Matashi ya kashe mahaifinsa da adda a Jigawa
Published: 6th, May 2025 GMT
Wani matashi dan shekarar 20 ya fada hannun hukuma kan zargin kashe mahaifinsa da adda a Jihar Jigawa.
Rundunar ’yan sandan Jihar Jigawa ta kama wanda ake zargin kashe mahaifinsa mai shekara 57, da adda.
Wanda aka kashe ya samu raunuka a kafadarsa da wuya da kirjinsa, kuma an kai shi Babban Asibitin Tarayya (FMC) da ke Birnin Kudu, inda aka tabbatar da mutuwarsa.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Litinin 5 ga Mayu, 2025, da misalin ƙarfe 10:00 na safe a unguwar Bakin Kasuwa, da ke Karamar hukumar Gwaram.
Wata mata ta auri maza biyu a lokaci guda a Kano ’Yan PDP 6 a Majalisar Tarayya sun koma APC Daukar nauyin dalibai: Rikici ya barke a Hukumar Raya Arewa Maso YammaKwamishinan ’yan sandan Jihar Jigawa, AT Abdullahi, ya ba da umarnin cewa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) da ke Dutse su karɓi ke cin domin don gudanar da bincike mai zurfi, wanda bayan nan za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu domin ya girbi abin da ya shuga.
Kakakin rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya tabbatar da kama wanda ake zargin tare da ba da tabbacin cewa za a yi adalci kuma za a bayar da ƙarin bayani a nan gaba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu na ƙaddamar da wasu ayyuka a Jihar Kaduna
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu na ziyarar aiki a cikin Jihar Kaduna.
Shugaba Tinubu na ziyarar ne domin ƙaddamar da wasu ayyuka da gwamnan jihar, Uba Sani ya aiwatar a tsawon shekara biyu da ya yi yana mulkin jihar.
Za a dawo da dukkan Alhazai gida ranar 28 ga Yuni – NAHCON Kotu ta ba da belin Natasha kan N50m kan zargin bata sunan AkpabioWasu daga cikin ayyukan da shugaban ya ƙaddamar sun haɗa da: asibitin ƙwararru mai gadaje 300 da gwamnatin jihar ta gina don bunƙasa harkokin lafiya.
Daga nan kuma shugaban ya ƙaddamar da cibiyar koyar da sana’o’i, da kuma motocin sufuri masu amfani da iskar gas ta CNG guda 100.
A cikin waɗanda suka yi wa Shugaba Tinubu rakiya sun haɗa da: Mataikamin Shugaban ƙasa na musamman kan harkokin siyasa, Sanata Ibrahim Masara, da mai taimaka wa shugaban kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu da Shugaban Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau I. Jibrin da wasu manyan jami’an gwamnati.