Friedrich Merz ya zama sabon shugaban gwamnatin Jamus
Published: 6th, May 2025 GMT
Friedrich Merz na jam’iyyar CDU ya zama sabon shugaban gwamnatin Jamus.
Majalisar Dokokin Jamus ta Bundestag ta zabi Merz a matsayin sabon shugaban gwamnati lokacin zaɓen zagaye na biyu, bayan ya gaza samun ƙuri’un da yake buƙata a zagayen farko na zaɓen.
A zaɓen farko Merz ya samu ƙuri’u 325 na jam’iyyun ƙawance daga majalisar mai mambobi 630.
Kafin zama shugaban gwamnati ana buƙatar kuri’u 316 kuma jam’iyyar CDU/CSU da kuma jam’iyyar SPD suna da kujerun majalisar 328, fiye da adadin da ake buƙata.
Merz zai maye gurbin Olaf Scholz wanda ya faɗi zaɓen ƙasar da aka gudanar a watan Fabrairu
Upon announcing the second vote, the head of the Union bloc in parliament, Jens Spahn, said, “The whole of Europe, perhaps even the whole world, is watching this second round of elections.”
Da yake sanar da maimaita kaɗa ƙuri’u a zagaye na biyu, shugaban ƙungiyar Tarayyar Turai a majalisar, Jens Spahn, ya ce, “Gaba ɗaya nahiyar Turai, wataƙila ma duniya baki ɗaya, na kallon wannan zagaye na biyu na zaɓen.”
Jamus wadda ke zaman ƙasa mafi yawan al’umma a cikin ƙasashe 27 na Tarayyar Turai, ita ce ke da mafi girman tattalin arziƙin nahiyar kuma a sahun farko ta fuskar diflomasiyya.
A yanzu dai ajandar da Mista Merz zai sanya a sahun farko sun haɗa da yaƙin da ake yi a Ukraine da kuma manufofin da gwamnatin Donald Trump ta shimfiɗa kan harkokin kasuwanci ƙari kan al’amuran cikin gida, kamar tasowar jam’iyyar masu ra’ayin mazan jiya, mai ƙyamar baƙin haure.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a
A cewar shugaban kwamitin, Katsina na kuma goyon bayan batun sauke wasu ikon gwamnati daga matakin tarayya zuwa jihohi, saka sarakunan gargajiya a cikin kundin tsarin mulki da kuma sake fasalin harkokin kuɗi.
Sanata Ibrahim ya shaida wa kwamitin cewa an tattara dukkan ra’ayoyi da buƙatun jama’ar Katsina, tare da gabatar da su a cikin takardar matsayar.
Tun da farko, yayin da yake ƙaddamar da taron jin ra’ayoyin jama’a, shugaban kwamitin majalisar dattawa kan gyaran kudin tsarin mulki ya buƙaci a riƙa yin irin wannan taron lokaci zuwa lokaci domin ya dace da halin da ake ciki.
Sanata Barau Jibrin, wanda shi ne mataimakin shugaban majalisar dattawa, ya tabbatar da cewa dukkan abubuwan da aka tattara daga gwamnati, ƙungiyoyi da jama’a za a gabatar da su a gaban majalisar domin yin doguwar tattaunawa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp