Aminiya:
2025-06-21@06:33:11 GMT

Friedrich Merz ya zama sabon shugaban gwamnatin Jamus

Published: 6th, May 2025 GMT

Friedrich Merz na jam’iyyar CDU ya zama sabon shugaban gwamnatin Jamus.

Majalisar Dokokin Jamus ta Bundestag ta zabi Merz a matsayin sabon shugaban gwamnati lokacin zaɓen zagaye na biyu, bayan ya gaza samun ƙuri’un da yake buƙata a zagayen farko na zaɓen.

A zaɓen farko Merz ya samu ƙuri’u 325 na jam’iyyun ƙawance daga majalisar mai mambobi 630.

Kafin zama shugaban gwamnati ana buƙatar kuri’u 316 kuma jam’iyyar CDU/CSU da kuma jam’iyyar SPD suna da kujerun majalisar 328, fiye da adadin da ake buƙata.

Merz zai maye gurbin Olaf Scholz wanda ya faɗi zaɓen ƙasar da aka gudanar a watan Fabrairu

Upon announcing the second vote, the head of the Union bloc in parliament, Jens Spahn, said, “The whole of Europe, perhaps even the whole world, is watching this second round of elections.”

Da yake sanar da maimaita  kaɗa ƙuri’u a zagaye na biyu, shugaban ƙungiyar Tarayyar Turai a majalisar, Jens Spahn, ya ce, “Gaba ɗaya nahiyar Turai, wataƙila ma duniya baki ɗaya, na kallon wannan zagaye na biyu na zaɓen.”

Jamus wadda ke zaman ƙasa mafi yawan al’umma a cikin ƙasashe 27 na Tarayyar Turai, ita ce ke da mafi girman tattalin arziƙin nahiyar kuma a sahun farko ta fuskar diflomasiyya.

A yanzu dai ajandar da Mista Merz zai sanya a sahun farko sun haɗa da yaƙin da ake yi a Ukraine da kuma manufofin da gwamnatin Donald Trump ta shimfiɗa kan harkokin kasuwanci ƙari kan al’amuran cikin gida, kamar tasowar jam’iyyar masu ra’ayin mazan jiya, mai ƙyamar baƙin haure.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 

Brig.-Gen. Abu-Mawashi ya kara da cewa an kama ‘yan ta’adda 14,138 da sauran masu aikata laifuka yayin da aka ceto mutane 5,365 a cikin wannan lokaci.

 

Abu-Mawashi ya ci gaba da cewa, sojojin sun kwato daruruwan makamai da kuma harsashi da yawa duk acikin wannan lokaci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista
  • 2027: Manyan ’Yan adawa na neman rajistar sabuwar jam’iyya
  • Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani
  • Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump
  • Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho
  • Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi
  • An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 
  • Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC
  • Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano
  • “Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki