Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama
Published: 14th, September 2025 GMT
Hakazalika, sojojin na Brigade 12 tare da hadin gwiwar dakarun hadin gwiwa da ’yan banga a wannan rana, sun ceto fasinjoji 17 da wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a karamar hukumar Lokoja ta jihar Kogi.
Hakazalika, dakarun Sashe ta 1 ‘Operation Whirl Stroke (OPWS)’ sun ceto wani a karamar hukumar Katsina-Ala ta jihar Benuwe.
Haka kuma a jihar Filato a wannan rana, dakarun Sashe ta 8 ta ‘Operation Enduring Peace (OPEP)’ sun kama wasu da ake zargin barayin ne a karamar hukumar Mangu tare da kwato makamai da alburusai da kudade.
A wani samame kuma sojojin na Shiyya ta 1 OPWS sun kwato bindiga kirar AK-47 daya da harsashi 29 a wani sintiri a karamar hukumar Ado ta jihar Benuwe.
A wani samame makamancin haka a ranar 11 ga watan Satumba, sojojin na Brigade 12 a jihar Kogi sun yi nasarar kashe wani dan ta’adda a karamar hukumar Kabba Bunu, tare da kwato wata mujalla ta AK-47 cike da alburusai da wayoyin hannu 31.
Yayin da a jihar Borno, wani mayakin ISWAP/JAS ya mika kansa ga rundunar hadin gwiwa ta Ngamdu, inda ya bayyana wasu muhimman bayanai kan ayyukan ‘yan ta’adda.
A wannan rana, sojojin runduna ta 8 sun ceto mutane bakwai da aka yi garkuwa da su tare da kwato wata mota a yayin da suka yi arangama da ‘yan ta’adda a kan hanyar Marnona-Gundumi-Isa.
Bugu da kari, sojojin na Brigade 12 sun ceto wasu mutane hudu da aka yi garkuwa da su a hanyar Egbe – Eruku a karamar hukumar Yagba ta Yamma a jihar Kogi.
Bugu da kari kuma, a jihar Filato, sojojin Sashe na 2 sun dakile wani mummunan harin masu ra’ayin riƙau suka kai a karamar hukumar Quan-Pan tare da tallafin jiragen yaki mara matuki, yayin da dakarun Sashen 3 na OPEP suka ceto wani da aka yi garkuwa da shi a karamar hukumar Bassa.
Hakazalika a ranar 11 ga watan Satumba, sojoji sun kama masu fasa kwauri a karamar hukumar Mubi ta Kudu a jihar Adamawa wadanda suka yi watsi da wata motar dakon kaya dauke da jarkoki 20 na man fetur.
Hakazalika, a yankin Kudu-maso-Kudu, dakarun ‘Operation Delta Safe’ sun gano tare da tarwatsa wani wurin tace haramtacciyar mai mai dauke da kusan lita 3,800 na danyen mai da aka sace a jihar Bayelsa, yayin da wata tawaga ta cafke lita 1,600 na disal (AGO) da aka tace ba bisa ka’ida ba a jihar Ribas.
A ranar 12 ga watan Satumba, sojojin Sashen 3 na OPEP sun ceto wani da aka yi garkuwa da shi a karamar hukumar Bassa ta jihar Filato, wanda aka yi garkuwa da shi a Jos, jihar Filato a ranar 11 ga watan Satumba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: da aka yi garkuwa da a karamar hukumar ga watan Satumba jihar Filato
এছাড়াও পড়ুন:
An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
Mai shari’a Dahiru ya amince da buƙatar, ya kuma ɗage shari’ar zuwa ranar 12 ga watan Disamba, 2025, domin ci gaba da sauraron shari’ar.
Ƙuli-ƙuli dai nau’in abin ci ne mai taushi da ake yi da gyaɗa, ana soyawa har sai ya zama ƙura-ƙura ta yadda za a ci cikin nishaɗi.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA