hada da Khan-Yunus. ‘Yan sahayoniyar sun yi amfani da manyan bindigogi da kuma jiragen sama na yaki. Adadin wadanda aka tabbatar da sun yi shahada ya zuwa yanzu sun haura 40. Sai dai wasu rahotannin da suke fitowa daga Gaza din sun ce, adadin shahidan ya karu zuwa 82. Jiragen HKI suna kai wa yankin na Gaza hare-hare daga kduancinsa zuwa arewacinsa cikin hauka. A Khan-Yunus ‘yan Sahayoniyar sun...
    A yau ne za a gudanar da tattaunawar zaman lafiya kan yaƙin da ke tsakanin Ukraine da Rasha a birnin Istanbul da ke ƙasar Turkiyya, – amma fadar Kremlin ta bayyana cewa shugaban Rasha, Vladimir Putin, ba ya cikin jerin jami’an da za su halarci tattaunawar. Rahotanni daga kafafen yaɗa labarai sun ce shugaban Amurka Donald Trump shima ba zai halarci taron ba – duk da cewa ya nuna sha’awar halarta jiya idan har Putin zai je. Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, zai kuma kasance a babban birnin Turkiyya, Ankara a yau don ganawa da shugaba Recep Tayyip Erdogan inda ya ce zai je taron tattaunawar da Rasha a Istanbul ne kawai idan Putin ya halarta. Tun daga watan Disamba na...
    Majalisar dokokin jihar Kaduna ta amince da dokar hukumar kula da manyan makarantu ta jihar Kaduna, ta shekarar 2025, ya zama doka. Dokar dai na da nufin daidaita harkokin gudanar da manyan makarantun sakandire a fadin jihar domin daidaita tsarin ilimin zamani.   Da yake jagorantar zaman majalissar, mataimakin kakakin majalisar Mista Henry Magaji Danjuma ya bayyana cewa sabuwar dokar za ta inganta yadda ake gudanar da manyan makarantun sakandire a jihar.   Kudirin dokar ya biyo bayan gabatar da rahoton Barr. Mahmud Lawal Isma’ila, shugaban kwamitin hadin gwiwa kan ilimi da shari’a, kuma wakilin mazabar birnin Zaria. Ya bayyana cewa dokar ta zama dole ne ta hanyar gyare-gyaren nan a tsarin ilimin Najeriya.   “A da, mun gudanar da...