Aminiya:
2025-05-06@14:52:35 GMT

’Yan PDP 6 a Majalisar Tarayya sun koma APC

Published: 6th, May 2025 GMT

Mambobin Jam’iyyar PDP shida a Majlisar Wakilai daga Jihar Delta sun sauya sheka zuwa Jam’iyya APC.

Kazalika wasu biyu daga Jihar Enugu sun sauya sheka daga Jam’iyyar adawa ta LP zuwa PDP.

Shugaban Majalisar Wakiliai, Abbas Tajuddeen, ne ya sanar da hakan bayan dawowar majalisar daga hutu a ranar Talata.

Shugaban Majalisar ya bayyana cewa ’yan majalisar sun yanke shawarar sauya sheka ne sakamakon rikicin cikin gida da ya dabaibaye jam’iyyun nasu a matakin jiha da kuma kasa.

Wadanda sauka sauya sheka zuwa APC su ne: Victor Nwokolo,  Julius Pondi, Thomas Ereyitomi, Nicholas Mutu, Okodiko Jonathan, da kuma Nnamdi Ezechi. Wadanda suka bar LP zuwa PPD su ne Mark Obetta da kuma Dennis Nnamdi.

Idan ba ma manta ba a kwanakin baya ne Gwamnan Delta, Sheriff Francis Orohwedor Oborevwori, da tsohon gwamnan jihar kumwa tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa Ifeanyi Okowa, da wasu kusoshin PDP suka sauya sheka zuwa APC.

 Ana yawan samun sauya sheka a Majalisar Wakilai daga jam’iyyun adawa zuwa APC mai mulki, a wannan majalisa ta 10.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai sauya sheka daga PDP sauya sheka

এছাড়াও পড়ুন:

Trump Na Shan Suka Kan Wallafa Hotonsa Na AI Sanye Da Kayan Fafaroma

Shugaban Amurka, Donald Trump na shan suka daga wasu jagororin mabiya ɗarikar Katolika, saboda wallafa hotonsa da ya samo daga manhajar ƙirƙirarriyar basira ta AI, sanye da kayan fafaroma.

Mista Trump ya wallafa hoton ne a shafukan sada zumunta na fadar White House.

Matakin na zuwa ne yayin da mabiyar ɗarikar Katolika, ke shirin zaɓen sabon fafaroma, bayan alhinin da suke ciki na rasuwar jagoran ɗarikar, Fafaroma Francis, wanda ya mutu ranar 21 ga watan Afrilu.

Taron mabiya ɗarikar Katorlika na birnin New York ya zargi Shugaba Trump da zolayar Addininsu.

Wallafa hoton na zuwa ne kwanaki bayan da shugaban ya zolayi wani mai bayar da rahotonni da cewa ”ina son zama fafaroma”

Ba Trump ne shugaban Amurka na farko da aka taɓa zarga da zolayar mabiya ɗariƙar Katolika ba.

A shekarar da ta gabata ma an zargi tsohon shugaban Amurka, Joe Biden lokacin da ya sanya hannu kan alamar kuros a lokacin wani gangamin masu goyon bayan zubar da cikin a Tampa da ke jihar Florida

A ranar Laraba mai zuwa ne fadar Vatican za ta fara shirye-shiryen zaɓen sabon fafaroma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Sha Alwashin Mayar Da Martani Cikin Gaggawa Kan Duk Wani Hari Kan Kasarta
  • Aikin Hajjin 2025 Ya Fara A Hukumance Yayin Da Tawagar NAHCON Ta Musamman Ta Tashi Zuwa Makkah
  • Majalisar Kano Ta Amince Da Dokar Wutar Lantarki Da Za Ta Raba Wa Jihohi 3 Wuta
  • Umaru ’Yar’adua da shugabannin Najeriya da suka rasu a kan mulki
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Ce Masifar Yunwa Ta Kara Yin Kamari A Yankin Zirin Gaza Na Falasdinu
  • OPEC+ Zata Kara Yawan Man Fetur Da Take Haka Da Ganga 411,000 A Cikin Watan Yuli Mai Zuwa
  • Iran ta yi Allah-wadai da harin da Isra’ila ta kai kan jirgin ruwan da ke jigilar abinci zuwa Gaza
  • Kafar United Daya Ta Kai Wasan Karshe A Gasar Europa League
  • Trump Na Shan Suka Kan Wallafa Hotonsa Na AI Sanye Da Kayan Fafaroma