Leadership News Hausa:
2025-09-17@20:28:15 GMT

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

Published: 14th, September 2025 GMT

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

Kamar yadda Oche, wadda ‘ya’yan ‘yar’uwarta suke zuwa makarantar Reno ta Oluwami da Firmare , da take Abuja inda shekarun baya suke biyan wajen Naira 600,000 ko wane zangon karatu, saboda wasu haraje- harajen da aka haɗa da su ciki.

“Maganar gaskiya kowace shekara idan za’a shiga sabon zangon karatu, makarantu su kan ƙara kuɗin makaranta, su ƙara wasu sabbin abubuwa, kamar su kuɗin ICT, wasanni tsaro.

Sai dai ƙarin da akwai matuƙar matsala.”

A makarantar( Prime School ) da ke, Karu,inda aka ƙiyasta ana biyan kusan Naira 300, 000, kowane zangon karatu,wani Malamin da baya son a ambaci sunansa ya ce, akwai ƙarin kuɗin makaranta waɗanda suna da alaƙa ne da lamarin daya shafi kayn zuwa makaranta, bunƙasar makaranta, da kuma sauran abubuwa.

“Idan aka dukkan ƙarurrukan da aka yi abin zai zama da akwai ɗaure kai. Kuɗin haya ya ƙaru a wannan unguwa idan kuma mutum ya yi bincike kuma za a gane irin mutanen da suke zama a wurin, waɗanda abinda suke samu ba kasafai yake biya masu buƙata ba. Don haka idan har ka sa ɗanka wannan makaranta,duk da yake dai z aka, iya biya,amma idan wani babban abu ya taso kamar kiuɗin haya abin sai dai ayi shiru kamar yadda ya ce,”.

Wani mahaifi, Joseph Hange wanda ‘yarsa take zuwa makarantar Bright Child Academy, Lugbe, cewa ya yi sabuwar shekarar karatun ta zo da abubuwa masu sosai zuciya.

“Abin bai tsaya kan maganar ƙare-ƙaren kuɗaɗen bane kawai na kuɗin makaranta, abinci, Littattafai, suturar zuwa makaranta, ziyarar buɗe ido, duk a haɗa su wuri ɗaya. Kamar su da suke harkar kasuwanci, lamarin tattalin arzikin ba shi da daɗi.Cewa ya yi sun tattauna a gida ko daga ƙarshe irin wannan tafiyar za ta ɗore”.

Yayin da Iyaye lamarin ya hana su kwanciyar hankali,su ma Malaman makarantar kamar duk jirgi ɗaya ya ɗauko su.Domin kuwa yawancin makarantu yawan ƙarin kuɗin makaranta bai kai wag a ƙarin albashi ga su Malaman makarantar.

Wani Malami mai suna Moses Sachi a Abuja shi ma abin ya dame shi, saboda kuwa cewa yayi “Muna dai jin Iyaye suna kokawa, amma mu ma a matsayinmu na Malamai, matsalar da take damun Iyayen yaran muma ita ce ke damun mu .Lamarin kuɗin haya, abinci, da zirga- zirga abin yana ci mana tuwo a ƙwarya.

Wasu daga cikinmu akwai ayyukan da muke yi domin a samu tsira da mutunci kamar, zuwa koyar da darussa a gida, ƙananan sana’oi, kawai saboda dai mu samu kulawa da Iyali . Wasu makarantu sun ɗan yi ƙarin albashi wanda bai maganin matsin tattalin arzikin da kowa yake fuskanta ba, bama kamar talaka kamar yadda ya jaddada” .

Binciken da LEADERSHIP ta yi rahoton ya nuna matslar ba kawai ta ƙare bane kan ƙarin kuɗin makaranta ba.Kuɗaɗen haya sun ƙaru a sassa daban daban kamar su Abuja, Legas, da kuma wasu manyan wurare kamar Karu, Lugbe, da Gwarimpa da sauarn sassan Babban Birnin Tarayya Abuja, masu gidaje sun ƙara kuɗin haya da kashi 30 kamar yadda binciken ya nuna

Shi yasa Iyayen da suke biyan kuɗin makaranta dubban Nairori yanzu dole ne su san irin hanyar da za su bi, domin su nemi ƙarin kuɗin da za su cika domin biyan haya.

Wani mahaifi a Nyanya, mai suna Isaac Terseer, ya yi lamarin kallon abinda zai yi wuyar jurewa:

Inda ya ce “Wannan tamkar mutum ya riƙa bin inuwa ne da ƙoƙarin kamata.An ƙara kuɗin makaranta, kuɗin haya sun ƙaru.

Wannan halin ƙuncin rayuwa tana sa mutane ko iyalai su cikin halin ni’yasu kan yadda za su yanke shawarar daga cikin abubuwan da suka kamata su yi su ɗauki ɗaya da suke ma kallpon ya fi muhimmanci. Wasu na canza wa ‘ya’yansu makaranta zuwa wadda kuɗin da za su iya biya.Wasu suna tunanin yanke shawarar a riƙa koya masu a gida, ko kuma maida su makarantun gwamnati duk kuwa da yake akwai matsalar kayan aiki da, da rashin nagartar koyarwar.

An samu bayanan da suke nuna Iyaye na biyan tsakanin Naira milyan 3 zuwa 5 kowane zangon karatu.

Ta ɓangaren tsaka- tsaki ana biyan Naiar 800,000 zuwa milyan 2.5 kowane zangon karatu.

Waɗanda ake ma kallon masu sassauci ne a Abuja ana biyan Naira 120,000 zuwa 200, 000 a kowane zangon karatu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Makaranta kowane zangon karatu kuɗin makaranta zuwa makaranta ƙarin kuɗin kamar yadda kuɗin haya

এছাড়াও পড়ুন:

Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku

Al’ummar garin Dukku a Ƙaramar Hukumar Dukku ta Jihar Gombe sun koka kan mummunan halin hanyar da ta haɗa su da babban birnin jihar, tare da kira ga gwamnati da ta gaggauta gyaran ta.

A cewar direbobi, tafiyar Dukku zuwa Gombe wadda a da take ɗaukar mintuna 50 kacal, yanzu ta koma fiye da awa biyu saboda lalacewar hanyar, abin da ke jawo gajiya da takaici ga fasinjoji da masu tuƙi.

An fara gina hanyar Gombe-Dukku-Darazo ne tun a shekarun 1980, aka gyara ta a farkon shekarun 2000. Sai dai daga baya aka yi sakaci da ita duk da kasancewarta hanyar da matafiya daga jihohin Adamawa, Taraba, Jigawa, Kano, Bauchi da wasu ke bi.

“Gyaran motoci na cinye mana kuɗi”

Usman Abubakar, direba mai shekaru 45 da gogewar tuki na sama da shekaru 19, ya ce lalacewar hanyar na sa direbobi kashe kuɗi masu yawa wajen gyaran motoci.

Bida Poly ta sa sojoji kula da jarrabawar ɗalibai ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu

“Gaskiya hanyar ta lalace matuƙa. A da tafiyar Dukku zuwa Gombe kan ɗauki mintuna 45, yanzu kuwa ko awa biyu ba ta isa ba. Rami ne a ko’ina, musamman daga Tongoyel zuwa Bojude da Bozonshulwa. Sau da dama idan ka fito da safe sai ka tarar da motoci sun tsaya cak a hanya. Shock absorber, gilashi da sauran sassan mota suna yawan lalacewa saboda ramukan hanyar,” in ji shi.

Ya ce a da ‘shock absorber’ na iya kaiwa shekara biyu kafin ya lalace, amma yanzu ko watanni uku bai yi ba sai ya karye. Hakazalika tsohon gilashi da ake siya ₦90,000 yanzu cikin sati biyu kawai sai ya fashe.

Usman ya kuma ce ya sha yin haɗura a hanyar cikin watanni biyu kacal, inda tayar motarsa ta fashe, ‘shock absorber’ ya karye, sannan kingpin ya lalace — duka sakamakon shiga ramuka.

Wani direba, Abubakar Hassan, ya ce lalacewar hanyar ta kai shi ga tunanin barin aikin tuƙi gaba ɗaya saboda asarar kuɗi.

“Idan ruwan sama ya sauka, tafiya sai ta koma tamkar azaba. Sau da dama motoci kan kwana a hanya saboda lalacewa,” in ji shi.

Fasinjoji sun bayyana ƙalubale

Kabiru Zubairu, ɗaya daga cikin fasinjojin da ke yawan amfani da hanyar, ya ce, “A da tafiyar kilomita 72 kan ɗauki mintuna 45 zuwa 60, yanzu ta koma awa biyu. Idan na taso Dukku da karfe 7:00 na safe, yanzu sai mu isa bayan 9:00. Wannan na jawo mana jinkiri sosai.”

Wani fasinja, Abubakar Aliyu, ya ce mutane da dama sun daina zuwa Gombe saboda halin hanyar. “Idan ka yi tafiya sai jikinka ya yi ciwo. Wasu matasa kan zuba yashi a cikin ramuka, amma ruwan sama yana wanke shi,” in ji shi.

Muhimmancin hanyar — Masana

Mai sharhi a harkokin jama’a, Sulaiman Sa’idu Liman, ya ce kusan kilomita 64 daga cikin 72 na hanyar Dukku zuwa Gombe sun lalace, kuma motoci yanzu ba sa iya wuce gudu na kilomita 20 a awa ɗaya.

“Hanyar na da muhimmanci ga tattalin arziki da walwalar al’umma. Ana jigilar kayan gona, kayayyakin lafiya da marasa lafiya ta wannan hanya zuwa Asibitin Koyarwa na Tarayya (FTH) Gombe,” in ji shi.

Likita Aliyu Bashir kuwa ya ce lalacewar hanyar na haifar da matsaloli ga lafiyar jama’a, musamman ƙura da ke haddasa cutar asma, da kuma haɗarin haihuwa kafin lokaci ga mata masu juna biyu saboda girgizar mota.

Kungiyoyi da direbobi sun yi kira

Shugaban Ƙungiyar Tuntuɓa ta Dukku (DCF), Muhammad Bala Hashidu, ya yi kira da a gaggauta gyaran hanyar gaba ɗaya.

Shi ma shugaban Kungiyar Direbobi ta NURTW a Dukku, Abdulhamid Hassan, ya ce kusan kowace rana ana samun aƙalla motoci 10 da ke lalacewa a kan hanyar, abin da ya rage musu kuɗin shiga.

Gwamnati ta magantu

Mai magana da yawun gwamnan Gombe, Ismaila Uba Misilli, ya tabbatar da cewa gwamnati na aiki tare da takwarorinta na Arewa maso Gabas domin samun tallafin Gwamnatin Tarayya wajen gyaran hanyar.

“Kwanan nan gwamnonin yankin sun gana da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu inda suka roƙi a gyara muhimman hanyoyi ciki har da wannan. Domin hanya ta tarayya ce, gwamnatocin jihohi ba su da ikon gyaran ta kai tsaye. Amma gwamnoni sun dage wajen ganin an gyara ta,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja