Aminiya:
2025-11-02@06:20:10 GMT

’Yan rakiyar amarya 19 sun mutu a hatsarin mota a Zamfara

Published: 14th, September 2025 GMT

Aƙalla mutane 19 ne suka mutu a yayin da suka ɗauko wata amarya zuwa ɗakin mijinta bayan motarsu ta faɗa a ƙarƙashin gadar Gwalli da ke yankin Fass a Ƙaramar Hukumar Gummi a Jihar Zamfara.

Lamarin ya faru ne da yammacin Asabar da misalin ƙarfe 4:45 na yamma, lokacin da motar, da ke ɗauke da maza da mata da yara ta faɗo daga saman karyayyiyar gadar, ta nutse a cikin ruwa.

Wani ɗan uwan amaryar, Babangida Halifa Ibrahim Fass, wanda ya rasa ’yan uwa a cikin hatsarin, ya ce hatsarin ya faru ne a lokacin da ake kai ’yar uwarsa amarya gidan mijinta  da ke Jega a Jihar Kebbi.

Ya ce, “Motar ta faɗo ne daga kan gada ta nutse a ruwa. Da aka ciro su, mutum 19 daga cikinsu sun mutu, maza, mata da yara.”

Najeriya ta daɗe tana fama da shugabanni marasa nagarta — Sanusi II HOTUNA: Mahaifiyar Dangote ta halarci gasar karatun Alƙur’ani ta Shetty a Kano

A ranar Lahadin nan ake sa ran yin jana’izar su, kuma an bayyana cewa mahaifin amaryar shi ne tsohon ɗan majalisar jihar, Marigayi Sheikh Dauda Fass.

Gadar Gwalli, wadda ke haɗa ƙauyukan Gwalli, Yar Gusau da Fass, ta daɗe a lalace ba tare da an gyara ta ba.

An fara gyara ta a lokacin mulkin tsohon gwamna Abdulaziz Yari, amma ruwan sama ya sake lalata ta tun kusan shekaru bakwai da suka gabata.

A bana ma, al’ummar yankin sun yi ƙoƙarin cike sasanta da suka zaizaye da yashi domin rage haɗarin, amma duk da haka gadar ta sake karyewa.

Wasu mazauna ƙauyen sun ce lalacewar gadar ta jawo musu wahala musamman a lokacin damina, inda ake tsoron ambaliyar ruwa ta tafi da mutane.

Babangida ya ɗora alhakin matsalar a kan sakacin gwamnati, yana cewa: “Tun lokacin muna cikin wahala. Wasu lokuta har ta cikin rafi muke ƙetarawa domin kai gawa maƙabartar. Mun taɓa cike buhunan shinkafa da na siminti da yashi don gina gadarmu.”

Mutanen yankin sun roƙi gwamnatin jihar da ta tarayya da su gaggauta gina sabuwar gada kafin irin haka ya sake faruwa.

Sun ce wannan lamari ya sake nuna yadda jama’ar Zamfara ke rayuwa cikin tsoro da wahala duk da iƙirarin gwamnati na gyara muhimman hanyoyi a ƙauyuka.

Da aka tuntubi mai magana da yawun gwamna, Mustapha Jafaru Ƙaura, ya fara cewa bai san da kauyen ko kuma wannan lamarin ba, amma daga bisani ya yi alƙawarin yin bincike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Amarya ɗaukar amarya Gadar Gwalli Hatsari Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

A zantawar Sule Lamido da BBC, ya bayyana cewa; an yi masa kora da hali a hedikwatar jam’iyyar ta PDP.

Ya kara da cewa, ya je hedikwatar jam’iyyar PDP ne; domin karbar fom na takarar shugabancin PDP, sai ya samu ofishin da ya kamata ya karba a kulle, da ya tambaya sai aka ce da shi, a hannun gwamnan Adamawa kadai zai samu fom din.

Lamido ya ci gaba da cewa, ba ya fata a kai ga matakin da za a hana shi shiga takarar, “domin ina tunanin rigimar cikin gida ce, sannan kuma za mu iya samun maslaha a cikin gidan. Amma idan hakan bai yiwu ba, daga nan kuma na san me zan yi,” in ji shi.

Haka zalika, Sule Lamido ya ce; a shirye yake ya tsaya takarar shugabancin jam’iyyar a zaben da za a yi lokacin babban taron jam’iyyar a watan Nuwamban wannan shekara a birnin Ibadan na Jihar Oyo.

Bugu da kari, Lamidon ya sha alwashin tafiya kotu idan har aka ki sayar masa da fom din tsayawa takarar.

Kazalika, rahotanni sun tabbatar da cewa; tuni tsohon ministan ayyuka na musamman, Kabiru Tanimu Turaki ya yanki nasa fom din, a daidai lokacin da aka ki sayar wa da tsohon gwamnan na Jigawa fom din takarar shugabancin jam’iyyar ta hamayya, wato PDP.

Har wa yau, Jam’iyyar PDP ta sanar da dage tantance dan takara daga ranar Talata zuwa wani lokaci nan gaba, duk da cewa; jam’iyyar ba ta fadi dalilin yin hakan ba.

Haka nan, sanar da Kabiru Tanimu Turaki a matsayin dantakarar maslaha daga Arewacin Nijeriya ya bar baya da kura, inda wasu daga cikin shugabannin jam’iyyar PDP na shiyyar Arewa maso yammacin kasar, shiyyar da Turaki ya fito suka yi watsi da matakin da gwamnoni suka dauka.

Kazalika, shugaban jam’iyyar PDP na Jihar Sakkwato, Muhammad Bello Aliyu na cikin shugabannin da suka yi fatali da matakin da gwamnonin suka dauka, saboda a cewarsa, ba a ba su damar zama su tattauna ba, gabannin tsayar da Turakin. Kana kuma, an sake samun wasu jiga-jigan jam’iyyar daga Jihar Kebbi da suka yi fatali da wannan maslahar.

Dangane da wanan sabuwar rigima ko rikici, malami a kwalejin ilimi ta share fagen shiga jami’a da ke Kano kuma mai sharhi kan al’amuran yau da kullum, Dakta Kabiru Sa’id Sufi ya ce; ana neman fama karaya ne a yunkurin gyara targade.

“Mun dauka cewa, tunda aka zo batun zaben shugabanci, matsalolin da jam’iyyar ke ciki sun kusa zuwa karse, musammman ganin har an yi kokarin rarraba mukamai zuwa shiyya-shiyya, amma kuma sai hakan ya bar baya da kura.

“Yanzu haka, an fara samun korafi daga bangarori da dama, ciki har da daga wadanda ake ganin ba su da wata matsala.”

Haka nan, ya kara da ce; hana Sule Lamido sayen fom din takarar shugabancin jam’iyyar, wani babban al’amari ne, domin kuwa a cewar tasa; hakan ya kara haifar da rashin gamsuwa a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar.

Ya ce, “Akwai da ma wasu da suke ganin an lasa musu zuma a baki a Arewacin kasar na tsayawa takara, sai daga baya suka gane cewa, ba da gaske ake ba. Idan aka duba, za a ga akwai rashin gamsuwa daga bangarori da yawa. Ko bangaren Shekarau ma, sun nuna rashin gamsuwa da yadda ake tafiyar da al’amuran.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta October 31, 2025 Manyan Labarai Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi? October 31, 2025 Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
  • Ƙwallo ta kashe ɗan wasan Cricket
  • Sudan : Kasashen duniya na Allah wadai da cin zarafi a lokacin kama El-Fasher
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba
  • Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin