Masu garkuwa da Shugaban APC a Ondo sun riƙe masu kai kuɗin fansa
Published: 15th, May 2025 GMT
’Yan bindigar da suka yi garkuwa da Shugaban Jami’iyyar APC a Ƙaramar Hukumar Ose a Jihar Ondo, Nelson Adepoyigi, sun riƙe mutanen da suka kai musu kuɗin fansarsa, sa’annan suka ƙara ƙudin fansar da suka nema da ninki shiga.
A ranar Litinin da dare ne ’yan bindiga suka yi awon gaba da Honorabul Nelson Adepoyigi a ƙofar gidansa inda suka nemi kuɗin fansa naira miliyan 100 kafin daga bisani a daidaita a kan miliyan biyar.
Majiyoyin sun a lokacin da yake ƙoƙarin shiga gida ne maharan suka far masa suka fito da shi daga cikin motarsu, sa’annan suka make shi da gungumen ice sa’annan suka tafi da shi.
Wani makusanci ga waɗanda suka kai kuɗin ya bayyana cewa, “Bayan daidaitawa da ’yan bindigar a kan kuɗin fansa, da masu biyan kuɗin suka kai sai ’yan bindigar suka kama su suka ɗaure a cikin dajin.”
A soke sakamakon jarabawar JAMB na 2025 gaba ɗaya —Ɗalibai ’Yan bindiga sun kashe jarirai, sun bai wa karnuka namansu a ZamfaraDa yake tabbatar da faruwar abin, Shugaban Ƙaramar Hukumar Ose, Kolapo Ojo, ya ce yanzu ’yan bindigar sun ƙara yawan kuɗin fansar zuwa Naira miliyan 30 kafin sakin ɗan siyasan da sauran mutanen biyu.
Sai dai ya buƙaci jama’a su kwantar da hankalinsu, jami’an tsaro na yin duk mai yiwuwa domin kuɓutar da duk mutanen.
Kakakin ’yan sanda a jihar, Olusola Olayinka, ya shaida wa Aminiya cewa rundunar ta haɗa guiwa da jami’an tsaron sa kai da maharba domin zaƙulo ’yan bindigar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa yan bindigar
এছাড়াও পড়ুন:
Mangal ya bada tallafin N80m don yi wa marasa lafiya tiyata a Katsina
Fitaccen ɗan kasuwar nan, Alhaji Dahiru Bara’u Mangal, ya bayar da tallafin Naira miliyan 80 don taimaka wa mutane masu fama da cutar mafitsara da matsalar gwaiwa domin yi musu tiyata kyauta.
An gudanar da tantance marasa lafiyar a Asibitin Ƙashi na Amadi Rimi kafin a fara aikin tiyatar a ranar Asabar da ta gabata.
Kebbi: PDP za ta yi haɗaka don ƙalubalantar APC a zaɓen 2027 Mutanen Sakkwato na neman ɗaukin gwamnati game da Bello TurjiAlhaji Kabir Husaini, wanda ke jagorantar aikin, ya bayyana cewa wannan shi ne karo na uku da Mangal ke bayar da irin wannan taimako ga marasa lafiya masu ƙaramin ƙarfi.
Ya ce a baya, Mangal ya taimaka wajen yi wa masu lalurar gwaiwa tiyata.
Tun bayan fara shirin a shekarun baya, sama da mutum 3,000 ne suka ci gajiyar aikin tiyatar da aka gudanar a wurare daban-daban.
A wannan karon, Mangal ya bayar da Naira miliyan 20 daga cikin tallafin domin yi wa mutum 100 tiyata a kan cutar mafitsara da kuma lalurar gwaiwa.
Ɗaya daga cikin waɗanda suka ci gajiyar shirin, Adamu Aliyu, ya ce da babu wannan tallafi, da har yanzu yana fama da cutar saboda ba shi da isasshen kuɗi don biyan kuɗin tiyatar.
Alhaji Mangal ya fara bayar da irin wannan taimako tun shekarar 2016, kuma tallafin yana zuwa har wasu maƙwabtan jihohi da ma Jamhuriyar Nijar.
Wata mata da ta nemi a sakaya sunanta ta ce wannan aiki ya zama darasi ga masu hali da ba sa son taimakon jama’a.
“Tun sama da shekara 20 Alhaji Mangal ke ciyar da marasa ƙarfi da abinci, kuma har yanzu bai fasa ba,” in ji ta.