Aminiya:
2025-05-06@17:38:54 GMT

Friedrich Merz ya zama sabon shugaban gwamnatin Jamus

Published: 6th, May 2025 GMT

Friedrich Merz na jam’iyyar CDU ya zama sabon shugaban gwamnatin Jamus.

Majalisar Dokokin Jamus ta Bundestag ta zabi Merz a matsayin sabon shugaban gwamnati lokacin zaɓen zagaye na biyu, bayan ya gaza samun ƙuri’un da yake buƙata a zagayen farko na zaɓen.

A zaɓen farko Merz ya samu ƙuri’u 325 na jam’iyyun ƙawance daga majalisar mai mambobi 630.

Kafin zama shugaban gwamnati ana buƙatar kuri’u 316 kuma jam’iyyar CDU/CSU da kuma jam’iyyar SPD suna da kujerun majalisar 328, fiye da adadin da ake buƙata.

Merz zai maye gurbin Olaf Scholz wanda ya faɗi zaɓen ƙasar da aka gudanar a watan Fabrairu

Upon announcing the second vote, the head of the Union bloc in parliament, Jens Spahn, said, “The whole of Europe, perhaps even the whole world, is watching this second round of elections.”

Da yake sanar da maimaita  kaɗa ƙuri’u a zagaye na biyu, shugaban ƙungiyar Tarayyar Turai a majalisar, Jens Spahn, ya ce, “Gaba ɗaya nahiyar Turai, wataƙila ma duniya baki ɗaya, na kallon wannan zagaye na biyu na zaɓen.”

Jamus wadda ke zaman ƙasa mafi yawan al’umma a cikin ƙasashe 27 na Tarayyar Turai, ita ce ke da mafi girman tattalin arziƙin nahiyar kuma a sahun farko ta fuskar diflomasiyya.

A yanzu dai ajandar da Mista Merz zai sanya a sahun farko sun haɗa da yaƙin da ake yi a Ukraine da kuma manufofin da gwamnatin Donald Trump ta shimfiɗa kan harkokin kasuwanci ƙari kan al’amuran cikin gida, kamar tasowar jam’iyyar masu ra’ayin mazan jiya, mai ƙyamar baƙin haure.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka sake kai sabon hari kan kasar Yemen

Amurka na kara kai hare-hare ta sama a yankuna daban-daban na kasar Yemen.

Babban birnin kasar, Sanaa, shi ne Amurka ta kai wa hari a safiyar yau Litinin.

Wasu hare-hare ta sama da Amurka ta kai a yankunan Bani Matar, Bani Hushaysh da Bani Al-Harith a birnin Sanaa.

Hakazalika, harin da jiragen yakin Amurka suka kai kan wata kasuwa da ke gundumar Shu’ab ta birnin San’a ya lalata shaguna da dama.

A cewar ma’aikatar lafiya ta Yemen, wasu ‘yan kasar 14 ne suka jikkata sakamakon harin da Amurka ta kai a yankin kasuwanci.

Garin Saada da ke arewa maso yammacin kasar, shi ma ya fuskanci hare-hare uku na Amurka.

Bugu da kari, wasu hare-hare ta sama na Amurka sun auna yankuna biyu na yankunan Maarib da al-Jawf na kasar Yemen.

Kakakin Kwamitin Tsaron Amurka James Hewitt, ya ce sojojin Amurka sun kai hare-hare sama da 1,000 a kan Yeman kuma za su ci gaba da kai hare-hare tare da hada kai da Isra’ila.

Hare-haren dai ya biyo bayan nasarar harba makami mai linzami da Yeman ta kai kan yankunan falasdinawa da aka mamaye, wanda ya afkawa filin jirgin sama na Ben Gurion da ke Tel Aviv, lamarin da ya janyo tsaikon zirga-zirgar jiragen sama.

Mutane 8 ne suka jikkata a cewar ma’aikatan jinya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kashi Na Biyu Na Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Sin Ta Tashi Zuwa Abyei
  • Xi Da Shugaban Majalisar Turai Da Shugabar Kwamitin EU Sun Tayawa Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Hulda
  • An kashe mutum 6 a sabon hari a Filato
  • Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini
  • Manzon Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugaba Nguema Na Gabon
  • Tarayyar Turai: Muna Goyon Bayan Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diplomasiyya
  • Amurka sake kai sabon hari kan kasar Yemen
  • Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi
  • Ghana Za Ta Hada Gwiwa Da Gwamnatin Jihar Kebbi Kan Noma