Aminiya:
2025-08-06@00:03:32 GMT

Matashi ya kashe mahaifinsa da adda a Jigawa

Published: 6th, May 2025 GMT

Wani matashi dan shekarar 20 ya fada hannun hukuma kan zargin kashe mahaifinsa da adda a Jihar Jigawa.

Rundunar ’yan sandan Jihar Jigawa ta kama wanda ake zargin kashe mahaifinsa mai shekara 57, da adda.

Wanda aka kashe ya samu raunuka a kafadarsa da wuya da kirjinsa, kuma an kai shi Babban Asibitin Tarayya (FMC) da ke Birnin Kudu, inda aka tabbatar da mutuwarsa.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Litinin 5 ga Mayu, 2025, da misalin ƙarfe 10:00 na safe a unguwar Bakin Kasuwa, da ke Karamar hukumar Gwaram.

Wata mata ta auri maza biyu a lokaci guda a Kano ’Yan PDP 6 a Majalisar Tarayya sun koma APC Daukar nauyin dalibai: Rikici ya barke a Hukumar Raya Arewa Maso Yamma

Kwamishinan ’yan sandan Jihar Jigawa, AT Abdullahi, ya ba da umarnin cewa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) da ke Dutse su karɓi ke cin domin don gudanar da bincike mai zurfi, wanda bayan nan za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu domin ya girbi abin da ya shuga.

Kakakin rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya tabbatar da kama wanda ake zargin tare da ba da tabbacin cewa za a yi adalci kuma za a bayar da ƙarin bayani a nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwaram Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Shirin ACRESAL Zai Samar Da Injinan Ban Ruwa Masu Amfani Da Hasken Rana A Jigawa

A kokarin da Gwamnatin Jihar Jigawa ke yi na kara habbaka harkokin noma, shirin ACRESAL yace sami amincewar gwamnatin na siyo injinan ban ruwa masu amfani da hasken rana guda 3,000 domin tallafawa manoma.

Shugaban Shirin na Jihar, Malam Yahaya Kafin Gana ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse.

Yana mai cewar, samar da injinan ban ruwa masu amfani da hasken rana ga manoman na da nasaba da bunkasa aikin gona a jihar Jigawa.

A cewar sa, shirin ACRESAL na jihar ya sami sahalewar gyaran karin wasu cibiyoyin renon itatuwa guda 3 a sassan jihar.

Malam Yahaya Uba Kafin Gana ya kara da cewar, cibiyoyin renon itatuwan da za’a gyara sune na garuruwan Birnin Kudu da Kafin Hausa da kuma na Gadar Kazaure.

Yana mai nuni da cewar baya ga gyaran cibiyoyin, har Ila yau za’a kuma a samar musu da rijiyoyin samar ruwan sha masu amfani da hasken rana.

Kafin Gana, yace nan bada jimawa ba za su sake zakulo wasu cibiyoyin renon itatuwa guda 5 domin mayar da su irin na zamani.

Yace shirin ya kuma siyo karin Injinan yasar kogi guda 2 domin mara baya ga guda 2 da ake dasu a ma’aikatar kare muhalli ta jihar Jigawan.

Kazalika, ya ce shirin zai samar da hasken wutar lantarki mai amfani da hasken rana a garuruwan Matamu da Safa da Galaucimi da Hannun Giwa da Kwazalewa da Tozarya dake kananan hukumomin Birniwa da Birnin Kudu da Miga da Kafin Hausa da Kazaure har ma da Sule Tankarkar.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ruftawar gini ta kashe uwa da ’ya’yanta 5 a Katsina
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja
  • An Zargin Akantan jihar Nasarawa Da Shiga Harkokin Siyasa
  • An Kaddamar Da Shirin Dashen Itatuwan Dabino Miliyan 50 A Jigawa
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
  • Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • An kama dilallan ƙwaya 28 a cikin barikin sojoji a Kaduna
  • Gwamnatin Jigawa Ta Dauki Manyan Matakan Kare Jihar Daga Ambaliyar Ruwa
  • Shirin ACRESAL Zai Samar Da Injinan Ban Ruwa Masu Amfani Da Hasken Rana A Jigawa