Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Baghaaei ya bukaci kasashen turai da su shiga a dama da su kan tattaunawa dangane da shirin nukliyar kasar Iran na zaman lafiya. Ya kuma jaddada cewa Iran tana turjiya ga dukkan tunanin Amurka na wargaza shirin Nukliyar kasar Iran kwata-kwata.

Baghaei ya kara da cewa duk da cewa Iran a shirye take a ci gaba da tattaunawa kan shirin makamashin nukliyar kasar, da sake farfado da yarjeniyar JCPOA ta shekara ta 2015 amma kuma ba zata taba barin hakkinta na mallakar fasahar nukliya da luma sarrafashi a hanyoyin da yarjeniyar NPT ta amince da su ba.

Kuma da alamun tattaunawar tsakanin Amurka da Iran ya daki dutse, saboda sun sami sabani a kan wasu al-amura wadanda basu shafi Nukliya ba, don haka ne aka fasa taron roma wanda yakamata a gudanar a ranar asabar da ta gabata. Batun cewa Mike Waltz mai bawa shugaban kasar Amurka shawara kan tsaro yana son cusawa gwamnatin Amurka ra’ayin Benyamin Natanyahu firai ministan HKI a tattaunawar Amurka da Iran, ya ce, wannan al-amari ne na cikin gida ga gwamnatin Amurka, amma abinda ya shafi Iran shi ne menene Amurka zata gabatar a kan teburin tattaunawa da ita.

Don haka ne Iran take bukatar kasashen Turai su shigo a dama da su a cikin wannan tattaunawar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Saboda wannan baiwa daga Allah, iyalai da ‘yan uwan mai akuyar suka sanar da shirye-shiryen gudanar da bikin murnar haihuwar ‘ya’yan akuyar a ranar Lahadi mai zuwa a Garun Dakasoye, karamar hukumar Garun Malam ta Jihar Kano, inda za a yi musu suna da kuma karatun Alkur’ani mai girma.

 

A nasa bangaren, mahaifin budurwar, Malam Aliyu dake Garin Dakasoye, ya tabbatar da cewa za su gudanar da bikin domin nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki bisa wannan ni’ima da ya ba su.

 

Ya kara da cewa: “Mun gode wa Allah bisa wannan arziki, kuma muna sa ran gudanar da bikin tare da sanya musu suna domin nuna godiya ga Allah mai daukaka.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Tarayyar Turai EU Ta Mika Bukatunta Ga Kasar Iran.
  • Majiyoyin Diblomasiyya Sun Ce Washington Zata Jagoranci Turawa A Tattaunawa Da Iran
  • Iran Ta Bukaci Kwamitin Tsaro Na MDD Ta Zabi Diblomasiyya Kan Fito Na Fito
  • Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Iran Ta Sauke Hakkin Da Ya Hau Kanta Sauran Bangaren Turai
  • Rahoto: An gudanar da tattaunawa mai tsawo tsakanin Syria da Isra’ila a Landan
  • Pezeshkian: Iran da Masar suna da tsohon tarihi a duniya
  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka