An yi wa zakarun wasan motsa jiki ruwan a Akwa Ibom
Published: 14th, September 2025 GMT
An yi wa ’yan wasan guje-guje da tsalle-tsalle na Jihar Akwa Ibom ruwan kuɗi, bayan sun yi fice a gasar wasannin motsa jiki ta ƙasa da aka yi wa laƙaba da IBOM 2025, wacce aka kammala a ƙarshen makon nan.
Gwamna Umo Eno, ya bai wa gwarazan ’yan wasan da suka lashe kambin Zinare kyautar Naira 500,000, waɗanda suka samu Azurfa Naira 250,000, yayin da waɗanda suka lashe Tagulla suka tashi da Naira 150,000.
A jawabinsa na rufe gasar da aka gudanar a filin wasa na Uyo, babban birnin jihar, Gwamna Eno ya bayyana cewa dukkan ’yan wasan sun fito ne daga ƙananan hukumomi 31 na jihar.
Baya ga kyautar da ’yan wasa suka samu, gwamnan ya bai wa kowace ƙaramar hukuma da ta halarci gasar Naira miliyan 15.
Haka kuma, waɗanda suka yi wa sauran zarra sun samu Naira miliyan 10, yayin da sauran ƙananan hukumomin kuma kowacce ta samu Naira miliyan 5 a matsayin tallafi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Akwai Ibom
এছাড়াও পড়ুন:
An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
Majiyar ta kara da cewa, bayan yunkurinsu bai yi nasara ba a Tsanyawa, maharan sun sake wani sabon shiri, inda suka kai hari a kauyen Yar Tsamiya da ke gundumar Faruruwa, karamar hukumar Shanono, da misalin karfe 1:30 na dare, inda suka kashe mutane uku suka, tare da sace wasu uku.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA