Aminiya:
2025-05-06@18:16:21 GMT

Matashi ya kashe mahaifinsa da adda a Jigawa

Published: 6th, May 2025 GMT

Wani matashi dan shekarar 20 ya fada hannun hukuma kan zargin kashe mahaifinsa da adda a Jihar Jigawa.

Rundunar ’yan sandan Jihar Jigawa ta kama wanda ake zargin kashe mahaifinsa mai shekara 57, da adda.

Wanda aka kashe ya samu raunuka a kafadarsa da wuya da kirjinsa, kuma an kai shi Babban Asibitin Tarayya (FMC) da ke Birnin Kudu, inda aka tabbatar da mutuwarsa.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Litinin 5 ga Mayu, 2025, da misalin ƙarfe 10:00 na safe a unguwar Bakin Kasuwa, da ke Karamar hukumar Gwaram.

Wata mata ta auri maza biyu a lokaci guda a Kano ’Yan PDP 6 a Majalisar Tarayya sun koma APC Daukar nauyin dalibai: Rikici ya barke a Hukumar Raya Arewa Maso Yamma

Kwamishinan ’yan sandan Jihar Jigawa, AT Abdullahi, ya ba da umarnin cewa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) da ke Dutse su karɓi ke cin domin don gudanar da bincike mai zurfi, wanda bayan nan za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu domin ya girbi abin da ya shuga.

Kakakin rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya tabbatar da kama wanda ake zargin tare da ba da tabbacin cewa za a yi adalci kuma za a bayar da ƙarin bayani a nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwaram Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram ta kashe sojoji huɗu a Yobe

’Yan ta’addan Boko Haram da suka kai hari kan rundunar soji ta 27 da ke Buni Yadi a jihar Yobe, sun kashe akalla sojoji hudu tare da lalata kayan aiki da dama na soji.

An kai harin ne kafin wayewar garin Asabar, jim kaɗan bayan da Ƙungiyar Gwamnonin Arewa maso Gabas ta gana a Damaturu domin tattauna hanyoyin haɗin gwiwa wajen yaki da ta’addanci.

Wani jami’in tsaro ya bayyana cewa maharan sun kai mummunan hari suna harbul kan mai da harbe-harbe.

Hedikwatar sojojin Najeriya ta tabbatar da harin inda ta bayyana cewa sojoji na fafatawa da ISWAP a Buni Gari.

ISWAP sun kai wa sojoji hari a Yobe  Rashin tsaro: ‘Ba za mu miƙa wuya ga ’yan ta’adda ba’

Sai dai har yanzu ba a bayyana cikakkun bayanai kan asarar rayuka ba.

Mazauna garin Buni Yadi, mahaifar Gwamna Mai Mala Buni, sun tsere zuwa wurare masu aminci, kuma sojoji sun rufe babbar hanyar da ta hada Yobe da kudancin Borno.

Wannan harin ya biyo bayan wani irin harin da aka kai makonni biyu da suka gabata a yankin Chalie na Buni Yadi inda aka ce an kashe sojoji uku.

Hare-haren ’yan ta’adda sun karu a yankunan Borno, inda suke kai hari kan kauyuka da sansanonin soji.

Gwamnan Jihar Borno Babagana Zulum da sauran shugabanni sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki mataki, suna masu nuni da cewa wasu ƙananan hukumomi na karkashin ikon Boko Haram tare da nuna damuwa game da shigowar ’yan ta’adda daga kasashe makwabta.

Sun yi kira da a kai farmaki a yankin tafkin Chadi da dajin Sambisa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dattawa ta kafa kwamitin lura da gwamnan riƙo na Jihar Ribas
  • An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
  • EFCC Ta Kama Matashi A Kaduna Bisa Zargin Wulaƙanta Naira A Bidiyon Barkwanci
  • ‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa
  • ’Yan fashi sun kashe matashi a Kano
  • An Kama Wani Ɗan Ghana Bisa Zargin Kai Mata Hajji Ba Tare Da Lasisi Ba
  • An Share Filin Noma Kadada 100 Don Karfafa Matasa Su Yi Noma A Babura Jihar Jigawa
  • Sojoji sun kama jami’an tsaro da ke haɗa baki da ’yan ta’adda
  • Boko Haram ta kashe sojoji huɗu a Yobe