A yau, rukunin farko na tawagar wanzar da zaman lafiya da martanin gaggawa na kasar Sin kashi na biyu wadda za ta je yankin Abyei, ya tashi daga birnin Zhengzhou na kasar Sin, da jirgin saman soja domin gudanar da aikin wanzar da zaman lafiya na tsawon watanni 12. Bugu da kari, ana shirin tura rukuni na biyu na tawagar a tsakiyar watan Mayu.

 

Kasar Sin ta aike da tawagar wanzar da zaman lafiya da martanin gaggawa ta farko zuwa yankin Abyei a watan Mayun shekarar 2024. Tawagar tana dauke da bangarori da dama da suka hada da bangaren tuki, sadarwa, bincike, da kiwon lafiya, wadanda ke yin sintiri da makamai, da kula da wadanda suka jikkata, da kuma masu rakiya daga nesa. Bayan kammala mika ragamar aiki, kashi na farko na tawagar wanzar da zaman lafiya da martanin gaggawa da aka aika zuwa Abyei za su koma kasarsu nan gaba kadan. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tawagar wanzar da zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta yi tsokaci game da matakin Amurka na sanya Najeriya cikin jerin kasashen da ake da damuwa a kansu, inda ta jaddada matsayin Sin na matukar goyon bayan gwamnatin Najeriya, wajen jagorantar al’ummarta zuwa turbar neman ci gaba bisa yanayin da kasar ke ciki.

A ’yan kwanakin nan ne shugaban Amurka Donald Trump, ya sanar da sanya Najeriya cikin jerin kasashen da kasarsa ke kara mayar da hankali a kansu, bisa zargin barazanar da ya ce mabiya addinin Kirista na fuskanta a kasar. Trump ya kara da cewa, idan har gwamnatin Najeriyar ta gaza shawo kan kisan Kiristoci, to Amurka za ta hanzarta dakatar da dukkanin tallafin da take baiwa kasar, kana za ta kaddamar da matakan soji a Najeriyar.

To sai dai kuma a nata martani, ma’aikatar harkokin wajen Najeriyar ta fitar da wata sanarwa, wadda ke musanta zargin na Amurka, tare da jaddada cewa Najeriya na ci gaba da yaki da ayyukan masu tsattsauran ra’ayi, da kare rayukan ’yan kasar, da martaba rayukan mabiya mabambantan addinai da akidu, kana tana biyayya ga dokoki daidai da odar kasa da kasa.

Cikin amsar da ta bayar dangane da tambayar wani dan jarida, Mao Ning ta ce kasar Sin na adawa da wata kasa ta tsoma baki cikin harkokin cikin gidan wasu kasashe na daban, ta hanyar fakewa da batun kare hakkokin addini ko na bil’adama. Kazalika, tana adawa da yawaitar barazanar kakaba takunkumai da amfani da karfin tuwo. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya November 4, 2025 Daga Birnin Sin Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa November 4, 2025 Daga Birnin Sin Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha November 4, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
  • 2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC
  • ’Yan kwangila sun hana zaman majalisa kan rashin biyan haƙƙoƙinsu
  • KADUNA TA ZAMA JIHAR FARKO A NIJERIYA DA TA AIWATAR DA SHIRIN SAMAR DA ABINCIN MAI GINA JIKI GA YARA – UNICEF
  • Prime Ministan Sudan Yayi Gargadi Game Da Aikewa Da Dakarun Tabbatar Da Zaman Lafiya Kasar
  • Kano Pillars ta koma ƙarshen teburin Gasar Firimiyar Nijeriya
  • Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT
  • Marasa Lafiya A Nasarawa Sun Koka Game Da Yajin Aikin Likitoci
  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza