Aminiya:
2025-05-15@17:18:54 GMT

Masu garkuwa da Shugaban APC a Ondo sun riƙe masu kai kuɗin fansa

Published: 15th, May 2025 GMT

’Yan bindigar da suka yi garkuwa da Shugaban Jami’iyyar APC a Ƙaramar Hukumar Ose a Jihar Ondo, Nelson Adepoyigi, sun riƙe mutanen da suka kai musu kuɗin fansarsa, sa’annan suka ƙara ƙudin fansar da suka nema da ninki shiga.

A ranar Litinin da dare ne ’yan bindiga suka yi awon gaba da Honorabul Nelson Adepoyigi a ƙofar gidansa inda suka nemi kuɗin fansa naira miliyan 100 kafin daga bisani a daidaita a kan miliyan biyar.

Majiyoyin sun a lokacin da yake ƙoƙarin shiga gida ne maharan suka far masa suka fito da shi daga cikin motarsu, sa’annan suka make shi da gungumen ice sa’annan suka tafi da shi.

Wani makusanci ga waɗanda suka kai kuɗin ya bayyana cewa, “Bayan daidaitawa da ’yan bindigar a kan kuɗin fansa, da masu biyan kuɗin suka kai sai ’yan bindigar suka kama su suka ɗaure a cikin dajin.”

A soke sakamakon jarabawar JAMB na 2025 gaba ɗaya —Ɗalibai ’Yan bindiga sun kashe jarirai, sun bai wa karnuka namansu a Zamfara 

Da yake tabbatar da faruwar abin, Shugaban Ƙaramar Hukumar Ose, Kolapo Ojo, ya ce yanzu ’yan bindigar sun ƙara yawan kuɗin fansar zuwa Naira miliyan 30 kafin sakin ɗan siyasan da sauran mutanen biyu.

Sai dai ya buƙaci jama’a su kwantar da hankalinsu, jami’an tsaro na yin duk mai yiwuwa domin kuɓutar da duk mutanen.

Kakakin ’yan sanda a jihar, Olusola Olayinka, ya shaida wa Aminiya cewa rundunar ta haɗa guiwa da jami’an tsaron sa kai da maharba domin zaƙulo ’yan bindigar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa yan bindigar

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Dangin sun yi kira ga hukumomin tsaro da su gaggauta ɗaukar matakin ceto waɗanda aka yi garkuwa da su, da kuma ƙara tura jami’an tsaro zuwa yankin.

Harin ya zo ne a lokacin da ake samun ƙaruwar ayyukan ‘yan ta’adda a wasu sassan ƙasar, musamman a yankin Arewa-Maso-Gabas.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Tinubu ya ƙaddamar da rundunar tsaron daji a faɗin Najeriya
  • An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
  • Falasdinawa Sun Harba Wa HKI Makamai Masu Linzami
  • Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi
  • Rahoto : Sama da mutum miliyan 80 aka raba da muhallansu a fadin duniya
  • Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m
  • Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe
  • ‘Yan Tawayen Sudan Sun Kai Hari Kan Gidan Yarin Al-Obeid Tare Da Kashe Fararen Hula Masu Yawa