Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya
Published: 15th, September 2025 GMT
Tun daga ranar 18 ga wata, za a kaddamar da fim mai taken 731 a sassan duniya da dama, fim din da ya bayyana yadda rundunar sojojin kasar Japan da suka kutsa kasar Sin suka gudanar da nazari a kan hada makamai da cututtuka tare da gudanar da gwaje-gwaje a jikin al’ummar kasar Sin, a birnin Harbin na lardin Heilongjiang da ke arewa maso gabashin kasar Sin, kafin al’ummar kasar Sin su cimma nasarar yaki da su.
A ranar 19 ga watan Agusta, hukumar kula da tsaron kasar Rasha ta fitar da wata takardar sirri da yanzu gwamnati ta mayar da ita ba ta sirri ba, wadda ta nuna cewa, domin neman yin amfani da makaman da aka hada da cututtuka a yakin kutsen da suka kaddamar a kasar Sin, reshen rundunar sojojin Japan da suka yi kutse a kasar Sin mai lambar 731, sun yi ta gudanar da gwaje-gwaje a jikin al’umma, har ma sun kai harin boma-bomai da aka samar da cututtuka a kan daruruwan Sinawa, don neman tantance ingancin cututtuka ta hanyar kirga mutanen da suka harbu da cututtuka.(Lubabatu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma October 30, 2025
Daga Birnin Sin Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC October 30, 2025
Daga Birnin Sin Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya October 30, 2025