Gaza : Adadin Wadanda sukayi shahada a hare-haren Isra’ila cikin sa’o’I 24 ya karu
Published: 6th, September 2025 GMT
A cikin sa’o’i 24 da suka gabata, akalla Falasdinawa 68 ne suka yi shahada a Zirin Gaza, wanda ya kawo adadin wadanda suka rasu a yakin kisan kare dangi na Isra’ila tun watan Oktoban 2023 zuwa sama da 64,368.
Akalla Falasdinawa tara ne sukayi shahada a wani kazamin harin da aka kai ta sama a birnin Gaza da Khan Yunus, ciki har da takwas lokacin da aka kai hari kan wani gini a unguwar Sheikh Radwan.
Kamfanin dillancin labaran iqna, ya nakalto cewa, a ranar Asabar, wani yaro ya yi shahada a wani harin da Isra’ila ta kai kan wata mota a sansanin al-Mawassi da ke Khan Yunis.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, bayan harin bam da Isra’ila ta kai kan cibiyar rarraba kayan agaji a kudancin Wadi Gaza da ke tsakiyar yankin zirin Gaza, an kashe wasu Falasdinawa biyu tare da jikkata wasu akalla 17.
Dama kafin hakan, an kashe wasu Falasdinawa shida da ke jiran agajin jin kai sakamakon harbin da Isra’ila ta yi musu a kusa da wata cibiyar rarraba kayayyaki a kudu maso yammacin birnin Khan Younis, kamar yadda majiyar ta ruwaito.
A wani labarin kuma, Majiyoyin Falasdinawa sun rawaito cewa, da gangan sojojin Isra’ila suka kai hari kan Hasumiyar Al-Soussi, wani gini da ke dauke da dimbin al’ummar Gaza da suka rasa matsugunansu a ranar Asabar. Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da majalisar zartaswar firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ta amince da “Operation Gideon’s Chariots II”, wanda ke da nufin kwace iko da birnin Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyoyin gwagwarmaya sun fusata da barazanar Isra’ila na bude “kofofin jahannama” a Gaza September 6, 2025 Iran ta aike da kayayyakin jin kai tan 100 zuwa Afghanistan September 6, 2025 Ammar Hakeem ya gana da larijani a nan birnin Tehran . September 6, 2025 HKI Ta Kashe Falasdinawa 50 A Harin Da Takai A Yankin Gaza September 6, 2025 An yi Kira Ga El-rufai Da Ya yi Hattara Da Kalamansa September 6, 2025 An Gudanar Da Zanga-zangar Adawa Da Shirin Amurka Na Kwace makaman Hizbullah. September 6, 2025 Manyan Jami’an Kungiyar Hamas sun Gana Da Minister Harkokin Wajen Iran September 6, 2025 Afirka za ta iya samun tagomashi wajen habaka tattalin arzikin dijital – IFC September 6, 2025 Araqchi: Kasashen Turai Suna Nuna Son Kai A Kan Batun Hana Kera Makamin Nukiliya September 6, 2025 Kasar Iran Ta Bayyana Lokacin Sabon Zagaye Na Tattaunawa Tsakaninta Da Hukumar IAEA September 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Israila Ta Kai Hari Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A
Rahotanni sun bayyana cewa gwamnatin isra’ila na fuskantar suka game da matakin da ta dauka na kai hari kan kungiyar unicef ta majalisar dinkin duniya a gaza, matakin da falasdinawa da masu sa ido ke gani a matsayin wata dabara ta murukushe kungiyoyin agaji da kuma fitar da kungiyoyin majalisar dinkin duniya daga yankin gaza
Rahoton da wani jami’in majalisar dinkin duniya ya fitar a jiya jumaa ya nuna cewa sojojin isra’ila sun kama wani ma’aikacin UNICEF mai suna Raed Afif mai shekaru 45 da haihuwa a kerem shalom alokacin da yake gudanar da ayyukansa.
Yazu wa yanzu isra’ila bata bayyana dalilan da suka sanya ta kama shi ba kuma take ci gaba da tsare shi.
Kwana daya kafin tayi kamun isra’ila ta bukaci kungiyar ta Unicef da ta kwashe dukkan kayayyakin agajinta daga yankin , kawai sai ta rufe dukkan kofofin shiga da magunguna zuwa asibitocin dake arewacin yankin Gaza. Kungiyoyin bada agaji na duniya sun yi gargadin cewa wannan matakin an dauke shi ne domin yanke duk wasu ayyukan jinkai da ake yi da kuma korar dukkan kungiyoyin agaji da hakan zai kara sanyawa yanayi ya kara tazzar a yankin Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci Daga Yanzu November 1, 2025 Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci