Aminiya:
2025-09-17@20:29:57 GMT

’Yan rakiyar amarya 19 sun mutu a hatsarin mota a Zamfara

Published: 14th, September 2025 GMT

Aƙalla mutane 19 ne suka mutu a yayin da suka ɗauko wata amarya zuwa ɗakin mijinta bayan motarsu ta faɗa a ƙarƙashin gadar Gwalli da ke yankin Fass a Ƙaramar Hukumar Gummi a Jihar Zamfara.

Lamarin ya faru ne da yammacin Asabar da misalin ƙarfe 4:45 na yamma, lokacin da motar, da ke ɗauke da maza da mata da yara ta faɗo daga saman karyayyiyar gadar, ta nutse a cikin ruwa.

Wani ɗan uwan amaryar, Babangida Halifa Ibrahim Fass, wanda ya rasa ’yan uwa a cikin hatsarin, ya ce hatsarin ya faru ne a lokacin da ake kai ’yar uwarsa amarya gidan mijinta  da ke Jega a Jihar Kebbi.

Ya ce, “Motar ta faɗo ne daga kan gada ta nutse a ruwa. Da aka ciro su, mutum 19 daga cikinsu sun mutu, maza, mata da yara.”

Najeriya ta daɗe tana fama da shugabanni marasa nagarta — Sanusi II HOTUNA: Mahaifiyar Dangote ta halarci gasar karatun Alƙur’ani ta Shetty a Kano

A ranar Lahadin nan ake sa ran yin jana’izar su, kuma an bayyana cewa mahaifin amaryar shi ne tsohon ɗan majalisar jihar, Marigayi Sheikh Dauda Fass.

Gadar Gwalli, wadda ke haɗa ƙauyukan Gwalli, Yar Gusau da Fass, ta daɗe a lalace ba tare da an gyara ta ba.

An fara gyara ta a lokacin mulkin tsohon gwamna Abdulaziz Yari, amma ruwan sama ya sake lalata ta tun kusan shekaru bakwai da suka gabata.

A bana ma, al’ummar yankin sun yi ƙoƙarin cike sasanta da suka zaizaye da yashi domin rage haɗarin, amma duk da haka gadar ta sake karyewa.

Wasu mazauna ƙauyen sun ce lalacewar gadar ta jawo musu wahala musamman a lokacin damina, inda ake tsoron ambaliyar ruwa ta tafi da mutane.

Babangida ya ɗora alhakin matsalar a kan sakacin gwamnati, yana cewa: “Tun lokacin muna cikin wahala. Wasu lokuta har ta cikin rafi muke ƙetarawa domin kai gawa maƙabartar. Mun taɓa cike buhunan shinkafa da na siminti da yashi don gina gadarmu.”

Mutanen yankin sun roƙi gwamnatin jihar da ta tarayya da su gaggauta gina sabuwar gada kafin irin haka ya sake faruwa.

Sun ce wannan lamari ya sake nuna yadda jama’ar Zamfara ke rayuwa cikin tsoro da wahala duk da iƙirarin gwamnati na gyara muhimman hanyoyi a ƙauyuka.

Da aka tuntubi mai magana da yawun gwamna, Mustapha Jafaru Ƙaura, ya fara cewa bai san da kauyen ko kuma wannan lamarin ba, amma daga bisani ya yi alƙawarin yin bincike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Amarya ɗaukar amarya Gadar Gwalli Hatsari Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

 

Haka kuma, wannan na faruwa ne makonni biyu bayan yin garkuwa da Pastor Friday Adehi na Christian Evangelical Fellowship of Nigeria (CEFN) tare da wani abokin cocinsa bayan kammala wa’azi. Wannan ya kara nuna yadda matsalar garkuwa ke ta’azzara a yankin Kogi East.

 

A gefe guda, kungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA), reshen Idah, ta bukaci gwamnati a matakai daban-daban da ta dauki matakan gaggawa don kawo karshen satar mutane a jihar. Shugaban kungiyar, Barr. James Michael, ya ce yawaitar garkuwa a kan titunan yankin ya jefa rayukan jama’a cikin hatsari, don haka gwamnati ya kamata ta dauki tsauraran matakai domin kare lafiyar al’umma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
  • Ambaliya ta lalata gidaje da gonaki a Kaduna