Aminiya:
2025-06-21@14:33:17 GMT

Matashi ya kashe mahaifinsa da adda a Jigawa

Published: 6th, May 2025 GMT

Wani matashi dan shekarar 20 ya fada hannun hukuma kan zargin kashe mahaifinsa da adda a Jihar Jigawa.

Rundunar ’yan sandan Jihar Jigawa ta kama wanda ake zargin kashe mahaifinsa mai shekara 57, da adda.

Wanda aka kashe ya samu raunuka a kafadarsa da wuya da kirjinsa, kuma an kai shi Babban Asibitin Tarayya (FMC) da ke Birnin Kudu, inda aka tabbatar da mutuwarsa.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Litinin 5 ga Mayu, 2025, da misalin ƙarfe 10:00 na safe a unguwar Bakin Kasuwa, da ke Karamar hukumar Gwaram.

Wata mata ta auri maza biyu a lokaci guda a Kano ’Yan PDP 6 a Majalisar Tarayya sun koma APC Daukar nauyin dalibai: Rikici ya barke a Hukumar Raya Arewa Maso Yamma

Kwamishinan ’yan sandan Jihar Jigawa, AT Abdullahi, ya ba da umarnin cewa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) da ke Dutse su karɓi ke cin domin don gudanar da bincike mai zurfi, wanda bayan nan za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu domin ya girbi abin da ya shuga.

Kakakin rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya tabbatar da kama wanda ake zargin tare da ba da tabbacin cewa za a yi adalci kuma za a bayar da ƙarin bayani a nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwaram Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu na ƙaddamar da wasu ayyuka a Jihar Kaduna

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu na ziyarar aiki a cikin Jihar Kaduna.

Shugaba Tinubu na ziyarar ne domin ƙaddamar da wasu ayyuka da gwamnan jihar, Uba Sani ya aiwatar a tsawon shekara biyu da ya yi yana mulkin jihar.

Za a dawo da dukkan Alhazai gida ranar 28 ga Yuni – NAHCON Kotu ta ba da belin Natasha kan N50m kan zargin bata sunan Akpabio

Wasu daga cikin ayyukan da shugaban ya ƙaddamar sun haɗa da: asibitin ƙwararru mai gadaje 300 da gwamnatin jihar ta gina don bunƙasa harkokin lafiya.

Daga nan kuma shugaban ya ƙaddamar da cibiyar koyar da sana’o’i, da kuma motocin sufuri masu amfani da iskar gas ta CNG guda 100.

A cikin waɗanda suka yi wa Shugaba Tinubu rakiya sun haɗa da: Mataikamin Shugaban ƙasa na musamman kan harkokin siyasa, Sanata Ibrahim Masara, da mai taimaka wa shugaban kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu da Shugaban Majalisar Wakilai,  Tajudeen Abbas da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau I. Jibrin da wasu manyan jami’an gwamnati.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bom ya kashe mutum 5 a Kano — ’Yan sanda
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 
  • Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata
  • Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom
  • Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina
  • An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 
  • Tinubu na ƙaddamar da wasu ayyuka a Jihar Kaduna
  • An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina
  • Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Tafkin Chadi
  • EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana