Aminiya:
2025-09-18@08:34:52 GMT

Masu garkuwa da Shugaban APC a Ondo sun riƙe masu kai kuɗin fansa

Published: 15th, May 2025 GMT

’Yan bindigar da suka yi garkuwa da Shugaban Jami’iyyar APC a Ƙaramar Hukumar Ose a Jihar Ondo, Nelson Adepoyigi, sun riƙe mutanen da suka kai musu kuɗin fansarsa, sa’annan suka ƙara ƙudin fansar da suka nema da ninki shiga.

A ranar Litinin da dare ne ’yan bindiga suka yi awon gaba da Honorabul Nelson Adepoyigi a ƙofar gidansa inda suka nemi kuɗin fansa naira miliyan 100 kafin daga bisani a daidaita a kan miliyan biyar.

Majiyoyin sun a lokacin da yake ƙoƙarin shiga gida ne maharan suka far masa suka fito da shi daga cikin motarsu, sa’annan suka make shi da gungumen ice sa’annan suka tafi da shi.

Wani makusanci ga waɗanda suka kai kuɗin ya bayyana cewa, “Bayan daidaitawa da ’yan bindigar a kan kuɗin fansa, da masu biyan kuɗin suka kai sai ’yan bindigar suka kama su suka ɗaure a cikin dajin.”

A soke sakamakon jarabawar JAMB na 2025 gaba ɗaya —Ɗalibai ’Yan bindiga sun kashe jarirai, sun bai wa karnuka namansu a Zamfara 

Da yake tabbatar da faruwar abin, Shugaban Ƙaramar Hukumar Ose, Kolapo Ojo, ya ce yanzu ’yan bindigar sun ƙara yawan kuɗin fansar zuwa Naira miliyan 30 kafin sakin ɗan siyasan da sauran mutanen biyu.

Sai dai ya buƙaci jama’a su kwantar da hankalinsu, jami’an tsaro na yin duk mai yiwuwa domin kuɓutar da duk mutanen.

Kakakin ’yan sanda a jihar, Olusola Olayinka, ya shaida wa Aminiya cewa rundunar ta haɗa guiwa da jami’an tsaron sa kai da maharba domin zaƙulo ’yan bindigar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa yan bindigar

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.

An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.

Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.

An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.

Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.

Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun sako ma’auratan da suka sace a Katsina bayan biyan N50m
  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A  HKI
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin