Leadership News Hausa:
2025-09-20@12:22:44 GMT

Tawagar Hafsoshin Sojojin Afirka Ta Ziyarci Kasar Sin

Published: 7th, May 2025 GMT

Tawagar Hafsoshin Sojojin Afirka Ta Ziyarci Kasar Sin

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Ta Halarci Babban Taro Kan Kasuwancin Halal A Malaysia

Tawagar gwamnatin jihar Jigawa ta shiga sahun sauran kasashe da suka halarci taron kasa da kasa na Halal da ke gudana a Malaysia (MIHAS), domin neman jari da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa na tattalin arziki.

Tawagar karkashin jagorancin Kwamishinan Harkokin Kiwo, Farfesa Abdurrahman Salim Lawal, ta hada da Dr. Saifullahi Umar, Darakta-Janar na Hukumar Zamanantar da Harkar Noma ta Jihar Jigawa, da kuma Hajiya Aisha Sheik Mujaddadi, Darakta-Janar ta Hukumar Inganta Zuba Jari ta Jihar.

Tuni dai tawagar ta halarci taruka daban-daban yayin isar su kasar ta Malaysia, ciki har da taron Halal Certification Convention, taron kasuwancin Halal na duniya, da  MIHAS Power Talk kan zuba jari ta hanyar Halal, da kuma zaman tattaunawa kan kasuwar Halal da bada shaida.

 

Farfesa Lawal ya ce Jihar Jigawa na son ta zama cibiyar samar da kayayyakin Halal a yammacin Afirka, ta hanyar nuna ƙarfin ta a bangaren noma, musamman kiwo da kuma amfanin gona.

Ya kara da cewa manufar ita ce samar da haɗin gwiwa da kamfanonin Malaysia, hukumomin gwamnati, da shugabannin masana’antun da ke samar da kayayyakin Halal a fannonin sarrafa nama da noman da aka tabbatar da Halal.

“Shigar mu cikin MIHAS wani bangare ne na jajircewar wannan gwamnati wajen bambance hanyoyin samun kudaden shiga da kuma samar da ayyukan yi. Mun yi imani cewa haɗin gwiwa da bayanan da muka samu daga wannan taro za su taimaka wajen jawo jari da kuma samar da damar arziki ga al’ummarmu.” In ji shi.

Tawagar ta kuma gudanar da tarurruka da dama tare da manyan masu ruwa da tsaki na Malaysia domin tattauna batutuwan zuba jari, musayar fasaha, da kuma shirye-shiryen ƙarfafa ƙwarewa.

 

Usman Muhammad Zaria

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT
  • Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu
  • Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka
  • Jihar Jigawa Ta Halarci Babban Taro Kan Kasuwancin Halal A Malaysia
  • Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
  • Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka
  • Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica
  • Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Kaduna Ranar Juma’a
  • Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB
  • Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka