Iran Ta Bukaci Kasashen Turai Su Shiga Tattaunawar Nukliya Da Take Yi Da Amurka
Published: 6th, May 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Baghaaei ya bukaci kasashen turai da su shiga a dama da su kan tattaunawa dangane da shirin nukliyar kasar Iran na zaman lafiya. Ya kuma jaddada cewa Iran tana turjiya ga dukkan tunanin Amurka na wargaza shirin Nukliyar kasar Iran kwata-kwata.
Baghaei ya kara da cewa duk da cewa Iran a shirye take a ci gaba da tattaunawa kan shirin makamashin nukliyar kasar, da sake farfado da yarjeniyar JCPOA ta shekara ta 2015 amma kuma ba zata taba barin hakkinta na mallakar fasahar nukliya da luma sarrafashi a hanyoyin da yarjeniyar NPT ta amince da su ba.
Kuma da alamun tattaunawar tsakanin Amurka da Iran ya daki dutse, saboda sun sami sabani a kan wasu al-amura wadanda basu shafi Nukliya ba, don haka ne aka fasa taron roma wanda yakamata a gudanar a ranar asabar da ta gabata. Batun cewa Mike Waltz mai bawa shugaban kasar Amurka shawara kan tsaro yana son cusawa gwamnatin Amurka ra’ayin Benyamin Natanyahu firai ministan HKI a tattaunawar Amurka da Iran, ya ce, wannan al-amari ne na cikin gida ga gwamnatin Amurka, amma abinda ya shafi Iran shi ne menene Amurka zata gabatar a kan teburin tattaunawa da ita.
Don haka ne Iran take bukatar kasashen Turai su shigo a dama da su a cikin wannan tattaunawar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Ce Ba Wani Ma’aikacin Hukumar IAEA A Kasar A Halin Yanzu
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’ila Bakae ya bayyana cewa a halin yanzu babu wani ma’aikacin hukumar makamashin nukliya ta duniya a cikin kasar. Kuma al-amarin yadda iran zata yi hulda da hukumar bayan yakin kwanaki 12 ya koma hannun majalisar dokokin kasar da kuma majalisar koli ta harkokin tsaron kasar.
Kakakin ya kara da cewa daga yanzu mu’amala da hukumar ta IAEA dole ne ta kasance ta yadda Iran zata kare amincin cibiyoyin makamashin nuliya ta kasar. Da kuma tabbatar da cewa babu wata sirrin kasar wanda zai isa hannun makiyanta.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Pezeshkian ya yaba da irin goyon bayan da Pakistan ta baiwa Iran a lokacin yaki August 4, 2025 Bloomberg: FBI ta cire sunan Trump daga Fayilolin badakalar Epstein August 4, 2025 Jerin gwanon nuna goyon baya ga al’ummar Gaza a Sydney Australia August 4, 2025 MDD ta yi gargadi game da mummunar matsalar da yunwa ka iya haifarwa ga al’ummar Gaza August 4, 2025 Rasha da China sun fara wani gagarumin atisayen soji na hadin gwiwa a tekun Japan August 4, 2025 Araqchi Ya Bayyana Makomar Sinadarin Uranium Da Iran Ta Inganta A Lokacin Yaki August 3, 2025 Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Sun Bayyana Cewa: Masu Shirin Halaka Gaza Suna Son Mamaye Duniyar Musulmi Ne August 3, 2025 Iran Ta Jaddada Cewa: Karfin Makamai Masu Linzami Da Jiragen Sama Marasa Matuka Ciki Suna Nan Cikin Shiri August 3, 2025 Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Tana Kokarin Boye Barnarta A Zirin Gaza August 3, 2025 Tsohon Shugaban Amurka Joe Biden Ya Caccaki Trump Kan Rusa Kundin Tsarin Mulkin Kasar August 3, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci