Aminiya:
2025-11-02@16:53:08 GMT

Ban taɓa nadamar shiga Kannywood ba — Kabiru Nakwango

Published: 14th, September 2025 GMT

Kabiru Abubakar Aliyu, wanda aka fi sani da Nakwango, ɗaya ne daga cikin jiga-jigan da aka kafa masana’antar fina-finan Hausa ta Kannywood da su.

A cikin wannan tattaunawar, ya bayyana cewa bai taɓa yin da-na-sanin shigarsa sana’ar ba, sannan ya bayyana dalilin da yanzu ba a cika ganin sa sosai a fina-finai ba, da ma yadda ya ce fim ɗin Hausa ya taɓa zama silar sasanta wasu ma’aurata da aurensu yake tangal-tangal.

Tun yaushe ka shiga harkokin fim ɗin Hausa?

Ai harkar fim ɗin Hausa daga baya ta fito, a da wasan kwaikwayo ake yi. Na fara wasan kwaikwayo na rediyo wajen 1970, lokacin ina ƙarami. A lokacin rikoda ta fito. To a sannan na fito a matsayin mace a wasan, saboda a sannan muryata ba ta fashe kamar yanzu ba. Daga nan sai sha’awar abin ta daɗa shiga raina, tun da dama ina kallon iyayenmu a harkar a lokacin irin su Ƙasimu Yero da su Usman Baba Pategi (Samanja), da yake su sun daɗe suna yi kuma abin yana ba ni sha’awa.

Kamar fim ɗin Hausa irin na Kannywood fa, yaushe ka fara shi?

An fara fim ɗin Hausa irin na yanzu ne a wajen 1994/1995. To a lokacin mu tuni ma mun yi nisa a harkokin wasan kwaiwayo, duk da ba mu ce za mu shigo fim ɗin ba. Amma aƙalla tun kafin a fara fim irin na yanzu, mun yi fina-finai za su kai aƙalla bakwai.

A lokacin ba wai zuwa muka yi makaranta aka koya mana yadda za a yi ba, kyamara kawai za a kafa mana, a lokacin irin JVC kyamara ɗin nan, har yanzu ina da ita, wacce take zuwa batiri daban, kanta ma daban. To a haka tun wannan lokacin mun yi fina-finai da dama.

Ko za mu iya sanin wasu daga cikin su?

A lokacin akwai fina-finai irin su ‘Jambaɗe’, ‘Jan artabu’, sai ‘Ta inda kuka yake zuwa…’, da sauransu.

Lokacin da kuke wasan kwaikwayo na rediyo, wace rawa ka fi takawa a cikinsu?

Na fito a mace, wacce ake kira Matar Malam. Ka san ita matar malam duk abin da Malam ya zo da shi, shi za a yi. Ko dai ta bi shi ko kuma ta kangare. Daga baya kuma sai na fito a ɗalibi, daga nan kuma ba a daɗe ana yi ba sai muka shiga ‘stage drama’.

Za ka iya tuna fim ɗin da ka fara fitowa a ciki?

Na fara fitowa a wani fim na Hamisu Iyantama da ake kira ‘Ƙilu ta ja bau’. Ba zan iya tuna shekarar ba. Amma kafin na fito a wannan, na shirya fim nawa na kaina mai suna ‘So ne ko ƙauna’. Shi ne fim na farko na Hausa da ya fara fita a sinima ta farko a Kano, wato Wapa Sinima. Daga baya muka kai shi sinimar Eldorado. Su ne fina-finan farko na Hausa da aka fara a ƙarƙashin kamfaninmu da ake kira da Dabo Films.

Shin ko ka kiyaye shekarar da aka yi shi?

Eh, shi a 1995 aka yi shi.

Akwai waɗanda suke yi wa ’yan fim na yanzu kallon masu ƙarancin tarbiyya. Ya kake ji a matsayinka na ɗaya daga cikinsu?

Bahaushe yana cewa mutunci riga ne, kowa ka gani shi yake sa wa kansa. Babu a inda babu mutanen kirki ko fitsararru. Duk harkar duniya akwai baragurbi. Shugabanni, malamai, ’yan acaɓa, kowacce harka. Shi wannan kallon da mutane suke yi wa ’yan fim, magana ta gaskiya ba kowa suke yi wa ba.

Wanda ya yarda a ce da shi mutumin kawai, za a faɗa masa, haka ma wanda ya yarda a faɗa masa mutumin kirki, shi ma haka za a faɗa masa.

A kwanakin nan, ana ganin bidiyoyinka kana karantarwa. Kwanan nan ka fara ko dama tun tuni kana yi?

Ni malamin makaranta ne, ban kuma ma san lokacin da na fara ba. Aikin mahaifina ne noma da karantarwa, a haka ya haife ni na gan shi yana yi, kuma na koya na iya. Duk abin da ka gan ni ina yi ba su ba, kawai kewayawa na yi na dawo kansu. Amma kuma ni ba malami ba ne babba kamar yadda wasu suke kallo na.

Shin har yanzu kana harkar fim ɗin ko ka daina?

Fim, dalilai da yawa sun sa na dakatar da yawan yin shi, amma ban ce na daina ba. Idan aka zo da fim irin nawa, wanda zai yi kira ga hanyar Allah, kuma ya yi kama da maganar Allah, to zan yi. Amma idan na ga fim ba na Hausawa ba ne, kawai fim ne da aka rubuta shi da yaren Hausa ba zan yi ba.

To ke nan kana ganin irin waɗancan fina-finan da ke isar da saƙon sun yi ƙaranci ke nan?

Idan ka kalli fina-finan da ake yi yanzu, mafiya yawa da yaren Hausa ake yin su, amma ba fim ɗin Hausa ba ne, ni kuma wakilin Hausawa ne.

To mene ne bambancinsu?

Yawwa. Za a ɗauko al’ada. Alal misali, idan Bature zai yi maka fim, zai ɗauko rayuwarsa da al’adarsa da ƙarfin ƙasarsa, sannan ya yi farfaganda domin jan hankalin mutanen duniya ƙarfinsa da muhibbarsa, don ka ji tsoron sa. Kai kuma Bahaushe idan ka ta shi za ka nuna waye kai, yaya ka taso, da me ka girma? Ko rubutun wasiƙa za ka yi, me zai hana ka rubuta da ajami? Hakan zai zama wani abin bajinta, saboda Turawan sun zo sun same ka kana da karatu da rubutu da tsarin shari’a da na mulki.

To amma yanzu sai a zo a yi fim da salon Turawa. A yi fim a ɗauki bindiga ana hare-harbe. Wannan ba al’adar Bahaushe ba ce, kuma a Nijeriya ma ba mu san wannan ba. Fim ake yi kawai da yaren Hausa, amma ba na Hausawa ba. Ko ɗakin shari’a za ka nuna a fim, ya kamata ya zama irin na Bahaushe da siffar shigar alƙali ya kamata ya nuna al’adar Bahaushe tun da ko a kotu ba a haɗa maza da mata wajen zama. Amma ba haka muke yi ba yanzu.

Sannan hatta kalaman da za a yi amfani da su a fim, ya kamata su zama a ingantacciyar Hausa, amma yanzu sai ka ga ana Ingausa ko kuma ka ji mutum ya zunduma ashar a fim. Wannan ba daidai ba ne saboda Bahaushe bai san wannan ba.

Amma ban raina musu ba, suna matuƙar ƙoƙari. Kuma tun farko an sami tangarɗa da aka bar abin a hannun matasa ba a shige ta ba. Attajirai, shugabanni, malamai duk ba su shige ta ba. Kaɗan daga cikin malamai ne ma ba sa aibata ’yan fim. Idan matsala ta zo dubawa ake yi ana da maganinta, ko kuma idan an kawar da ita wacce ta fi ta za ta shigo Kana tunanin nan gaba akwai wanda zai iya hana sana’ar fim? Ko gwamnatin jiha ko ta tarayya?

Sana’a ce da matasa suka ƙirƙire ta daga babu, har ta kai inda take a yau. Ina daga cikin waɗanda suka fara fim ɗin Hausa na yanzu, (ba wasan kwaikwayo ba).

Duk da waɗannan tarin matsalolin da ka yi bayani, waɗanne hanyoyin kake ganin za a bi domin inganta fim ɗin Hausa?

To Allah Ya sawwaƙe. Hanyoyin suna da yawa, amma dole sai an nemi dai masu sana’ar domin a nuna musu ga abin da ake da buƙata, ba wai a wofantar da su ba. Gwamnati ta yarda za ta shiga ciki ta shige musu gaba, ta nuna musu yadda za su girmama Nijeriya su nuna ɗayantakar ƙasar, saɓanin yadda ake nunawa yanzu cewa akwai Hababba da Haƙarami. Akwai ƙabilu ƙasƙantattu akwai shafaffu da mai. To sai an gyara an nuna musu. Duk matsalolin siyasa da na diflomasiyya, duk abin da kake so ɗan fim zai iya gyara shi.

An taɓa wasu ma’aurata, miji da matansa biyu, har yana shawarar sakin su, amma ta sanadin kallon fim suka shirya kansu, mai rubuta fim ɗin ma bai san su ba, kawai ya kalli abin da ke faruwa ya yi fim. Har nan gidana mijin ya zo tare da matan nasa tun daga Sakkwato. Ban san su ba, kuma ba fim ɗina ba ne, amma saboda rawar da na taka har fim ɗin ya yi tasiri a rayuwarsu suka zo don nuna godiya.

’Yan fim suna zuba kuɗinsu, ka ga kuwa dole su yi tunanin yadda kuɗaɗensu za su dawo. Amma wanne irin tallafi gwamnati ta saka a ciki, ba wai kullum wani ya shiga gidan rediyo ya ce duk ’yan fim ’yan iska ba ne.

Ko kana da wani da-na-sani a harkar fim gaba ɗayanta tun lokacin da ka fara ta?

Alhamdulillahi ban taɓa yin da-na-sani ba. Ni dai ban san abin da na yi na da-na-sani ba, sai dai idan wani ya hango. Amma ni dangane da iyayena, ko surukaina ko ’ya’yana ko abokan karatuna ko malamaina, ba ni da matsala kuma ban taɓa abin da zan yi da-na-sani a ciki ba. Hasali ma nakan haɗu da mutanen da ke girmama ni a sanadiyyar fim ɗin.

Akwai abin da ba za ka iya mantawa da shi ba a harkar na daɗi ko akasin haka?

Gaskiya suna da yawa. Na daɗin daga ciki akwai ranar da na yi tafiya daga Kano zan je Gombe, sai mota ta lalace min a hanya, ni kuma kuɗin hannuna a lokacin ba za ma su ishe ni wunin ranar ba, ballantana na gyara motar. To fuskata da ake gani a fim ta sa aka tarbe ni aka kira bakanike ya gyara min motar aka sallame shi, sannan ni ma aka ba ni kuɗin da suka ishe ni har na dawo gida na yi uzururrukana da su na aƙalla kwana 10, duk arziƙin fim.

Na kuma taɓa sauka a wani gari cikin dare, ina neman wanda zan je wajensa, saboda lokacin babu wayar salula, ina ta tambayar mutumin ba a gano shi ba, ga shi wajen ƙarfe ɗaya na dare. Na shiga wata unguwa sai kawai wani mutum ya buɗe ƙofa ya ce Malam Kabiru ne? Ai kuwa sai ya ce da matarsa na shigo na kwana a gidansa sai da safe na nemi wajen da zan je. Komai akwai a ɗakin.

Har yanzu kuma muna zumunci da mutumin. Kwana biyar na yi niyyar yi a garin a lokacin, amma daga ƙarshe sai da na yi kwana 13, saboda karamcin da aka nuna min. Har littafi sai da mutumin ya sa muna darasi da shi.

Kazalika, a lokuta da dama matata ta sha zuwa asibiti amma a ce ba sai ta bi layi ba, cikin ƙanƙanin lokaci za a yi mata komai, wannan duk arziƙin fim ne. Ina kuma da makaranta, amma tun daga wurare masu nisa wasu suke kawo ’ya’yansu, saboda kawai sun ji an ce tawa ce kuma suna gani na a fim. Sannan mutane na girmama ni duk inda na shiga, duk da cewa wani girman ma ban cancance shi ba.

Sannan a ɓangaren rashin daɗi kuwa, an taɓa kama ni saboda na tsaya wa wani mutum a kotu, amma ya gudu. Zan kwana a caji ofis amma wani ya zo ya fitar da ni cikin daren, sai da ya je har wajen alƙali ya nemi izini. Masinjan kotun ne yake ba da labari wani ya ji ya yi ta faɗi tashi sai da ya je har wajen alƙali ya ba da umarni aka sake ni, ban kwana a ofis ɗin ba. To ka ga wannan abu ne mara daɗi da ba zan manta da shi ba.

Ko akwai wanda yake sha’awar harkar fim a zuri’arka?

Eh, akwai ɗana da ya nuna sha’awa amma bai yi nisa ba ya bari. Yanzu haka kuma akwai wanda ya ce yana sha’awar tace fim, sai na haɗa shi da masu yi, yanzu haka kuma har ya goge a tace fim din.

To kana fatan nan gaba ya zama magajinka ke nan a masana’antar?

A’a, ba zai iya ba.

Me ya sa?

Shi fim da taka rawa a cikinsa a jikin mutum yake. Sai dai ya yi shuhura a wani abin daban, amma ba irin nawa ba. Kowa da yadda Allah Ya yi shi. Akwai waɗanda suka fi ni ilimin addini a Kannywood, amma sai a ce a kira ni. Akwai kuma waɗanda sun fi ni ƙwarewa a harkar, amma saboda wasu dalilai, sai a ce a kira ni.

Kowa da yadda Allah Ya yi shi. Misali irin su Ibrahim Mandawari, gogagge ne a fim, da shi aka fara Kannywood, amma abin da zai yi ba zan iya yi ba, shi ma abin da zan yi ba zai iya ba, saboda kowa da irin baiwarsa.

Ko kana da saƙo ga ’yan uwanka ’yan fim?

Babban saƙona gare su shi ne su ji tsoron Allah kan duk abin da suke yi, sannan su yi ƙoƙari wajen tallar addininsu da al’adunsu sannan su riƙa yafiya a junansu.

Ga sauran jama’a kuma, ya kamata su riƙa kyautata zato, su daina gaggawar yanke wa wasu hukunci. Kowa na iya yin kuskure, kuma za a iya gyara masa ta hanyar da ta dace, amma ba ta kafafen yaɗa labarai ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kabiru Nakwango kannywood kwaikwayo wasan kwaikwayo a Kannywood

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci Daga Yanzu

A wani rahoto da miami herald ya wallafa a jiya jumaa ya nuna cewa kasar Amurka na shirin kaiwa kasar Venuzuwela hare hare,  yayin da Donald trump shugaban kasar Amurka yake musantawa cewa babu wani shiri na daukar matakin soji a kasar ta latin Amurka.

Yace gwamnatin trump ta yanke shawarar kai hari kan wasu wuraren soji a kasar, a kowanne lokaci.

Yace duk da yakin da washington ke yi kan miyagun kwayoyoi gwamnatinsa ba ta la’akari da kai hare-haren sojin kan venuzuwela yana nuna a akwai karo da juna a kalamansa na makon da ya gabata

Da manema labarai suka tambayeshi ko hare-haren da Amurka takai a yan kwanakin nan kan jiragen ruwa a yankin karebiya da aka ce suna fataucin miyagun kwayoyi na iya sanyawa akai hare hare kan venuzuwela trumpa ya amsa da cewa A’a.

 A yan makwannin nan da suka gabata Trump ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta kai hari kan wuraren da suke da alaka da miyagun kwayoyi acikin venuzuwela yana mai cewa kasar za ta zama  it ace ta gaba da za su daukai mataki a kanta.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci Daga Yanzu
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai
  • Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano Spalleti
  • Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai