2025-11-05@12:08:42 GMT
إجمالي نتائج البحث: 710
«Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Iran»:
(اخبار جدید در صفحه یک)
Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci ya jaddada cewa: Iran ba za ta taba yin watsi da inganta uranium ba, kuma tattaunawa da Amurka za ta haifar da illa A jawabin da ya yi wa al’ummar Iran ta gidan talabijin a yammacin jiya Talata, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce: Ba za su mika wuya ga matsin lamba kan wani lamari na su ba. A cikin jawabinsa ta gidan talabijin ga al’ummar Iran a daren jiya, Jagoran ya taya al’ummar Iran murnar shigowar watan Mehr (23 ga watan Satumba, bisa kalandar Iran), da watan komawa makarantu da jami’o’i da ilmantarwa, da kuma shirin kaddamar da miliyoyin matasa a fadin kasar wajen samun ilimi da mulki. Wannan...
Shugaban kasar Afirka Ta kudu Cyril Ramaphosa da ya gabatar da jawabi a taron babban zauren MDD ya jaddada matsayar kasarsa na son ganin an bai wa al’ummar Falasdinu kasarsu akan iyakar 1967. Da yake Magana akan abinda yake faruwa yanzu a Gaza, shugaban kasar ta Afirka Ta Kudu ta caccaki HKI akan yadda take azabatar da al’ummar Falasdinu a dunkule. Haka nan kuma ya yi kira da a kawar da dukkanin abubuwan da suke kawo cikas wajen kafawa Falasdinawan kasar tasu. Share 0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks...
Majalisar Wakilai ta bayyana cewa ta amince da duk wasu tsare-tsare da dabarun karɓo rancen kuɗaɗe na Shugaba Bola Tinubu, bisa la’akari da ƙoƙarin da yake yi na farfaɗo da tattalin arziki da kuma rage talauci a ƙasar nan. Shugaban Majalisar, Abbas Tajudeen ne ya bayyana hakan a yayin da yake jawabi ranar Litinin, a taron shekara-shekara karo na takwas kan bitar kasafin kuɗaɗe na majalisun dokokin nahiyyar Afirka (African Network of Parliamentary Budget Offices) da ke gudana a Abuja. Sarkin Ruman Katsina ya rasu Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a Neja Abbas ya ƙaryata raɗe-raɗin cewa majalisar ta ƙi amincewa da tsare-tsaren karɓo rance na shugaban ƙasar, inda ya ce zantuka ne marasa...
Majalisar Wakilai ta bayyana cewa ta amince da duk wasu tsare-tsare da dabarun karɓo rancen kuɗaɗe na Shugaba Bola Tinubu, bisa la’akari da ƙoƙarin da yake na farfaɗo da tattalin arziki da kuma rage talauci a ƙasar nan. Shugaban Majalisar, Abbas Tajudeen ne ya bayyana hakan a yayin da yake jawabi ranar Litinin, a taron shekara-shekara karo na takwas kan bitar kasafin kuɗaɗe na majalisun dokokin nahiyyar Afirka (African Network of Parliamentary Budget Offices) da ke gudana a Abuja. Sarkin Ruman Katsina ya rasu Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a Neja Abbas ya ƙaryata raɗe-raɗin cewa majalisar ta ƙi amincewa da tsare-tsaren karɓo rance na shugaban ƙasar, inda ya ce zantuka ne marasa tushe...
Kwamandan sojan Iran Amir Hatami wanda ya gana da kwamandan dakarun kare juyin musulunci Janar Muhammad Pakpour saboda tunawa da makon hadin kai, ya kara da cewa; Bayan cin nasarar juyin musulunci a Iran, Iran da al’ummarta sun fara aiki tukuru domin kare cikakken ‘yancin Iran.” Har ila yau, Amir Hatami ya yi ishara da hadin gwiwa a tsakanin sojojin da dakarun kare juyin juya halin yana a matsayin ginshikin tsaron kasar Iran, kuma wata kofa ta kai wa mataki na koli na tsaro. A gefe daya dakarun kare juyin musulunci ( irgc) sun jaddada matsayarsu ta ci gaba da zama cikin Shirin fuskantar abokan gaba. A cikin wata sanarwa da suka fitar a farkon makon tsaro mai alfarma, na...
Shugaban kasar Korea Ta Arewa Kim jung Un ne ya sanar da cewa kasarsa ta kera wani sabon makami na sirri, kuma ta samu ci gaba sosai a fagen nazari da binciken kayan tsaro. Shugaban kasar ta Korea Ta Arewa Kim Jun Ung wanda ya yi Magana da kamfanin dillancin labarun kasar ya kara da cewa; Sabbin makaman da su ka kera za su taimaka matuka wajen karfafa sojojin kasar.” Haka nan kuma ya ce, kasar Korea ta Arewa ta kuma karfafa sojojinta na ruwa ta hanyar kara samar da jiragen ruwa na yaki masu ninkaya a karkashin ruwa.” Kamfanin dillancin labarun Korea Ta Arewa ya sanar da cewa, a ranar Juma’ar da ta gabata ne shugaban kasar Kim Jun...
Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci na Iran sun bayyana cewa: Duk wani sabon kuskuren lissafin makiya zai fuskanci mayar da martani mai muni A cikin wata sanarwa da suka fitar a farkon makon tsaro mai alfarma, na ranar tunawa da arangama da gwamnatin Saddam ta yi da Jamhuriyar Musulunci ta Iran a tsakanin shekarun 1980-1988, dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran (IRGC) sun jaddada cewa: Duk wani sabon kuskuren lissafi da makiya za su yi, za su fuskanci mummunan martani da zai zame babban darasi a gare su. A cikin bayanin da suka yi na farkon makon tsaro na dakarun IRGC sun bayyana cewa: A hakikanin gaskiya makon tsaro, biki ne na nasarar gwagwarmayar jama’a, kuma abin...
Ministan harkokin wajen Falasdinawa Varsen Aghabekian Shahin, ta godewa kasashen duniya da suka amince da samuwar kasar Falasdinu ya zuwa yanzu kuma kuma wadanda suke shirin yinhaka, sannan tana kodaitar da sauran kasashen duniya da su yi hakan. Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shahin tana fadar haka a taron yan jarida da ta kira a yau Lahadi a birnin Ramallah, sannan ta kara da cewa ya zuwa yanzu kasashe da dama sun bayyana amincewarsu da kasar Falasdinu, Kuma sakone mai kyau ga Falasdinwa, kuma banda haka wannan sakonnin fata ne na samuwar kasar Falasdinu mai zaman kanta. Ta kara da cewa, amincewa da kasar Falasdinu mai zaman kanta yana nufin HKI bata da iko a kanta....
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
A wata sanarwa da dakarun kare juyin juya halin musulunci ta Iran ta fitar a jiya Asabar ya ce; Abinda ya faru a lokacin yakin tsaron kasa mai tsarki na farko da na biyu, mayar da martanin Iran ya haifar da sakamako mai karfi wanda aiki ne na tsawon lokaci. Haka nan kuma sanarwar ta ce, duk wani sabon kuskure da abokan gaba za su yi na kawo wa Iran hari, to jamhuriyar musulunci ta Iran za ta sami fifiko akansu a fagen daga, domin martaninta zai zama mai tsanani. Dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran sun kuma bayyana makon tsaron kasa mai tsarki na tunawa da yake-yaken da aka kallafawa Iran, a matsayin daya daga cikin lokuta...
Gwamnatin yahudwan sahuniya ta kaddamar da hari da makami mai linzami kan wata motar hawa a layin Nabatiya- marjiyun dake khardali a kudancin labanon a ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da buda wuta da aka cimma tun 27 ga watan nuwamba na shekara ta 2024. Wannan hari wani bangare ne na kata yarjejeniyar da bangarorin biyu suka cimma, da hakan ya jawo mutuwar daruruwan mutane kuma ke kara jawo zaman dar-dar yankunan dake iyakar kasar da kuma HKI. Rahotanni da kafafen yada labarai na kasar labanon suka fitar ya nuna cewa wadannan hare haren wani nau’I ne na keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da aka cimma , da kuma ci gaba da wuce gona da iri a yankin...
Shugaban kasar Iran Masud pezishkiyan ya bayyana cewa Iran ba za ta mika wuya ga bukatun da suka wuce kima ba, kuma za ta iya shawo kan duk wani takunkumi da aka kakaba mata, Shugaban ya fadi haka ne a wajen bukin karrama yan kasar da suka samu lambobin yabo a gasar Olympic ta kimiyya ta duniya , bayan da kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya ya kada kuriar amincewa da kudurin dawo da takunkumi dake da alaka da shirinta na nukiliya. Haka zalika shugaban kasar yace makiya suna iya kai hari kan sakamakon binciken fasaha da aka yi, amma kwararru da masana ilimin kimiya wadanda suka samar da wadannan naurorin su ne hakikanin gaskiyar dukiya ga kasarmu, don haka...
Wata mata ta haifi jarirai huɗu — maza biyu da mata biyu — a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Tarayya ta Kimiyyar Kiwon Lafiya (FUHSTHA) da ke Azare, a ranar Alhamis, 18 ga Satumba, 2025. Sakataren yaɗa labarai na asibitin, Abdu Mohammed, ya shaida wa Aminiya cewa Malama Hauwa ta haifi yaran ne ta hanyar tiyata, kuma tana ci gaba da jinya tare da ’yan huɗun. A washegarin haihuwar, Hajiya Halima Garba, matar shugaban asibitin (CMD), ta ziyarci mai jegon tare da mijinta da manyan ma’aikatan asibitin. Ta taya iyalan murna tare da addu’ar samun lafiya cikin gaggawa. ’Yan bindiga sun kashe basarake, sun tarwatsa mutane a Sakkwato Kwalara ta kashe mutane 58, wasu sun kamu a Bauchi Kamar yadda ta...
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Iran ba ta yarda da duk wani aiki na siyasa ko matsin lamba na rashin adalci ba Rafael Grossi, babban darektan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, ya gana da ministan harkokin wajen Iran Seyyed Abbas Araqchi ta wayar tarho. Kamfanin dillancin labaran Tasnim ya bayar da rahoton cewa, a yayin wannan kiran, bangarorin biyu sun tattauna batutuwan baya-bayan nan a yarjejeniyar da aka kulla tsakanin Iran da hukumar ta IAEA, da batun maido da takunkuman da aka kakabawa Iran, da kuma matakin ci gaba da dage takunkumin da aka kakabawa Iran a kwamitin sulhu na MDD. Araqchi da Grossi sun cimma yarjejeniya a birnin Alkahira kan sabbin hanyoyin hadin gwiwa...
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta jaddada cewa: Iran tana da ‘yancin mayar da martani ga duk wani mataki da ya sabawa doka Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta fitar da wata sanarwa a jiya Juma’a dangane da haramtaccen matakin da kungiyar Tarayyar Turai Troika ta dauka na mayar da takunkumin Majalisar Dinkin Duniya kan Iran a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ta hanyar yin amfani da tsarin warware takaddama kan shirin hadin gwiwa na hadin gwiwa (JCPOA) (yarjejeniyar nukiliya ta 2015) da kuma kuduri mai lamba 2231. Bayanin ya ci gaba da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta yi Allah-wadai da matakin da kasashen Turai uku wato Faransa da Jamus da kuma Birtaniya suka dauka na yin amfani da...
Mataimakin ministan harkokin wajen Iran mai kula da harkokin shari’a da na kasa da kasa ya mayar da martani kan zargin shugaban Faransa Emmanuel Macron Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin shari’a da na kasa da kasa, Kazem Gharibabadi, ya musanta zargin da shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya yi a baya-bayan nan, yana mai jaddada cewa, a yayin da ministan harkokin wajen Iran ke magana, ko tattaunawa, ko ya aika da sako, ko gabatar da wata shawara, wannan mataki ya nuna ra’ayin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma yana samun matsaya na cikin gida, kamar yadda aka gani a tattaunawar fahimtar juna tare da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya a birnin Alkahira. A cikin...
Daga baya an ƙara nata wani nauyin kula da Tashoshin Warri, Koko, Burutu da kuma ta Sapele, waɗanda kamfanonin ƴ an kasuwa masu zaman kansu ne, ke tafiyar da su, amma har zuwa yau, mahukunta a NPA ne, ke tafiyar da duk wata ragamar hukumar baki ɗaya. A shekaru da dama da suka gabata, matsaloli da dama, sun dabaibaye NPA da suka haɗa da, cin hanci da rashawa da rashin ingantattun kayan aiki, musamman na zamani da sauransu, inda waɗannan matsalolin suka haifar wa da NPA koma baya matuƙa, musamman na wajen zama a kan gaba wajen gudanar da harkar hada-hadar kasuwanci a nahiyar Afirka. Amma, za mu iya cewa, Allah san barka da naɗa Dakota Abubakar Ɗantsoho, a matsayin...
Wasu kafafen diblomasiyya nakasashen yamma sun tabbatarwa wakilin tashar talabijin ta Al-mayadeen na kasar Lebanon kan cewa gwamnatin Amurka ce zata jagoranci kasashen yamma wajen tattaunawa da karar Iran. Majiyar ta kara da cewa turawan sun mika wuya ga takurawar washintong don jagorantar tattaunawa da JMI kan shirinta namakamashin nukliya da kuma batun yin watsi da sabon yarjeniyar da Iran ta kulla da hukumar IAEA a al-kahira a baya bayan nan. Banda haka suna son suyi amfani da tsarin Snapbackdon kara takurawa JMI. Sannan kasashen turaiba zasu sararawa JMI ko kadan ba a takurawar da suke mata a tattaunawar. Duk da cewa yarjeniyar Al-kahiri wani bangaremai muhimmanci ne ga bukatun kasashen Turai daga Tehran, amma har yanzun akwai sabbin sharuddan...
Rahotannin cibiyoyin kididdiga a HKI sun ambaci cewa, ana ci gaba da samun yin hijirar yahudwa zuwa waje wanda shi ne mafi girma a cikin shekaru da dama. Jaridar “Ma’ariv” ta amabto wani makwararre a fagen kididdiga yana cewa; Shekarar 2024 ta fuskanci ficewar mutane masu yawan gaske daga “Isra’ila” saboda yakin da ake yi a Gaza. Haka nan kuma ya ce, wannan shi ne karo na hudu a cikin shekaru masu yawa da ake yin hijira daga Isra’ila. Bugu da kari ya ce, baya ga yahudawa da akwai ‘yan hijira da dama da suke ficewa da hakan yake da jan hankali sosai. Haka nan kuma ya ambaci wasu daga cikin dalilan da su ka Sanya ake yin hijira da...
Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyid Abdulmalik al-Husy wanda ya gabatar da jawabi a yau Alhamis ya bayyana cewa: Makaman gwagwarmaya suna a matsayin lamuni ne nah ana abokan gaba yi wa al’umma kisan kiyashi da hare-haren wuce gona da iri. Da yake Magana akan abinda yake faruwa akan doron ruwan “Red Sea” Sayyid Abdulmalik al-Husi ya ce; Duk wani yunkuri na bayar da kariya ga jiragen ruwan HKI, da kuma a cikin mashigan ruwa da suke a yankin, ba za su ci nasara ba.” Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya kuma ce; Dukkanin hare-haren da su ka kai a makon da ya shude a ruwan “Red Sea” an kai shi ne akan jragen ruwan HKI kadai. Har ila yau,...
Zhakom ya ƙara da cewa, wanda aka cafken da kuma kayayyakin da aka ƙwato suna hannun rundunar domin ci gaba da bincike, kuma rundunar za ta ci gaba da farmakar wadanda suka tsere daga haramtacciyar masana’antar kera makaman. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Iran ta cika hakkinta, yanzu kuma turai ne ake jiran ta cika nata hakkokin Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa, a wani mataki da Iran ta dauka na nauyin shiga tattaunawa da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, domin tsara wani sabon daftarin aiki mai ma’ana kan yadda za a aiwatar da alkawuran da ta dauka na kare hakkokin da suka hau kanta, yanzu kuma ana jiran Turai ta cika nata alkawuran. A wata tattaunawa ta wayar tarho tare da ministocin harkokin wajen Faransa, Jamus, da Birtaniya, da kuma jami’in kula da harkokin waje na EU, Araqchi ya ce: “Dole ne sauran bangarorin su yi amfani da...
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Gwamnatin mamayar Isra’ila na aikata kisan kiyashi a Gaza, kuma magoya bayanta suna da hannu a ciki Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya jaddada cewa: Rahoton kwamitin binciken gaskiya na Majalisar Dinkin Duniya ya tabbatar da cewa, laifukan da haramtacciyar kasar Isra’ila ta aikata a Gaza sun kai na “kisan kare dangi”, inda ya yi kira ga masu kare gwamnatin ta Isra’ila da su daina shiga da hada baki wajen aikata wadannan laifuka kan al’ummar Falastinu. Baqa’i ya bayyana cewa: Kwamitin bincike mai zaman kansa na kwamitin kare hakkin bil’adama na Majalisar Dinkin Duniya kan laifukan da ake aikatawa a Falasdinu da aka mamaye karkashin jagorancin fitacciyar marubuciya Navi Pillay,...
Iran Ta Yi Nasarar Gwajin Tauraron Dan’adam ” Nahid 2″ Da Zai Samar Wa Yankunan Karkara Hanyar Sadarwa Ta “Internet”
Ministan sadarwa na Iran Sitar Hashimi ya bayyana cewa, an sami nasara a gwajin da aka yi na sabon tauraron dan’adam, mai suna “Nahid 2” wnada aikinsa shi ne samar da hanyoyin sanarwa na internet masu nagarta. Ministan sadarwar ya kuma ce dukkanin bangarorin tauraron dan’adam din sun yi aiki yadda ake so a yayin gwajin da hakan yake a matsayin wani ci gaba a fagen sadarwa a Iran. Har ila yau ministan Sadarwar Sitar Hashimi ya kuma ce; A tsakanin kauyuka 10,000 da ba su da hanyoyin sadarwa, yanzu an rage su da 2000, kuma ana ci gaba da aiki tukuru domin isa ga kauyunan da suke nesa,masu wahalar zuwa. Ministan sadarwar na Iran ya kuma kara da cewa;...
Rahotanni sun bayyana cewa kasar iran ta bayyana sabbin kayayyaki guda 5 da ta kera a wajen babban taron kere-kere na kasa da kasa karo na 23,kuma dukkansu kamfanonin kasar iran ne suka yi su domin rage dogaro da kayyakin kasashen waje. Taron ya samu halartar mataimakin shugaban hukumar kula da kimiya da fasaha ta kasa da sauran shuwagabannin kamfanoni inda ya nuna irin karfin iran wajen kere-kere da kuma mayar da hankali kan kamfanoni dake filin shakatawa na pardis technology park. Daga cikin magungunan da aka gabatar a wajen akwai Sirolimus wanda Zist takhmir company ya kera, kuma magungunan rigakafi ne da ake amfani da su wajen hana dashen gabobin jiki da kuma kula da cututtuka da ba kasafai...
Yadda kasashen yammacin duniya suka ki sauke nauyin dake wuyansu, ya danne wa kasashe masu tasowa hakkinsu. Misali, a lokacin da ake samun bazuwar annobar COVID-19, dimbin kasashen yamma sun yi ajiyar alluran rigakafi a gida, inda suka hana fitar da su zuwa ketare, da musayar fasahohi masu nasaba da su. Sai dai a lokacin, hukumomi masu kula da harkokin kasa da kasa, kamar su Hukumar Lafiya ta Duniya, da Majalisar Dinkin Duniya dukkansu sun kasa tilasta musu sauya manufofinsu. Wannan tsarin kasa da kasa, idan mun bar shi haka ba tare da wani sauyi ba, to, wata rana za mu ga an koma tsarin zalunci na zamanin mulkin mallaka, wanda zai yi barazana ga hakkin rayuwa, da raya kai...
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Human Rights Watch ta ce: Laifin da Isra’ila ta yi na kashe ‘yan jaridun Yemen babban ta’addanci ne Kungiyar kare hakkin bil’ adama ta Human Rights Watch ta tabbatar da cewa: Harin da yahudawan sahayoniyya suka kai a ranar 26 ga watan Satumba kan ‘yan jaridun kasar Yemen, wanda ya yi sanadiyar mutuwar ‘yan jarida sama da 30, laifi ne da ba za a iya kubutar da girman laifin kan wanda ya aikata ba. A cikin rahoton baya-bayan nan, kungiyar ta fitar ta bayyana cewa, ta tattara bayanan harin da makiya yahudawan sahayoniyya suka kaddamar a ranar 10 ga watan Satumba kan hedkwatar kafafen yada labarai a kasar Yemen, kuma ta yi la’akari da wannan...
An garzaya da ita asibiti, amma daga baya likitoci suka tabbatar da mutuwarta. ’Yansanda sun kama Bosede kuma suna bincike a kan lamarin. Kakakin rundunar, DSP Olusola Ayanlade, ya ce za su tabbatar da adalci. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
JMI ta zama zakara a gasar damben girgajiya ta kasa da kasa bayan ta fara shiga gasar shekaru 12 da suka gabata . Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi yana taya tawagar yan damben murna da nasarar da suka samu, ya kumakara da cewa wannan shi ne nasara ta wasannan kasa-da kasa har guda 6 wadanda Iran take samun lambobin zakara a cikinsu a wannan shekarar. Labarin ya kara da cewa yan damben Iran sun sami wannan nasarar kwana guda kafin a kammala gasar. An bayyana nasarar da yan damben Iran suka samu ne a jiya Litinin da yamma a birnin Zagreb inda aka gudanar da gasar. Sun sami lambobin...
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha
Ministan harkokin wajen Iran ya gana da takwarorinsa na Qatar, Turkiyya, Pakistan da Lebanon a Doha fadar mulkin kasar Qatar Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya gana da takwaransa na Qatar a gefen taron ministocin harkokin wajen kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC a birnin Doha. Doha ta sanar da cewa, fira ministan kasar Qatar kuma ministan harkokin wajen kasar ya yi nazari kan al’amuran yankin na baya-bayan nan yayin ganawarsa da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi. A yayin wannan taro, harin da yahudawan sahayoniyya suka kaddamar a birnin Doha shi ne babban abin da ake tattaunawa akai. Araqchi yayi Allah wadai da harin da gwamnatin mamayar Isra’ila ta kai, yana mai tabbatar da goyon bayan Jamhuriyar...
Babban sakatare tsaron kasa na Iran Ali Larijani ya fadi cewa ya zama wajibi kasashen musulmi su hada kai waje guda don tunkarar rashin hankalin Isra’ila da take yi kan alummar falasdinu. A cikin wani bayani da ya aike da shi a shafinsa na X ya ce wannan mataki zai tilastawa shugaban Amurka yin gaggawa wajen mika umarninsa ga gwamnatin Isra’ila bisa hujjar kawo zaman lafiya a duniya da kuma bada kyautar zaman lafiya ta Nobel. Kasar Qatar ta sanar da kiran zaman gagganawa na kasashen larabawa da na musulmi a ranar litinin mai zuwa domin tattaunawa game da harin da Isra’ila ta kai domin kashe jagororin kungiyar Hamas a kasarta. Manyan jami’an hamas da suke tattaunawa kan batun bukatar...
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya sanar da yiwuwar sake yin wani taro da babbar jami’ar kungiyar tarayyar Turai kan harkokin waje Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya sanar da yiwuwar sake ganawa da babbar jami’ar harkokin wajen kungiyar tarayyar turai Kaya Kalas. A cikin wata sanarwa da ya fitar a yammacin jiya Juma’a, Araqchi ya ce, “Akwai yiwuwar sake yin wani taro da jami’ar harkokin wajen kungiyar tarayyar Turai, kuma hakan ya dogara ne da shawarar Turai. Dangane da tattaunawar da aka yi a birnin Alkahira, ya ce, wadannan shawarwarin masu muhimmanci ne sosai, da kuma shawarwarin da ake yi a bayan yaki, inda hotunan shahidai ke wucewa a kan idonun mutane daya bayan daya, ba tattaunawa...
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa; Bai kamata a ji tsoron tattaunawa ba saboda hanya ce ta jaddada zaman lafiya Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Ana gudanar da dukkan ayyukan diflomasiyya cikin cikakken hadin kai tare da hukumomin da abin ya shafa, kuma bisa takamaiman umarni da ayyuka. Ya ce: “Ba za su taba yin kasa a gwiwa ba wajen kare hakki da tsaron al’umma, kuma ba za su taba tasirantuwa da kage-kagen yanayi ba, kuma za su yi aiki da karfi da azama wajen tabbatar da muradun al’ummar Iran.” Wannan dai ya zo ne a wata hira da gidan talabijin na kasar Iran a yammacin jiya Alhamis, inda ministan harkokin wajen kasar Abbas...
Kasar yamen itace kasar larabawa daya tilo a kasashen musulmi ta duniya da ta mike ta kalubalanci yakin kare dangi da HKI take ci gaba da yi kan yankin falasdinu, da Israila ta kira da yunkurin samar da fadaddiyar Isra’ila. Wani babban jami’in soji na kasar yaman ya fadi cewa za su ladabatar da isra’ila kan wannan hari da ta kai, Isra’ila ta kai hari kan wuraren farar hula, inda mutane da dama suka yi shahada wasu kuma suka jikkata, kuma duk wannan sadaukarwa ba zai hana ci gaba da goyon bayan alummr gaza ba, da kuma ladabtar da Isra’ila. Wasu majiyar labarai ciki har da kamfanin dillancin labarai na reuters da ma tashar talabijin din isra’ila sun sanar cewa...
Pezeshkian: Dole Kasashen Musulmi Da Na Larabawa Su Fito Fili Su Yi Allah Wadai Da Harin Isra’ila Kan Qatar
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Dole ne kasashen musulmi da na Larabawa su yi Allah wadai da yin tir da harin wuce gona da iri da gwamnatin mamayar Isra’ila ta kai kan kasar Qatar Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada goyon bayan Jamhuriyar Musulunci ta Iran ga ‘yan uwanta na kasar Qatar, yana mai cewa: Dole ne kasashen musulmi su dauki mataki da gaske wajen tofin Allah tsina kan gwamnatin mamayar Isra’ila da yin tir da laifukan da take aikatawa kan al’ummomi. A cikin wata tattaunawa ta wayar tarho da Sarkin Qatar Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani a yammacin jiya Talata, shugaba Pezeshkian ya yi Allah wadai da harin wuce gona da irin da yahudawan sahayoniyya suka...
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta yi watsi da abinda yazo cikin bayanin bayan taro na kungiyar kasashen Larabawa na cewa tsiran Abu Musa da Tumb babba da karami mallakin UAE ne. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran a nan Tehran na fada a cikin bayanin da ta fitar a safiyar yau Talata kan cewa, da wadannan kasashen sun fidda bayanai kan al-ummar gaza wadanda HKI take kissa dare da rana da yafi masu. Bayanin ya bukaci kasashen Larabawa su maida hankalinsu kan kasar Falasdinu da aka mamaye su kum yi aiki don hada kan a-ummar musulmi su tunkari HKI a kan ta’asan da take aikatawa a gaza, da sun yi abinda...
Rahotanni sun bayyana cewa ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya tattauna da takwaran aikinsa na kasar masar badar albadelatty ta wayar tarho inda suka tattauna game da batutuwan da suka shafi yankin da kuma irin ci gaban da aka samu, kuma sun mayar da hankali kan batutuwan da suka shafi Gaza da kuma shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya. Iran dai na neman isar da sakon diflomasiyya ne a daidai lokacin da ake ci gaba da takun saka tsakaninta da kasashen yammacin duniya dangane da shirinta na nukiliya. A halin da ake ciki, Masar ta dauki kanta a matsayin babbar mai shiga tsakani a rikicin Gaza, inda ta daidaita alakar ta da kasashen Larabawa da ke makwabtaka da...
Kafar yada labaran Syria ta ce Isra’ila ta kaddamar da hare-hare ta sama a wasu sassa na tsakiya da kuma yammacin kasar. Rahotanni sun ce an kai hare haren ne a kusa da Homs da Palmyra da kuma birnin Latakia da ke gabar ruwa. Ana ganin Isra’ilan ta kai hare-haren kan sansanonin Soji ne. Ba a bayar da rahoto akan mutanen da hare haren ya shafa ba, haka ita ma Isra’ilan ba ta ce komai a kan harin ba. Isra’ila dai na kai hare-hare ta sama tun bayan hambarar da gwamnatin shugaba Bashar al- Assad a watan Disambar bara. ana ta bangaren gamnatin kasar siriya ta tir da kai harin tare da bayyana shi a matsayin keta dokokin kasa da...
Ya ce: “A Zamfara an kashe ‘yan ta’adda 30 a hare-haren sama da kasa, yayin da masu tada kayar baya 76 da suka hada da mata da kananan yara suka mika wuya ga jami’an tsaro. “Rundunar ‘yansanda ta bayar da rahoton kama mutane 1,950 da ke da alaka da munanan laifuka, garkuwa da mutane, da kuma fashi. An kubutar da jimillar mutane 141 da aka yi garkuwa da su. Ya ce hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta kama sama da kilo 66,000 na miyagun ƙwayoyi. A ɓangaren Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annuti (EFCC), ya ce hukumar ta yi nasarar gurfanar da ƙorafe-ƙorafe 588 ga kotu a cikin...
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya zanta ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Masar Abdulatty donga ne da shirin nukliyar kasar Iran da kuma al-amuran gabasa da tsakiya musamman Gaza. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa a halin yanzu dai kasar Masar ta zama mai shiga tsakanin Iran da kasashen yamma dangane da shirin Iran na makamashin nuliya. Haka ma dangane da yaki a Gaza, kasar tana taka rawa don ganin an kawo karshen yakin da kuma shigo da abinci cikin cikin Gaza. Kasashen Iran da Masar dai suna kai kawo tsakanin kasashen musulmi da kuma kasashen larabawa don don dakatar da wannan kissan kiyashin da ke faruwa a Gaza. A cikin yan...
Ya bayyana karya ka’idojin da aka shimfiɗa kan amso basussukan a matsayin “babban abin damuwa da fargaba kan ɗorewar tattalin arzikin kasar,” yana mai jaddada cewa, akwai buƙatar samar da “sabbin tsaruka masu ƙarfi, da za su daidaita hanyoyin karɓar rance na gaskiya, da kuma ƙuduri na bai ɗaya don tabbatar da cewa, duk kuɗin da aka karɓo ya dace da buƙatar shirin inganta zamantakewar ‘yar Nijeriya”. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Tawagar kasar Iran ta maza da mata a wasan wushu a bangaren sanda da taolu ta samu gagarumar nasara inda ta samu lambobin yabo guda guda 10, zinariya 6 Azurfa guda 2 sai kuma tagulla guda 2, a wasan zakarun na washu karo na 17 da aka gudanar a kasar brazil, Gasar Wushu ta duniya ita ce ta farko a gasar da kasar Sin ta mamaye. inda Iran ta samun kambun mataimakiyar zakara ta sha gaban manyan kasashe biyu kamar Malaysia da Hong Kong, ya nuna irin gagarumin sauyi a cikin tsarin wushu na duniya, kuma ya nuna irin kaifin basira da bangarorin biyu suke da shi na maza da mata. Tawagar kasar Iran ta samu lambobin yabo guda 10...
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya jaddada yin kira ga al’ummar Musulmi cewa: Wajibi ne kasashen musulmi su yanke alakarsu da ‘yan sahayoniyya Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa: Dole ne kasashen musulmi su yanke duk wata huldar kasuwanci da siyasa da gwamnatin ‘yan sahayoniyya azzaluma tare da mayar da ita saniyar ware. Jagoran juyin juya halin Musulunci ya jaddada cewa: Dole ne a fuskanci bala’o’in da muguwar gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta haifar a Gaza. Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya yi tsokaci kan mummunan halin da ake ciki a zirin Gaza inda ya ce: Dole ne kasashen da suke gudanar da zanga-zangar a yau musamman kasashen musulmi su yanke duk wata huldar kasuwanci...
Ministan harkokin wajen kasar Iran abbas Aragchi ya yi kira ga kasashen turai 3 EU a takaice su dawo kan hanyar diblomasiyya don warware rikicin shirin Nukliyar kasar Iran wanda ya zo cikin yarjeniyar JCPOA na shekara ta 2015. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Argchi yana fadar haka a yau Lahadi a cikin wani rubutun da yayi a cikin Jaridar Guadian na kasar Burtania. Ministan ya kammala da cewa idan sun ki dawowa kasashen turai ne za’a ware nan gaba, don ba zasu taba cimma manufofinsu a kan Iran tare da sake maida takunkuman MDD kan kasar Iran ba. Tsarin Snpback dai wani tsari ne wanda zai bawa kasashe 6 wanda suke cikin yarjeniyar JCPOA danar...
Bictor Boniface Wani dan wasan da ya tafi zaman aro shi ne Bictor Boniface wanda ya bar Bayer Leberkusen ya koma Werder Bremen a matsayin aro na tsawon kaka guda a ranar da za a rufe cinikin yan wasa, dan wasan na Nijeriya ya saka hannu akan kwantiragin da zai sa ya zauna a Werder har zuwa watan Yuni na shekarar 2026, kungiyoyin biyu ne za su biya albashin Boniface. Tolu Arokodare Wolbes ta sanar da daukar Arokodare daga kungiyar KRC Genk ta kasar Belgium dake buga gasar Belgian Pro League a ranar karshe ta musayar yan wasa, dan wasan mai shekaru 24 ya rattaba hannu kan kwantiragin shekaru hudu da kungiyar ta Firimiya tare da zabin karin shekara,...
Kwamandan Sojojin Iran ya jaddada cewa: Dole ne a ko da yaushe Iran ta kasance a shirye don yin yaki Babban kwamandan sojojin kasar Iran ya jaddada wajibcin kasancewa cikin shiri a ko da yaushe domin yaki, yana mai cewa: A yau sun fahimci yaki da gaba da kuma makircin makiya daidai da yadda suke a baya. Babban kwamandan sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Manjo Janar Amir Hatami, ya ziyarci rundunonin sojoji a yankunan Isfahan, Tabriz, da Hamadan. A yayin da yake yin nazari kan shirye-shiryen wadannan runduna tare da rakiyar kwamandoji, mayaka, da matukan jirgin sama, ya lura da tsayin daka da al’ummar Iran suka yi wajen tunkarar wuce gona da iri da yahudawan sahayoniyya suka kaddamar na tsawon...
A cikin sa’o’i 24 da suka gabata, akalla Falasdinawa 68 ne suka yi shahada a Zirin Gaza, wanda ya kawo adadin wadanda suka rasu a yakin kisan kare dangi na Isra’ila tun watan Oktoban 2023 zuwa sama da 64,368. Akalla Falasdinawa tara ne sukayi shahada a wani kazamin harin da aka kai ta sama a birnin Gaza da Khan Yunus, ciki har da takwas lokacin da aka kai hari kan wani gini a unguwar Sheikh Radwan. Kamfanin dillancin labaran iqna, ya nakalto cewa, a ranar Asabar, wani yaro ya yi shahada a wani harin da Isra’ila ta kai kan wata mota a sansanin al-Mawassi da ke Khan Yunis. Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, bayan harin bam da Isra’ila...
An ce saurayin ya yi wa Ammaye wasa da cewa yana son aurenta domin “cika Sunnah”. Sai dai kuma an ce Ammaye ta yi wata magana da aka dauka a matsayin Batanci. Wannan ne ya fusata matasan yankin. Lamarin aka kai shi fadar Dagacin Kasuwar Garba, inda aka yi mata tambayoyi, kuma a cewar rahoto ta maimaita abin da ta fada tun farko. An ce Dagacin ya mika Ammaye ga jami’an tsaro domin gudanar da bincike, amma taron matasa masu hargitsi suka mamaye jami’an tsaro, suna cewa a kashe ta nan take. Jaridar PUNCH Metro ta gano cewa kafin jami’an tsaro su iso domin kawo dauki, matasan sun riga ya jajjefe Ammaye har ta mutu. Mai magana da yawun ‘yansandan...
Khalil al -Hayya shugaban kungiyar Hamas a yankin gaza dake falasdinu tare da yawa daga cikin mambobin kungiyar Hamas da jagororinta na siyasa sun gana da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi a birnin Doha na kasar Qatar, inda suka tattauna game da yakin kwanaki 12, da hakan ke nuna irin goyon baya da iran take bawa yan gwagwarmayar falasdinu ,wanda ya sanya wasu kasashen turai suka amince da falasdinu a matsayin kasa Amurka da HKI suna shirin ganin sun kwashe mutanen Gaza sai dai Arqchi ya aike da sako mai karfi zuwa ga Amurka da HKI a taron da suka yi da jami’an kungiyar hamas a gaza, na irin shirin da iran take da shi na ci gaba...
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Ghana ta sanar cewa ofishin jakadancinta dake birnin Tehran zai koma aiki a rana 16 ga watan satumnbar da muke ciki bayan rufeshi da aka yi na wucin gadi, Sake bude ofishin jakadancin Ghana a birnin Tehran zai kara bude hanyoyi kyautata dangantakar Ilimi, kasuwanci, da musayar ala’adu da kuma yin aiki tare , adaidai lokacin da kawancen kasashen duniya ke canza sheka, wannan mataki ya nuna aniyar Ghana na karkatar da alakarta ta kasashen duniya. An rufe ofishin jakadancin Ghana ne a ranar 16 ga watan yuni bayan yaki da ya barke tsakanin Iran da Isra’ila domin kare lafiyar ma’aikatanta a wannan lokacin . Wannan matakin da kasar Ghana ta dauka na sake bude ofishin...
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Babu aminci tsakanin kasar Iran da Hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana cewa: An rasa amana tsakanin Iran da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, yana mai jaddada cewa; “Iran ba ta maraba da mayar da takunkumin kan kasarta, amma ta koyi yadda za ta 0kare mutuncin al’ummarta da fuskantar wannan yaki na rashin adalci.” Dangane da yiwuwar sake wani yaki kuwa, ya ce, “Iran a shirye take.” Hakan ya zo ne a wata hira da jaridar Guardian ta yi da kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Ismail Baqa’i. Game da sharuɗɗa uku da Turai ta sanar don yin shawarwari, Baqa’i...
Qalibaf: Ya Bukaci Gwamnatocin Kasashen Musulmi Su Fito Su Yi Allah Wadai Da Ayyukan Isra’ila A Gaza
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ya jaddada cewa: Dole ne gwamnatocin Musulunci su dauki matakai na zahiri don dakile ayyukan kisan kare dangi ‘yan sahayoniyya a Gaza Muhammad Baqir Qalibaf, Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ya jaddada bukatar da ke akwai ga al’ummar Musulmi da su yi Allah wadai da kisan kiyashin da ake yi a Gaza ba tare da bata lokaci ba. Ya kuma yi kira ga gwamnatocin kasashen musulmi da su yi koyi da al’ummarsu da suka dauki matakai na zahiri don nuna rashin amincewa da duk wata hanyar aiwatar da kashe-kashen yahudawan sahayoniyya. A farkon taron majalisar a ranar Laraba, Qalibaf ya taya al’ummar musulmi murnar shigowar makon hadin kai, inda ya ce: A wadannan...
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya yi tir da kissan da sojojin HKI suka yiwa firay ministan kasar Yemen Ahmad Al-Rahawi da wasu jami’an gwamnatinsa. Ya kuma kara da cewa irin wadan nan hare-haren suna zagon kasa ga zaman lafiya a duniya. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a wani sakon da ya aika ga gwamnatin kasar Yemen da kuma iyalan wadanda suka rasa rayukansu a wannan harin na marasa imini, wanda sojojin HKI suka yi. Ministan ya yaba da yadda kasar Yemen ta tsaya kan kafafuwanta wajen taimakawa mutanen Gaza wadanda ake zalunta. Aragchi ya ci gaba da aibata MDD kan rashin daukar mataki kan HKI a yayinda an kusan...
Sojojin kasar Yemen sun bada labarin kai hari kan wani jirgin daukar man fetur na HKI a arewacin tekun maliya a safiyar yau litinin. Mai magana da yawun sojojin kasar ta Yemen Burgediya Yahyah Saree ne ya bada wannan sanarwan a wani jawabin da ya gabatar a faifai bidiya a safiyar yau Litinin, tare da amfani da makamai mai linzami samfurin Bailistik. Ya kuma tabbatar da cewa harin ya kai ga hadafinsa ya kuma wargaza jirgin ruwan na HKI dauke da manfetur zuwa haramtacciyar kasar. Gwamnatin kasar Yemen dai tana yaki da HKI tun bayan fara yakin tufanul Aksa a cikin watan Octoban shekara da 2023. Kuma HKI ta sha kaimata hare-hare, amma a wannan karon ta kai hare-hare kan...
Babban sakataren Majalisar kolin tsaron kasar Iran ya jaddada cewa: Iran na adawa da duk wani sauyi na siyasa a yankin Babban Sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Ali Larijani ya bayyana cewa: Iran na adawa da duk wani sauyi na siyasa a yankin da kuma cutar da alaka tsakanin Iran da Armeniya. Ali Larijani, babban sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran, ya gana tare da tattaunawa da Armen Grigoryan, sakataren kwamitin koli na tsaron kasar Armeniya a safiyar yau. A cikin wannan taro, babban sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran ya bayyana gamsuwar da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take da shi kan matakin tattalin arziki, siyasa, tsaro da kasar Armeniya, tare da jaddada hadin gwiwa da...
Kungiyar Hamas ta yi maraba da Allah wadai da kasashen Turai 6 suka yi da matakin wuce gona da iri da gwamnatin mamayar Isra’ila ta dauka kan Gaza Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta yi marhabin da matakin da wasu kasashen Turai shida suka dauka na yin Allah wadai da wuce gona da iri da yahudawan sahayoniyya suka yi a kan birnin Gaza, tare da la’akari da shi a matsayin wani muhimmin mataki da ke kara habaka matsayar kasashen duniya na neman kawo karshen wuce gona da iri kan al’ummar Falastinu. Kasashen da ake magana a kai su ne: Iceland, Ireland, Luxembourg, Norway, Slovenia, da Spain. Ministocin harkokin wajensu sun bayyana rashin amincewarsu da hare-haren wuce gona da iri kan...
Jakadan kasar Iran a majalisar dinkin duniya Amir Saeed Iravani yayi watsi da shirin kasashen turai 3 na sake farfado da takunkuman MDD kan Iran.. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Iravani yana fadar haka a jiya Jumma’a ya kuma kara da cewa Iran tana kan bakanta na tattauna da wadan nan kasashen Turai, wato Burtaniya, farana da kuma Jamus. Amma ba zata shiga tattaunawa da su tare da takura mata ba. Iravani ya bayyana cewa kasashen turai ne suka fara sabawa yarjeniyar JCPOA, inda suka ki aiwatar da alkawulan da suka dauka a cikinta. A halin yanzun dai kasashen turan sun bawa Jumhuriyar Musulunci ta Iran dama har zuwa wani lokaci don cika wasu sharudda kafin...
A cewarsa, jami’an NDLEA sun nuna kwarewa da kwarewa wajen gano yadda aka boye kwayoyin. “Wannan lamari ya nuna jajircewar hukumar wajen katse hanyar rarraba miyagun kwayoyi da tabbatar da tsaron al’umma.” Ya rawaito kwamandan NDLEA na Jihar Kano, Malam Abubakar Idris-Ahmad, yana yaba wa jami’an hukumar bisa jajircewa da himma wajen gudanar da aikin. Idris-Ahmad ya kuma yaba wa shugaban hukumar NDLEA na kasa, Tsohon Birgediya-Janar mai ritaya, Mohamed Buba-Marwa, bisa goyon baya da jagoranci da yake bayarwa. “NDLEA a Jihar Kano ta dage wajen aiwatar da manufarta ta kawar da miyagun kwayoyi a jihar, tare da gode wa hadin kai da goyon bayan jama’a wajen cimma wannan buri,” in ji shi. A cewarsa, jami’an NDLEA sun nuna kwarewa...
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta mayar da martani ga Tawagar Turai na kokarin dawo da takunkumi kan kasarta Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta fitar da sanarwa a matsayin martani ga sanarwar da Tawagar Tura ta yi wa kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya da baya kan ka’ida dangane da kuduri mai lamba 2231. Ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta yi watsi da kakkausan harshe tare da yin Allah wadai da shelanta batu da baya kan doka da tawagar Turai Faransa da Jamus da Birtaniya suka yi ga kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya dangane da kuduri mai lamba 2231 na shekara ta 2015. Wannan matakin bai dace ba, wanda ya ci karo da Tsarin Raba Rikici (DRM) na Haɗin gwiwar...
Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya yi gargadi kan mummunan sakamakon Shirin Isra’ila na fadada ayyukanta a birnin Gaza Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya António Guterres ya yi gargadi kan mummunan sakamakon matakin da haramtacciyar kasar Isra’ila zata dauka na fadada ayyukan soji a birnin Gaza, yana mai yin Allah wadai da manufofin fadada gine-ginen matsugunan yahudawa ‘yan mamaya a yankunan gabar yammacin kogin Jordan. A jawabin da ya yi wa manema labarai a jiya Alhamis, gabanin taron kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya a hedkwatar Majalisar dake birnin New York, Guterres ya bayyana cewa, matakin farko da gwamnatin mamayar Isra’ila ta dauka na kwace birnin Gaza ya sanar da wani sabon yanayi mai hadari. Ya kara da cewa “fadada...
Baki Kusan 50 Daga Kasashe 30 Na Turai Za Su Halarci Bikin Tunawa Da Nasarar Yakin Turjiyar Sinawa Kan Zaluncin Japanawa
A yau Alhamis, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya sanar da cewa, ya zuwa yanzu akwai shugabanni da tsoffin ‘yan siyasa da manyan jami’ai, da jakadun dake kasar Sin da sauransu kusan 50 daga kasashe 30 na Turai da suka tabbatar da za su halarci bikin da za a yi albarkacin cika shekaru 80 da samun nasara a yaki da kutsen Japan da yaki da mulkin danniya a duniya. Wannan ya nuna niyyarsu ta hada hannu wajen tunawa da tarihi da kiyaye zaman lafiya da adalci. Guo ya jaddada cewa, kasar Sin ta shirya bikin ne da nufin tunawa da tarihi da magabata, da kiyaye zaman lafiya da ma tabbatar da makoma mai kyau ga bil...
Wakilin Kasar Rasha A Vienna Ya Sanar Da Sake Dawo Da Ayyukan Hukumar IAEA A Cibiyar Busharhr Na Iran
Wakilin dindindin na kasar Rasha a kungiyoyin kasa da kasa a Vienna ya sanar da cewa: An sake dawo da ayyukan IAEA a cibiyar Bushehr Wakilin dindindin na kasar Rasha a kungiyoyin kasa da kasa a Vienna, Mikhail Ulyanov, ya sanar da dawo da ayyukan hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa a cibiyar makamashin nukiliya ta Bushehr dake kudancin kasar Iran. A cikin wani sako da ya aike a shafinsa na X, Ulyanov ya rubuta cewa: Iran ta sake tabbatar da cewa, ko da bayan hare-haren da sojoji suka kai wa cibiyoyin nukiliyar kasarta na zaman lafiya da ke gudana karkashin hukumar ta IAEA ba bisa ka’ida ba, abin kunya ne, a matsayinta ta mamba ta hukumar...
Lardin Hubei shi ma ya bi sawu, inda ya bullo da nasa shirye-shiryen na raba takardun tallafin tare da mai da hankali musamman a kan bangaren da ya shafi cin abinci. Babban makasudin hakan shi ne a karfafa mutane su rika fita zuwa gidajen cin abinci. Wannan ya kara farfado da salon cin abinci tare a tsakanin Sinawa da kuma kwarya-kwaryan harkokin da ake yi a gefen wasu tituna bisa tsari. Baya ga bunkasa tattalin arziki, wannan dabara tana samar da yanayi mai dadi da faranta ran jama’a. Shi ma birnin Shanghai ba a bar shi a baya ba a kan wannan sabga, inda shi kuma ya mayar da hankali a kan nishadantarwa ta fuskar al’adu. Birnin ya...
A wata ziyarar da wata tawagar yan jarida daga Iran suka kai birnin Mosco, kasashen biyu sun rattaba hannu kan yarjeniyoyin habaka dangantaka na sardarwa tsakanin kasashen biyu. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa hukumar tashoshin talabijin da Radiyo na kasar Iran da kuma na bangaren Rasha sun karan zurfafa dangantaka tsakaninsu a fagen yada labarai a yankin da kuma duniya gaba daya. Labarin ya kara da cewa wannan dangantakar zai sa fuskance labaran karya wadanda kafafen yada labarai na yamma suke yadawa. Har’ila yau yarjeniyoyin aiki tare tsakanin hukumomin watsa labaran kasashen biyu zai samar da labarai iri guda da kuma fadada hanyoyin samun labaran gaskiya a tsakaninsu. Daga cikin yarjeniyoyin dai akwai na tsakanin...
A wata ziyarar da wata tawagar yan jarida daga Iran suka kai birnin Mosco, kasashen biyu sun rattaba hannu kan yarjeniyoyin habaka dangantaka na sardarwa tsakanin kasashen biyu. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa hukumar tashoshin talabijin da Radiyo na kasar Iran da kuma na bangaren Rasha sun karan zurfafa dangantaka tsakaninsu a fagen yada labarai a yankin da kuma duniya gaba daya. Labarin ya kara da cewa wannan dangantakar zai sa fuskance labaran karya wadanda kafafen yada labarai na yamma suke yadawa. Har’ila yau yarjeniyoyin aiki tare tsakanin hukumomin watsa labaran kasashen biyu zai samar da labarai iri guda da kuma fadada hanyoyin samun labaran gaskiya a tsakaninsu. Daga cikin yarjeniyoyin dai akwai na tsakanin...
Ministan harkokin wajen Iran ya ce: A shirye Iran take ta gudanar da shawarwari da Amurka, amma kan sharudda Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya ce; kasarsa a shirye take ta dawo da tattaunawar makamashin nukiliya da Amurka, amma tare da ba da tabbacin babu batun kai hari kan Iran. Ya bayyana cewa ba za a cimma abin da Amurka ke so ba ta hanyar kai harin soji kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, kuma a duk wata tattaunawa dole ne Amurka ta kare sharuddan da Iran ta gindaya mata domin samun ci gaba mai daure wa. Araqchi wanda ya gana da Asharq Al-Awsat bayan halartar wani zama na musamman na ministocin harkokin wajen kungiyar hadin kan kasashen musulmi don...
Hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ba za ta duba wuraren da aka lalata na cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran ba a hare-haren Amurka Kamfanin dillancin labaran Associated Press ya bayar da rahoton cewa, a halin yanzu hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ba za ta binciki cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran da hare-haren Isra’ila da Amurka suka lalata ba. Har yanzu dai bangarorin ba su cimma matsaya ta karshe ba, amma jami’an diflomasiyya na jiran kammalawar ta. A karkashin yarjejeniyar, hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa IAEA za ta takaita ne ga cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran wadanda ba su da alaka da cin zarafin Isra’ila da Amurka. A ranar Talata, babban darektan hukumar...
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Tarihi ba zai yafe jinkirin yin Allah wadai da bala’in Gaza ba Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya bayyana cewa: “Al’umma ta tuna cewa bala’in Gaza bai shafi musulmi kadai ba, wannan lamari ne na gwaji na lamiri na dukkanin bil’adama, don haka suna kira ga dukkanin al’umma ba tare da la’akari da addini ko yanayin kasa ba, da su tsaya a bangaren bil’adama, adalci da mutunci, wato a bangaren dama na tarihi.” Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi ya bayyana haka ne a jawabin da ya gabatar a wajen taron baje kolin na majalisar ministocin harkokin wajen kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC, inda ya yi jawabi ga...
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Tun Bayan Barkewar Yaki Da Iran Babu Wata Hulda Tsakaninta Da Amurka
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Tun bayan barkewar yakin da Iran, babu wata hulda da ta hada ta da Amurka Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Ismail Baqa’i ya jaddada cewa: “Turawa za su iya taka muhimmiyar rawa a shawarwari,” yana mai bayanin cewa: “Tun bayan barkewar yaki da Iran, kasar Iran ta daina yin mu’amala da Amurkawa, amma tana ci gaba da hulda da Turawa ko da a lokacin da ake tsaka da yakin.” A wata hira da jaridar Süddeutsche Zeitung ta Jamus dangane da shawarar da Turai ta gabatar na tsawaita wa’adin aiki da hanyar da za a bi wajen ganin an dawo da takunkumin majalisar dinkin duniya kan Iran, kakakin ma’aikatar harkokin wajen...
Kafofin yada labarai na yahudawan sahayoniyya sun yarda da gazawar dakile Yemen daga ci gaba da ayyukan soji kan Isra’ila Kafofin yada labaran Isra’ila, wadanda tashar 12 da tashar ta 13 ke wakilta, sun amince da cewa: Hare-haren da makiya ke kaiwa kasar Yemen, ya gaza hana sojojin Yemen harba makamai masu linzami zuwa yankunan Isra’ila da aka mamaye. Waɗannan tashoshi na yahudawan sahayoniyya sun yi imani cewa; Da’awar iya dakile hare-haren sojojin Yemen kan yankunan Isra’ila, rudu ne kawai na jami’an haramtacciyar kasar Isra’ila ganin tsawon lokacin da za a iya dauka domin hana kai waɗannan ayyuka saboda “haɗarinsu.” Tashar talabijin ta yahudawa ta 13 ta yarda cewa harin na baya-bayan nan da aka kai kan kasar Yemen ba...
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce: Gwamnatin Mamayar Isra’ila Barazana ce Ga Tsaron Yanki
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Gwamnatin ‘yan sahayoniyya barazana ce ga wanzuwar tsaron yankin Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Yahudawan sahayoniyya suna wakiltar wata barazana ga wanzuwa tsaro da zaman lafiyar yankin da kuma kasashensu. Idan ba a dakile wannan barazanar ba, to babu shakka yankin zai fuskanci yake-yake marasa iyaka. A yayin taron manema labarai na mako-mako a ranar Litinin, Baqa’i ya yi ishara da zagayowar ranar 28 ga watan Mordad (19 ga Agusta, shekara ta 1953, yana mai cewa: Ba za a iya mantawa da wannan lamari mai zafi ba, juyin mulkin da ya hambarar da zababbiyar gwamnatin al’ummar Iran tare da hadin gwiwar Amurka da Birtaniya. Dangane da ci...
Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci na Iran sun bayyana cewa: A shirye suke su tunkari duk wata barazana da makarkashiyar ‘yan sahayoniyya da Amurka Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun fitar da sanarwa a ranar 16 ga watan Agusta na tunawa da dawowar fursunonin da aka ‘yantar zuwa mahaifar ta daular Musulunci. Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Fursunonin da aka ‘yantar madaukaka, sune ainihin bayyanar gwagwarmaya da tsayin daka na ruhi da kuma bege na dabaru. A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar 16 ga watan Agusta na bikin tunawa da dawowar ‘yantattun fursunoni (fursunonin yakin shekara ta 1980-1988 a yakin da aka kakaba kan Iran), da tunawa da yakin kwanaki 12 da...
Jaridar Wall Street Journal Ta Ce: Har Yanzu Isra’ila Na Ci Gaba Da Neman Wajen Da Zata Tura Falasdinawa Gudun Hijira
Jaridar Wall Street Journal ta bayyana cewa: Har yanzu gwamnatin mamayar Isra’ila tana ci gaba da neman kasashen da za su karbi ‘yan gudun hijiran Falasdinawan Gaza! Jaridar Wall Street Journal ta buga wani rahoto da ke cewa: Gwamnatin mamayar Isra’ila tana ci gaba da gudanar da tattaunawar da ta bayyana na zaman natsuwa domin tura ‘yan gudun haijiran Falasdinawa daga Gaza. Kasashen da suka hada da Libiya, Siriya da Sudan ta Kudu. Rahoton wanda Samar Sa’ed, Robbie Gramer, da Omar Abdel Baqi suka shirya, ya bayyana cewa: Gwamnatin mamayar Isra’ila da Amurka suke yunkurin tura dubban daruruwan Falasdinawa daga zirin Gaza zuwa gare su, matakin da suka gabatar cewa akwai hanyoyin jin kai, amma gwamnatocin yammacin Turai da kasashen...
Gwamnatin DR Kongo Ta Nuna Rashin Amincewarta Da Zabin Kenya Kan Wajen Da Zata Bude Karamin Ofishin Jakadancinta A Kasarta
Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo ta ki amincewa da nadin sabon karamin ofishin jakadancin Kenya a birnin Goma Gwamnatin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango ta sanar da kin amincewa da nadin sabon karamin ofishin jakadancin Kenya a birnin Goma da ke gabashin kasar, duba da matakin da ya saba wa ka’idojin diflomasiyya, duba da yadda Kongo ke ganin ci gaba da kasancewa a birnin na Goma ya saba ka’ida. A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Asabar din da ta gabata, mahukuntan kasar Kongo sun bayyana mamakinsu kan sanarwar da fadar shugaban kasar Kenya ta bayar na nadin Judi Kiara Nkumiri a matsayin karamin jakadanta a birnin Goma ba tare da amincewar ma’aikatar harkokin wajen Kongo ba. Sun dauki wannan a matsayin...
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa; Suna godiya ga Iraki saboda karimcin da ta yi wa masu ziyarar Arba’een na Imam Husain {a.s} Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya yaba da kokarin gwamnati da al’ummar Iraki wajen karbar bakwancin masu ziyarar juyayin Arba’een na Imam Husaini {a.s}. A yayin da yake halartar shirin na musamman na “muryar ku a ko’ina” da ake watsawa a gidan rediyon Saba, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya tattauna batutuwan da suka shafi gagarumin tattakin Arbaeen da tasirinsa ga duniyar musulmi. A farkon hirar, minista Araqchi ya mika sakon gaisuwarsa ga masu ziyarar Arba’een a birnin Karbala, inda ya bayyana farin cikinsa da halartar wannan gagarumin taron juyayi. Yana...
Firaministan Sin Ya Bukaci A Zage Damtse Wajen Bude Sabon Babin Gina Wayewar Kai Ta Fuskar Kare Muhallin Halittu A Sabon Zamani
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Babban Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Iran Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Martani Mai Tsanani Kan Duk Wanda Ya Kai Mata Hari
Babban sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran ya jaddada cewa: Iran za ta mayar da martani da karfi kan duk wani wuce gona da iri kanta Babban sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Ali Larijani ya bayyana cewa: Gwagwarmaya ita ce babban jari kuma wata dabara mai kima ga yankin, yana mai jaddada cewa: Iran za ta mayar da martani mai karfi kan duk wani hari da aka kai mata, kuma babu wata tattaunawa da za ta yi tasiri a karkashin tunanin Amurka na “zaman lafiya da nuna karfi.” Ali Larijani ya jaddada a shirye Iran take a koda yaushe ta mayar da martani mai karfi kan duk wani hari da gwamnatin mamayar Isra’ila za ta kai kan...
Kungiyar Kare Hakkin Bil’Adama Ta Human Rights Watch Ta Ce; Kai Hari Kan Gidan Yarin Evin Na Iran Laifin Yaki Ne
Kungiyar kare hakkin bil-Adama ta Human Rights Watch ta bayyana cewa: Harin da gwamnatin mamayar Isra’ila ta kai kan gidan yarin Evin na Iran laifi ne na yaki Kungiyar kare hakkin bil-Adama ta Human Rights Watch ta ce: Harin da gwamnatin mamayar Isra’ila ta kai kan gidan yarin Evin da ke birnin Tehran fadar mulkin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a ranar 23 ga watan Yuni yana matsayin laifin yaki. A cikin wani rahoto da ta buga jiya alhamis, kungiyar ta yi bayanin cewa hare-haren da gwamnatin mamayar Isra’ila ta kai kan gine-gine da dama a cikin rukunin, sun kuma kashe mutane akalla 80, a cewar sanarwar da Iran din ta fitar, da suka hada da fursunoni da ‘yan uwansu, da...
Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Wani Mummunan Hari Kan Gaza Tare Da Rusa Gidajen Mutane A Khan Yunis
Sojojin mamayar Isra’ila sun kai wani mummunan farmakin kan birnin Gaza tare da janyo ruftawar gidaje a Khan Yunis Falasdinawa da dama sun yi shahada tare da jikkata a yau Juma’a a wani kazamin harin da sojojin mamayar Isra’ila suka kai kan Gaza a rana ta hudu a jere, yayin da gwamnatin mamayar Isra’ila take ci gaba da mamaye birnin. A halin da ake ciki kuma an ci gaba da rusa gidaje a Khan Yunis da ke kudancin zirin Gaza. Majiyar Asibitin Al-Shifa ta sanar da cewa: Falasdinawa biyu sun yi shahada yayin da wasu suka jikkata a harin da sojojin mamayar Isra’ila suka kai unguwar Al-Rimal da ke yammacin birnin Gaza. Wakilin gidan talabijin na Aljazeera ya bayar da...
A yayin da yake martani kan suka da ake yi masa na rashin gabatar da kudirori a gaban majalisar, ya bayyana cewa, “tun da na je Majalisar, ba bu wani dan mazabata da ya rubuto min wani kudiri ko bukata da zan gabatar a gaban Majalisa, duk zarge-zargen karya ne suke yi min, kuma idan har akwai, wani ya fito ya kalubalance ni,” inji shi. “Hatta gabatar da kudirori da korafe-korafe a majalisar, wasu sai sun amso cin hancin kimanin naira miliyan 1, ko naira miliyan 2, ko naira miliyan 3, domin karantawa a zauren majalisar, bayan an karanta kudirin, kuma dole sai sun bibiyi ‘yan majalisa sama da 360 domin su goyi bayan a amince da kudirin.” ...
A yayin da yake martani kan suka da ake yi masa na rashin gabatar da kudirori a gaban majalisar, ya bayyana cewa, “tun da na je Majalisar, ba bu wani dan mazabata da ya rubuto min wani kudiri ko bukata da zan gabatar a gaban Majalisa, duk zarge-zargen karya ne suke yi min, kuma idan har akwai, wani ya fito ya kalubalance ni,” inji shi. “Hatta gabatar da kudirori da korafe-korafe a majalisar, wasu sai sun amso cin hancin kimanin naira miliyan 1, ko naira miliyan 2, ko naira miliyan 3, domin karantawa a zauren majalisar, bayan an karanta kudirin, kuma dole sai sun bibiyi ‘yan majalisa sama da 360 domin su goyi bayan a amince da kudirin.” ...
“Na zo Banga domin jajanta muku bisa wannan mummunan hari. Lokacin da abin ya faru bana nan, sai na umarci mataimakina ya jagoranci tawaga ta musamman domin yi muku ta’aziyya. “Na dawo Gusau jiya, kuma abu na farko da na fifita yau shi ne zuwa nan da kaina. Gwamnati za ta ƙara ƙoƙari wajen yaƙar ‘yan bindiga,” in ji shi. Gwamnan ya yi addu’ar Allah Ya ɗauki matakaki a kan waɗanda suka aikata wannan kisan gilla, sannan ya roƙi jama’a da su ci gaba da yin addu’a domin kawo ƙarshen duk wata ɓarna a Zamfara. Sarkin Kauran Namoda, Dokta Sunusi Ahmad Rashad, wanda ya raka gwamnan, ya yaba masa bisa saurin ɗaukar mataki bayan faruwar lamarin. “Wannan ziyara tana da...
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Tsokaci Kan Furucin Netanyahu Game Da Kafa “Babbar Kasar Isra’ila’
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya yi tsokaci kan furucin Netanyahu game da kafa ‘Babban Kasar Isra’ila’ Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya bayyana a safiyar yau alhamis cewa: Kafafen yada labaran yammacin duniya a al’ada na zargin duk wanda ya ambaci ra’ayin ‘yan sahayoniyya na kafa “Babban kasar Isra’ila” da kiyayya ga wata al’umma. Bayanin Araqchi, wanda aka yi da sanyin safiyar Alhamis a shafinsa na yanar gizo na dandalin sada zumunta na X, yana mai mayar da martani ga kalaman fira ministan gwamnatin mamayar Isra’ila Benjamin Netanyahu game da batun kafa “Babban kasar Isra’ila.” A cikin shafinsa na yanar gizo, Araqchi ya yi tambaya cewa: “Shin suna daukan furucin Netanyahu kansa a matsayin mai adawa da wata...
Hukuma mai kula da sauka da tashin jiragen sama a birnin Paris ya dakatar da wani ma’aikacinsa, wanda yake aikin a bangaren kula da sauka da tashin jiragen sama, saboda ya shelantawa wani jirin HKI wanda ke kokarin sauka a tashar jiragen kan cewa “yanci-yenci Falasdinu”. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya nakalto majiyar kafafen yana labarai na kasar Faransa na cewa, ma’aikacin ya fadi wadannan kalmomi ne ga matukin HKI wanda ya tashi a tashar ‘Charles de Gaulle’ da ke birnin Paris. Labarin ya kara da cewa matukin jirgin ne ya bada wannan rahoton ga hukumomin kasar Faransa don daukar matakin da ya dace. Ba’a bayyana sunan ma’aikacin ba, amma a jiya talata ce hakan ya auku,...
Miistan harkokin wajen kasar Masar ya sake ganawa da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi da kuma shugaban hukumar makamashin nukliya ta duniya Rafael Grossi ta wayar tarho. Kamfanin dillancin labarana Tasnim na kasar Iran ya nakalto ma’aikatar harkokin wajen kasar Masar na cewa jami’am gwamnatin kasashen biyu da kuma Grossi sun tattauna al-amura da suka shafi sake komawa kan taburin tattaunawa da kasar Iran kan shirinta na makamashin nukliya ne bayan yakin kwanaki 12 wadanda HKI da Amurka suka kaiwa kasar Iran. Badar Abdullatf ministan harkokin wajen kasar Masar yana kokarin sake maida dangantakar hukumar AIEA da kuma Iran bayan tayi tsami a watan yunin da ya gabata, inda Iran tana zargin Grossi da hada kai da Amurka...
Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Rano, Alhaji Muhammad Naziru Ya’u, na tsawon watanni uku sakamakon zarge-zargen aikata ba daidai ba. An yanke wannan hukunci ne a zauren majalisa ƙarƙashin jagorancin Shugaban Majalisar, Alhaji Jibril Isma’il Falgore, bayan kwamitin majalisar kan ƙorafe-ƙorafe ya gabatar da rahoton bincikensa. Yayin gabatar da rahoton, Shugaban Kwamitin wanda shi ne shugaban masu rinjaye, Alhaji Lawan Hussaini Dala, ya ce binciken ya samo asali ne daga ƙorafin da kansiloli tara daga cikin goma na Rano suka sanya wa hannu. A cewarsa, ƙorafin ya zargi shugaban da yin sakacin kuɗi, sayar da shaguna, da karkatar da takin zamani da aka ware wa ƙaramar hukumar, tare da wasu zarge-zarge daban. Lawan ya bayyana...
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Lokaci ya yi da za a amince da takunkumin da bai dace ba a matsayin laifi ga bil’adama Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya ce lokaci ya yi da za a amince da takunkumin bai daya da Amurka da kawayenta suka kakaba wa Iran a matsayin wani laifi na cin zarafin bil adama. A cikin shafinsa na dandalin X, Araqchi ya bayyana cewa: “Gwamnatocin yammacin duniya a koyaushe suna da’awar cewa takunkumin zaman lafiya ne maimakon yakin zubar da jinni, amma gaskiyar tana bayyana wani labari na daban.” Ya yi nuni da wani bincike na baya-bayan nan da aka buga a cikin jaridar The Lancet, wanda ya nuna cewa takunkumin bai-daya-musamman wanda...
An yi kira ga kwararrun kafafen yada labarai da su tabbatar da madogararsu domin tabbatar da samar da kyakykyawan rahoton abubuwan da ke faruwa a cikin al’umma. Babban Limamin Masallacin Al-Waheed Central, Imam Mustapha Luqman ne ya yi wannan kiran a lokacin da yake jawabi a wajen taron hadin gwiwa da kungiyar ‘yan jarida ta NUJ ta shirya domin fara taron makon manema labarai na shekara ta 2025, da kuma bikin cika shekara 45 daka guda a Ilorin jihar Kwara Ya shawarce su da su bi ka’ida wajen gudanar da ayyukansu na yada labarai. Imam Lukman ya bukaci masu aikin yada labarai da su kasance masu adalci da kyautatawa a tsakaninsu . A nasa jawabin, Fasto...
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: A Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Lokaci ya yi da za a amince da takunkumin da bai dace ba a matsayin laifi ga bil’adama Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya ce lokaci ya yi da za a amince da takunkumin bai daya da Amurka da kawayenta suka kakaba wa Iran a matsayin wani laifi na cin zarafin bil adama. A cikin shafinsa na dandalin X, Araqchi ya bayyana cewa: “Gwamnatocin yammacin duniya a koyaushe suna da’awar cewa takunkumin zaman lafiya ne maimakon yakin zubar da jinni, amma gaskiyar tana bayyana wani labari na daban.” Ya yi nuni da wani bincike na baya-bayan nan da aka buga a cikin jaridar The Lancet, wanda ya nuna cewa takunkumin bai-daya-musamman wanda...
Kungiyar Manyan Ma’aikatan Jami’o’in Najeriya (SSANU), Jami’ar Jihar Taraba Jalingo, ta bayar da wa’adin makonni biyu ga gwamna Agbu Kefas da shugabannin jami’ar da su gana da ita ko kuma ta shiga yajin aikin. A cikin sanarwar da aka fitar a karshen taron majalisar da aka gudanar a ranar 7 ga wata. Agusta 2025, kuma shugaban kwamitin, Comr. Bitrus Joseph Ajibauka, da sakatare, Mamki Joshua Atein, kungiyar ta bayyana rashin jin dadin ta kan yadda gwamna Kefas ya kasa mutunta yarjejeniyar da kungiyar ta cimma da Gwmanati a wata ganawa da shugabannin kungiyar tare da samar da samfuri da tsarin biyan basussukan da ake bin su a makon farko na watan Fabrairu, 2025, sun bayyana matakin da gwamnan ya...
Majalisar Dokokin Jihar Zamfara karkashin jagorancin Bashar Aliyu Gummi, ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta hada kai da ayyukan tsaro a Jihar domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma, kamar yadda babi na biyu na kundin tsarin mulki ya tanada. A zaman taron na ranar Talata, mambobin sun yi zargin cewa, ‘yan bindiga sun mamaye al’ummomi da dama a fadin jihar Zamfara, kuma sun zargi Gwamnan da mayar da hankali kan burin siyasa da kuma zargin abokan hamayya. Sun kuma yi zargin cewa, Gwamnan bai kai ziyara ko aika tallafi ga al’ummomin da hare-hare ya shafa ba, inda suka ce ziyarar da ya shirya kai wa al’ummar Banga da ke karamar hukumar Kaura Namoda ta kasance da...
Wani babba`ani babba`sojojin kasar Iran ya gargadi HKI da kuma Amurka kan cewa duk wasu hare-hare kan kasar zai kara fushin sojojin kasar. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto babban kwamandan sojojin sama na JMI Major General Abdolrahim Mousavi yana fadar haka a lokacin ganawarsa da babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Afrika ta kudu General Rudzani Maphwanya a yau talata a nan Tehran. Janar Mousavi ya kara da cewa dakarun kare juyin juta halin musulunci a nan Iaran wato IRGC sune sojojin da suka fi kawo fada da yan ta’adda a duniya, sannan rundunar a shirye take ta yi aiki da sojojin Afrika Ta Kudu don samun irin kwarewan da rundunar take da shi a wannan bangaren...
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa a halin yanzu ma’aikatarsa ce take kula da dukkan al-amuran da suka shafi shirin makamashin Nukliya na kasar, tun bayan da majalisar dokokin kasar ta bukaci a jingine aiki da hukumar makamashin Nuikliya ta Duniya IAEA bayan yakin kwanaki 12 da HKI da Amurka suka kaiwa kasar. Aragchi ya bayyana cewa mai yuwa nan gaba, majalisar koli na tsaron kasar ta kula da lamarin shirin makamashin nukliya ta kasar. Amma a halin yanzu tana hannun ma’aikatar harkokin wajen kasar ne. A jiya talata ce mataimakin babban sakataren hukumar makamashin nukliya ta duniya ya ziyarci Tehran, ya kuma tattauna dangane da yadda mu’amalar kasar zata kasance da hukumar. Labarin ya bayyana...
Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki
Mai magana da yawun ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ya bayyana a yau Talata 12 ga wata cewa, bisa dokoki ko ka’idojin da suka shafi saka wasu sassa cikin wadanda aka sanyawa takunkumin sayar musu da kayayyaki, ma’aikatar ta fitar da sanarwa mai lamba 21 da ta 22 a ranar 4 da kuma ranar 9 ga watan Afrilun bana, inda ta saka wasu sassa 28 na Amurka cikin wadanda ta sanyawa takunkumin sayar musu da kayayyaki, wato hana sayar musu kayayyakin amfanin jama’a da ake iya amfani da su a bangaren soja. Har wa yau, domin tabbatar da matsayar da aka cimma a wajen shawarwarin manyan jami’an Sin da Amurka a bangaren tattalin arziki da cinikayya, an yanke shawarar cewa,...
Ministan Harkokin Wajen Iraki Ya Bukaci Zaman Tattaunawa Tsakanin Kungiyar Larabawan Yankin Tekun Gulf Da Iraki Da Kuma Iran
Ministan harkokin wajen kasar Iraki ya ba da shawarar gudanar da taron kasashen Larabawan yankin tekun Pasha da Iraki da kuma Iran Ministan harkokin wajen kasar Iraki Fuad Hussein ya gabatar da shawarar gudanar da taron hadin gwiwa tsakanin kasashen Iraki, Iran, da kuma kasashen larabawan yankin Gulf, a tsarin na 6+2, a gefen taron majalisar dinkin duniya. A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar Iraki ta fitar ta bayyana cewa: Mataimakin fira ministan kasar ta Iraki, kuma ministan harkokin wajen kasar Fuad Hussein ya gana da Ali Larijani, sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran. Sanarwar ta bayyana cewa, a yayin ganawar, an tattauna dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, da aikin layin dogo da zai hada Shalamcheh...
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Sojojin mamayar Isra’ila sun harba wata mugunyar ‘karfin wuta’ da jiragen saman yaki kan yankin kudancin Gaza Bayan tsakar dare ne jiragen yakin sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila suka kaddamar da luguden wuta a kudancin birnin Gaza. Cibiyar yada labaran Falasdinu ta nakalto majiyoyin da ta bayyana a matsayin na cikin gida na cewa: Jiragen saman sojin mamayar Isra’ila sun kaddamar da hare-haren wuce gona da iri, inda suka harba makamai masu linzami sama da 20 cikin ‘yan mintuna a kudancin mahadar Al-Musalaba da Dawla da kuma kusa da masallacin Ali, inda suka nufi kudu. Wakilin cibiyar ya ruwaito cewa, galibin hare-haren sun fi karkata ne a kan titin 8 da ke kudancin Gaza. Wadannan hare-haren dai na zuwa ne a...