Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Gwamnatin ‘yan sahayoniyya barazana ce ga wanzuwar tsaron yankin

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Yahudawan sahayoniyya suna wakiltar wata barazana ga wanzuwa tsaro da zaman lafiyar yankin da kuma kasashensu. Idan ba a dakile wannan barazanar ba, to babu shakka yankin zai fuskanci yake-yake marasa iyaka.

A yayin taron manema labarai na mako-mako a ranar Litinin, Baqa’i ya yi ishara da zagayowar ranar 28 ga watan Mordad (19 ga Agusta, shekara ta 1953, yana mai cewa: Ba za a iya mantawa da wannan lamari mai zafi ba, juyin mulkin da ya hambarar da zababbiyar gwamnatin al’ummar Iran tare da hadin gwiwar Amurka da Birtaniya.

Dangane da ci gaban yankin kuwa, Baqa’i ya bayyana cewa: Babban abin da ya fi daukar hankali a halin yanzu shi ne laifukan kisan kiyashi da ake ci gaba da wanzuwa a Falasdinu. A cikin ‘yan kwanakin da suka gabata, an shaida matakin da yahudawan sahayoniyya suka dauka na kakaba wa Gaza cikakken shingen da fice, inda a kullum ake kashe akalla mutane 80 da ba su ji ba ba su gani ba.

Ya kara da cewa, “kasashen duniya sun bayyana kin amincewarsu da manufar tilastawa Falasdinawa gudun hijira, amma duk da goyon bayan Amurka da kuma ci gaba da aiwatar da munanan manufofin Isra’ila na rashin hukunta ta, hukumar Isra’ila ta dage kan ci gaba da aikata laifukan da take aikatawa, wanda ya zama ci gaba da manufofin kisan kiyashi. A ranar Asabar din da ta gabata, yahudawan sahayoniyya sun kai hari kan yankunan kasar Yemen, kuma Iran ta jaddada yin Allah wadai da kakkausar murya, kuma harin kan ababen more rayuwa laifi ne na yaki.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Da Armenia sun kudiri aniyar kara bunkasa alakokinsu a dukkanin fagage August 19, 2025 Hamas da sauran bangarorin Falastinawa sun amince da shawarar tsagaita wuta August 19, 2025 DR Congo da mayakan M23 sun kasa cimma matsaya a  yarjejeniyar Doha August 19, 2025 Burkina Faso: Ba mu da bukatar Kodineta ta  MDD a kasarmu August 19, 2025 Araqchi: Iran Ba Za Ta Amince Da Sauyi A Kan Iyakokin Yankin Siyasa Ba August 18, 2025 Mataimakin Kwamandan Dakarun IRGC Ya Jadadda Cewa; Suna Sanya Ido Kan ‘Yan Sahayoniyya Da Magoya Bayansu August 18, 2025 Mai Ba Da Shawara Ga Kwamandan Sojojin Iran Ya Ce; Akwai Yiwuwar Sake Yaki, Don Haka Suna Cikin Shiri August 18, 2025 Shugaban Amurka Ya Ce: Yaki Tsakanin Iran Da Isra’ila Bai Kare Ba August 18, 2025 Trump Yace Zelensky Zai Kawo Karshen Yaki Da Rasha Tare Da Barin Batun NATO Da Crimea August 18, 2025 MSF Ta Ce Yawan Mutanen Da Suke Mutuwa A Gaza Sun Ninka Har Sau Uku Bayan Fara Aikin GHF August 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya

Shugaban Amurka Donald Trump ya umarci Ma’aikatar Yakin da ta ci gaba da gwajin makaman nukiliya nan take, shawara da tauni ta tsorata masu fafutukar yaki da irin wannan manufa.

A cikin wani sako da ya wallafa a dandalinsa na Truth Social yau Alhamis, Trump ya bayyana cewa ya bayar da umarnin “saboda shirye-shiryen tantancewa da wasu kasashe suke yi.” Kuma a cewarsa wannan tsari zai fara nan take,”

Shugaban Amurka ya bayyana Rasha da China a matsayin kasashe na biyu da na uku na duniya masu karfin makamman nukiliya, bi da bi, yana mai tabbatar da cewa idan Washington ba ta ci gaba da gwajin makaman nukiliya ba, wadannan kasashe za su cimma ta nan da ” shekaru biyar.”     

Ana sa ran tsarin gwajin zai samar da bayanai kan ayyukan sabbin makaman yaki da kuma amincin tarin makaman da suka tsufa.

Matakin na Trump shi ne wani kira na kai tsaye da Amurka ta yi na ci gaba da gwajin nukiliya tun bayan gwajin da Washington ta yi na karshe a shekarar 1992.

Masu suka sun yi gargadin cewa sake fara gwajin nukiliya na kai tsaye zai iya kawo karshen shekaru da dama na kokarin hana yaduwa da kuma haifar da tarin gwaje-gwajen ramuwar gayya a duk faɗin duniya, wanda hakan zai wargaza Yarjejeniyar Hana Gwajin Makaman nukiliya (CTBT).

A bara, wani rahoto ya nuna cewa Amurka na shirin kashe ɗaruruwan biliyoyin daloli don sabunta makaman nukiliyarta.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan October 30, 2025 Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu October 30, 2025 Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher October 30, 2025 An Kafa Dokar Ta Baci A Darul-Salam Saboda Tarzoman Zaben Shugaban Kasa A Tanzania October 30, 2025 Rasha Da Amurka Sun Sake Dawo Da Gwaje-gwajen Makaman Nukiliya October 30, 2025 Kasar Czech Ta Hana Wa Wani Sojan HKI Shiga Kasar Bisa Gargadin  Faransa October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
  • Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Duk Wani Kutse Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya
  • Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan
  • Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu